← Book details Kaifi Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 21

Sashe 4

Kaifi Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Afeef wallahi lafiya ta ƙalau kuma ina cikin hayyacina sannan na san abinda nake fada, ni dai kawai dan Allah ka taimake ni ka yimin wannan alfarmar tun kafin na shiga wani hali dan ina son matata itama kuma tana sona.... Karka wani damu auren kisan wuta za kuyi da ita ba wai wani abu ba..... ". Hmmm what do you think will happen in the next chapter? Drop your guesses, comment what you think......... Next chapter loading...... ✍🏻

KAIFI ƊAYA... ✨

*When the world called her “useless”… he called her “mine.”*💘

_KAIFI ƊAYA_ is not just a love story. It’s the story of Mimi - a doctor whose name was dragged through scandal, whose body was broken by fate… 💔
And Afeef - the man who chose to stay when everyone told him to leave. 😥

They won the fight against the world.
But can they win the fight for each other, when silence is louder than lies, and love is tested by things neither of them chose? 🥺

*One blade. One choice. One love that refuses to break.*❤️
_Kaifi Daya_ - because true love doesn’t walk away when you can’t walk anymore..😥

It's available now 07044644433

Your heart will not be the same after the last page🥰✍🏻✍🏻

#Kaifi ɗaya #
#EmotionalRomance#
#MimiAndAfeef#

_*Ummi Shatu*_👌🏻
[7/18, 8:56 AM] Oum Jasrah: https://www.arewapen.com/book?id=6a50f2f571e75baab6622006

KAIFI ƊAYA....

_A story of scandal, sacrifice and a love that refused to break, a love that says am still here._

NA
UMMI A'ISHA

3

***Mamaki, fargaba da kuma zulumi duk shinfide kan fuskar Afeef yake kallon Aliyu zuciyarshi na lugude kamar zata faso kirjinsa ta fito, wai wannan wanne irin kwaɗo ne? Da wanne suna zai iya kiran wannan kwamacalar wacce Aliyu yazo da ita,

"ka fahimceni Afeef? Wani abun fa dole sai naka ne zai iya yi maka..... Nasan zaka yimin wannan alfarmar ko ban baka ko sisi ba..... Ka fadi duk abinda kake son inyi maka a duniyar nan, wallahi zanyi maka idan har zaka amshi wannan bukatar tawa...."

"wai dan Allah kai waye ya baka wannan shawarar Aliyu? Me yasa sai wannan ɗan jaririn? Afeef nawa yake da za ayi wannan abin dashi...."

Juyawa yayi ya kalli anty Mimi wacce ke magana cikin zafin rai, tunda aka fara maganar dama bata saka baki ba sai yanzu,

" Anty Mimi ina ganin girman ki amma kar ki sake kirana da jariri..... " shima ya fada cikin zafin rai, babu kalmar da tafi bakanta masa rai ta hassala shi irin jaririn da ta kira shi da shi a iya saninshi ai shi yanzu yafi karfin a kirashi da jariri tunda jariri na can bayan tsohuwar sa,kamar dama jira take ya tanka ta rufe shi da faɗa ta fara balbala masa masifa kamar zata doke shi,

"kai wanene idan ba jariri ba awurina, kana da wani girman ne wanda yafi wannan? Yaushe ma kazo duniyar da har ka girma? Tatsitsi da kai....."

Murmushi yayi mai cike da takaici da kuma baƙin ciki,

"yaya haidar ba zan iya wannan abun da kake son inyi maka ba..... Sai anjima" daga haka ya tashi ya fice ransa a ɓace zuciyarsa na faman tafarfasa wallahi ba dan yana ganin darajar anty Mimi ba idan wata ce ba ita ba bata isa ta faɗa masa haka ya ƙyaleta ba da sai ya dauki matakin da gaba daya baza su ji dadinsa ba, ransa a mutukar ɓace ya shiga motar sa ya fita daga cikin harabar asibitin ya nufi wurin Irfan.

Bayan fitar Afeef Aliyu kallon Mimi yayi cikin damuwa da fuskar lallashi yace,

"My love..... Fushi yanzu da zafin rai duk ba naki bane, dole sai kinyi hakuri kin dauke kai sannan zamu samu abinda muke so daga wurin yaron nan, idan muka ce zamu bishi ta zafin kai to bukatar mu ba zata taɓa biya ba...."

Dafe kanta tayi cike da damuwa idanuwan ta a lumshe tace,

" ni dai haka kawai banji hankalina ya kwanta da Afeef ba cikin wannan batun, me yasa ka dage lallai sai shi? Why? "

" Afeef cousin dinmu ne daga ni har ke dan haka na san zai yi wahala yaci amanarmu gaba daya, sannan na san yana ganin girman ki dan haka da wuya yace zai cimin amana ta hanyar raɓarki sabanin idan wani ne a waje na san zai yi wahala bai yi yunƙura aikata hakan ba ni kuma hakanne bana so, bana fatan wani namiji ya shigar min gona ta.... Wannan shine reason dina na son ayi sabgar nan da Afeef... Ki daure kiyi hakuri har mu shawo kansa ya amince, idan bukatar mu ta biya shikenan... "

" it's fine.... " shine kawai abinda tace ta kifa kanta kan teburin dake gabanta dan ta rasa me yake yi mata daɗi kuma, sallama Aliyu yayi mata ya fita kuma yana zuwa motar shi ya fara kiran Afeef bayan ya tura masa sako,

Afeef na cike da damuwa ya ƙarasa gidan Hajiya inda Irfan ke can yana jiransa, gashi yana dauke da damuwa amma kuma babu halin faɗa ko sanar da wani, duk yadda yake biye hajiya suyi ta haurawa amma yau bai kula ta ba kuma yana zuwa ta fara caccakeshi da masifa,

"sarkin zurfin ciki.... Na jima banga mugun mutum irinka ba lele, kowa yana bude baki yayi sallama amma kai sai dai kawai in ganka ka faɗo min cikin ɗaki sai kace kaine ka gina min dakin..... Wannan isar taka da ikon nan da kake yi a gidan nan ya isa haka, ko iyayen ku idan sun zo shigowa sai sun yi sallama da budaddiyar murya amma kai da yake isasshe ne sai ka gadama..... "

" wallahi nayi sallama kawai dai baki ji bane tunda yanzu ba wani ji kike yi ba sosai.... " ya fada cikin nuna alamun ƙosawa da maganar,

" to yanzu da naka kunnen nake ji da zaka ce bana ji..... Nace naka kunnen ka bani aro nake ji yanzu da kake ikirarin bana ji? "

" ohh Allah..... Ni dai yau na shiga uku, dan Allah hajiya Allah ya baki hakuri naji banyi sallama ba shikenan...." ya fada yana dafe kansa wanda yaji yana shirin fara yi masa ciwo, shigowar Irfan ta sa hajiya mayar da kallonta kansa shima ta fara balbale shi da fada,

" kai ba tun jiya nace akira min kai ba shine ka ki zuwa sai yanzu da wannan marar kunyar yazo sannan zaku haɗo kai kuzo...."

Zama Irfan yayi kusa da Afeef ya kyale hajiya bai tanka ba hakan ya sake tunzura ta tace,

"marassa kunya.... Ku tashi ku fice min daga cikin ɗaki ko inci muku mutunci yanzun nan...."

Afeef zamewa yayi ya kwanta kan kujera yana harararta batare da yayi magana ba dan ransa dama a ɓace yake kuma yana cikin damuwar wannan matsalar da yaya Aliyu ke kokarin lallai sai ya saka shi aciki shima ta shafe shi,

Yana kwance yana jinsu sai fafatawa suke yi ita da Irfan ahaka wayar shi ta fara kara ganin yaya Aliyu ne sai yaki dauka shikuma cigaba yayi da kiransa babu kakkautawa, ɗan kallonsa Irfan ya juya yayi sannan yace,

"your phone is ringing fa..... Afeef..... Are you sleeping?"

"wallahi bana jin dadi ne Irfan.... Kaina ma ciwo yake yi"

"sannu.. Allah ya sawwake"

Ita kuwa hajiya karkace kai tayi tana kallonsa zuwa can kuma tace,

"yi hakuri lele ai ban san baka da lafiya ba..... Na zata iya shegen naka ne ya tashi"

Lumshe idanuwansa kawai yayi bai ce komai ba, kwata kwata ya rasa me yake yi masa daɗi shi dai kawai yana jinsa gashi nan gashi nan dai shi ba mai lafiya ba shi ba marar lafiya ba, bayan hajiya ta fita Irfan ya dafa shi yace,

"Afeef wai me yake damunka ne? Naga kamar fa kana cikin damuwa, ko kai da mommy ne?"

Girgiza kai yayi dan baya jin zai iya sanar da wani wannan damuwar tashi,

"kaina ke ciwo Irfan..."

"bari na duba bedroom din anty Mimi na san is hardly a rasa paracetamol.."

"ok"

Ganin Irfan ya tashi itama hajiyan ta tashi yasa shi daukar wayar yaya Aliyu da har yanzu bai hakura ba wurin miss calls 10 yayi masa,

"Afeef.... Haba ƙanina... Nine fa yaya Aliyu yayanka, why are you like this? Yarda ce fa tasa nake son baka amanar Mimi..... Na san kai kadai ne zaka iya cika min alkawari"

"yaya Aliyu am very sorry...... Gaskiya bazan iya karbar wannan amanar ba, beside ma ni ban ko fara tunanin yin aure ba a yanzu"

"A'a Afeef..... Ka dai yi tunani dan yanzu daga ni har Mimi da kai muka dogara kaine kadai gatanmu a yanzu dan kaine zaka fitar damu daga cikin halin da muke ciki na damuwa da tashin hankali..... Dukanmu muna bukatar taimakonka dan Allah.... Please"

"Yaya haidar gaskiya bazan iya yi muku wannan taimakon ba..."

"kafi son muje mu samo bare wanda zai tona mana asiri Afeef? Kaifa dan uwanmu ne...."

"dan Allah yaya Aliyu kayi hakuri mu bar maganar nan dan wallahi kaina ba zai iya dauka ba tayi masa girma"

"ka dai zauna kayi tunani Afeef..."

Ganin Irfan na tahowa yasa Afeef katse wayar ya ajiyeta kan kirjinsa tare da lumshe idanuwansa, zama Irfan yayi yana mika masa paracetamol din sannan cikin son jin karin bayani yace,

"naji kamar kana waya, kai da waye?"

"babu kowa... Ba waya nake yiba"

Shuru Irfan yayi amma shi dai ya san kunnen sa ya jiyo masa kamar Afeef din yana yin waya sai dai amma tunda yace ba haka bane dole ya barshi a haka din.

Bayan azahar yabar family house kamar yadda suke kiran gidan ya nufi gidansu zuciyarsa cike da tunani iri iri kuma daban daban, part dinshi kawai ya shiga ya kwanta bai ko leka side din mommy ba sai ita mommy dince ta shiga wurinshi, kwance ta iskeshi harda su lulluba kamar wani mai yin bacci,

"Afeef baka da lafiya ne?"

"mommy am fine kawai ina hutawa ne...."
Chapter 4 · 0% Book details