Sashe 10
Kaifi Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"amma dai ai ka san hajiya ba tabbas nima wata rana tana birkice mun idan ƴar rikicin na kusa"
Da wannan hirar suka ƙarasa part ɗin hajiya wacce ke zaune tana faman lasar farfesun naman kai wanda ya dahu rigif, zama suka yi suka fara tsokanarta wani ta kula su wani ta rabu dasu, zuwa la'asar anty Mimi ta dawo gidan amma babu wanda ya san dawowarta bare har ya ganta dan bedroom dinta ta wuce ba tare da ta nemi kowa ba,
Shima Afeef yau bai nemi inda take ba yayi sallama da Hajiya ya tafi, iya hajiya da Irfan ne kadai suka san zai koma aiki gobe, da yake yawanci idan zai koma tafiyar asubanci yake yi shiyasa tun dare ya yi kokarin shirya jakar kayansa kamar yadda ya saba, bayan ya kammala haɗa komai ya fita zuwa part din mommy iya Manal ce kadai cikin falon tana kallo ya shiga ita kuma mommy din tana cikin kitchen, har cikin kitchen din ya bita cikin sanyin murya yace,
"mommy sannu da aiki......"
"yawwa"
"mommy na gama shiryawa gobe zan koma calabar..." ɗan sanyi mommy taji acikin ranta da taji cewa zai koma aiki gobe saboda bata son yaci gaba da zama auren nan da aka lankaya masa ya ɗore,
"Gara ka koma ai tunda zaman naka anan baida wani amfani..."
"insha Allah gobe zan tafi mommy...."
"Amma me yasa baka fada min da wuri ba, ai da anyi maka snacks kamar koda yaushe...."
"babu komai mommy, hajiya ta bani...."
"to shikenan"
Ganin yanda mommy din ta dan sauko har tana tarairayarsa yasa ya dan ji sanyi da dadi cikin ransa, 12 na dare ya kwanta bayan ya saita alarm dan yana son ya tashi kafin asubah tayi saboda gudun makara sai dai amma baccin yaƙi zuwar masa a maimakonshi ma tunani yaji yana ta bijiro masa cikin wannan lokaci wanda gaba ɗaya akan lamarinsu ne da ya shafi yaya Aliyu haidar, Anty Mimi da kuma shi, tun farko mema yasa ya yarda har yaji tausayinsu ya karɓi wannan tayin nasu? Juyi kawai yake ta faman yi har misalin karfe 1 da rabi na dare, da ya tabbatar baccin ba zai dauke shi a wannan lokaci ba sauka yayi daga kan gadon nasa ya shiga bathroom ya dauro alwala ya fito, sallar nafila yayi raka'a biyu sannan ya samu wuri ya zauna kan abin sallar tashi yana mai cigaba da yin addu'o'i har 3 saura kuma sai lokacin ya dan ji bacci a idanuwansa babu ɓata lokaci ya koma saman gadon shi ya kwanta, makara ya so yi saboda bai kwanta da wuri ba amma dai da kyar ya iya tashi ya shirya ya fita bayan yayi salla, sun yi sallama da kowa na gidan sannan ya tafi yana ji a cikin zuciyarsa wannan tafiyar tashi itace zata bawa zuciyar mommy damar hucewa cikin kankanin lokaci.
Yaya Aliyu tun ranar da aka ɗaurawa Afeef da anty Mimi aure ya fara jera lissafi wato ranar da ya dace Afeef ya saketa kamar yadda suka yi alƙawari, cikin bedroom dinta yake kwana hotunanta kafe a kowacce kusurwa ta bangon ɗakin, wani lokacin su kwana suna waya wata rana kuma su raba dare suna waya saboda irin dafin soyayyar da kowannensu ke ji cikin ransa, haka da rana da safe da yamma baya samun sukuni komai kankantarsa har sai ya kirata yaji muryar ta, sosai yanzu take jin abun yana bata tsoro dan kamar wanda Aliyun ya zautu abubuwan da yake yi a kanta sun fara wuce lissafin hankali,
Tun tana cikin bathroom tana wanka taji yana kiranta amma bata dauka ba saboda ta makara yau sosai kuma ba kowane ya makarar da ita ba face shi saboda shine ya hanata bacci suna ta faman hira har asubah, gashi yau akwai aiki shiyasa take ta sauri bata tsaya wani daukar wayar shi ba, cikin sauri ta fita ta bar gidan ta tafi asibiti kuma tana zuwa ta shiga theater, shi kuma ganin yana ta kiranta bata dauka ba yasa shi fita daga gida ya nufi asibiti dan ya san tana can tunda yau akwai aiki, daga shi sai kayan bacci ya shiga motar sa ya figeta zuwa asibiti, ta shiga theater dan haka ya zauna yana jiranta wanda ba ita ta fito ba sai 12,
"Aliyu yau baza ka fita aiki bane?" ta fada tana kallon sa bayan ta zauna kan kujerar ta,
"wallahi zan je aiki My love, in fact ma akwai wani important meeting da nake dashi but ba zan iya zuwa ba mutukar ban jiki ko kuma na ganki ba..." girgiza kai tayi cike da tausayinshi tace,
"Am fine... Dan Allah ka daina wasa da aikin ka, ina nan lafiya lau...."
"ta yaya zan iya tabbatar da hakan alhali ban sameki ba koda a waya ne?"
"Kaga ai na shiga theater ne and you know idan na fito dole zan kiraka back...."
Ajiyar zuciya ya sauke ya kalle ta cikin sanyin murya yace,
"insha Allah saura 1 week daidai Afeef ya sake ki kamar yadda muka shirya......"
"Babu problem, Allah ya kaimu...."
"yana nan ma kuwa? 2 days bana ganinsa, ko ciwon nashi ne ya tashi ko ya motsa? Bari na kirashi naji...." wayar shi ya dauka dake ajiye kan teburinta ya fara kiran layin Afeef..........✍️
KAIFI ƊAYA... ✨
*When the world called her “useless”… he called her “mine.”*💘
_KAIFI ƊAYA_ is not just a love story. It’s the story of Mimi - a doctor whose name was dragged through scandal, whose body was broken by fate… 💔
And Afeef - the man who chose to stay when everyone told him to leave. 😥
They won the fight against the world.
But can they win the fight for each other, when silence is louder than lies, and love is tested by things neither of them chose? 🥺
*One blade. One choice. One love that refuses to break.*❤️
_Kaifi Daya_ - because true love doesn’t walk away when you can’t walk anymore..😥
It's available now 07044644433
Your heart will not be the same after the last page🥰✍🏻✍🏻
#Kaifi ɗaya
#lovetriangle
#DrMimiAndAfeef
_*Ummi Shatu*_👌🏻
[7/18, 8:56 AM] Oum Jasrah: https://www.arewapen.com/book?id=6a50f2f571e75baab6622006
_A story of scandal, sacrifice and a love that refused to break, a love that says am still here._
KAIFI ƊAYA.....
NA
UMMI A'ISHA
8
***Zuba masa ido tayi kawai tana kallonsa cikin ranta tana jin wani irin bala'in tausayinshi saboda yana yin abu kamar wani wanda ya ɗan taɓu ko kuma ya zautu banda haka yanzu kalli fa a yanda ya fito ya taho office dinta dan kawai ya kirata a waya bai jita ba,ɗan tsakin da taji ya ja ne ya dawo da ita cikin hayyacinta,
"wannan yaron ko bacci yake yi bai tashi bane..... Na kira tana ta ringing bai yi picking ba"
"may be bai tashi daga bacci ba...."
"amma anya kuwa yana gari..... Nifa bana ganin shi ko a family house"
"shine dai nima ban sani ba dan na jima ban ganshi ba nima...."
"to babu matsala dai, zuwa anjima zan sake taɓa shi inji"
"ok"
"bari naje gida na shirya na fita office"
"ok to thank you"
Tashi yayi ya fita amma sai faman waiwayenta yake yi kamar yau ne ya fara ganin ta yayin da ita kuma ta janyo wani file ta bude ta fara rubutu aciki.
Bayan da Afeef ya koma bakin aikinsa gaba daya tattara maganar aurenshi da anty Mimi yayi ya ajiye a gefe dan a takaice ma shi ya manta da cewar akwai wani aurenta a kansa, baya waya da kowa sai Irfan kadai idan ya samu lokaci sai kuma mommy da daddy suma din kawai yana kiran su ne saboda ya kwantar musu da hankali domin duk ranar da basu ji shi ba hankalinsu tashi yake suyi ta tunanin ko ba ƙalau ba,kusan kullum sai yaga miss calls din yaya Aliyu amma bai taba kiran sa back ba abinda ya fara ƙonawa yaya Aliyun rai kenan shida anty Mimi dan a ganinsu wannan rainin wayo ne dan suna neman abu a wurin shi bashi ne zai bashi lasisi ko kuma damar wulakanta su ba yadda yaso,
Misalin ƙarfe 1 harda rabi na dare ya kira Irfan, yana kwance cikin dakinshi kuma dawowarshi kenan daga aiki, jin Irfan ya daga wayar ya sashi yin murmushi kafin a hankali yace,
"wai bacci kake yi?"
"wallahi idona biyu yanzun nan naje na dauko anty Mimi daga hospital na dawo da ita gida....." ai sai lokacin Afeef ya tuna da maganar auran shi da ita da kuma uban kiran wayar da yaya haidar ke ta faman yi masa babu dare ba rana,
"ohh matata ka dauko min daga aiki kenan.... Thank you for taking good care of her for me....."
Dariya Irfan yayi yace "you see your life?"
"yanzu dai menene labari? How is everyone? Ya anty Mimi hope she's fine?"
"baka da number dinta ne kake tambayata? Call her and ask....."
"yanzu ma sai da na gama waya da ita before na kiraka" ya fada cike da tsokana,
"kamar gaske...."
"am serious young man"
"yanzu dai wai zuwa yaushe zaka dawo?"
Ɗan dogon numfashi ya ja sannan a hankali yace "i don't know gaskiya.... I can't say, but idan na samu time zan zo"
Sun jima suna hira kafin suka yi sallama kowannensu ya ajiye waya, Irfan tunani yake yi cikin ransa anya kuwa anty Mimi da Afeef suna communicating? Dan bai ga alamar hakan ba dan baya mantawa tafiyar Afeef dinma shi take tambaya wai abokinsa yana nan kuwa taga bata ganin shi kwana biyu shi kuma yace ai ya koma calabar bai yi mata sallama bane? Daga haka yaga tayi shiru bata sake yin maganar ba,
A bangaren Afeef kuwa yana ajiye waya ya ɗan yi shuru na wasu yan mintuna kamar me yin tunani, iya gajeren wando ne a jikinsa tashi zaune yayi yana shawarar to ko ya kira yaya Aliyu yanzu? To kuma idan ya kirashi yanzu anya dare bai yi ba? Fasa kiran nasa yayi ya koma ya kwanta kan yar karamar katifarshi, kullum shi kadai yake kasancewa a ɗan karamin dakin nashi saboda tarbiyar da iyayenshi suka bashi duk wata rayuwar shashanci bata burge shi kuma baya cudanya da ita.
Da wannan hirar suka ƙarasa part ɗin hajiya wacce ke zaune tana faman lasar farfesun naman kai wanda ya dahu rigif, zama suka yi suka fara tsokanarta wani ta kula su wani ta rabu dasu, zuwa la'asar anty Mimi ta dawo gidan amma babu wanda ya san dawowarta bare har ya ganta dan bedroom dinta ta wuce ba tare da ta nemi kowa ba,
Shima Afeef yau bai nemi inda take ba yayi sallama da Hajiya ya tafi, iya hajiya da Irfan ne kadai suka san zai koma aiki gobe, da yake yawanci idan zai koma tafiyar asubanci yake yi shiyasa tun dare ya yi kokarin shirya jakar kayansa kamar yadda ya saba, bayan ya kammala haɗa komai ya fita zuwa part din mommy iya Manal ce kadai cikin falon tana kallo ya shiga ita kuma mommy din tana cikin kitchen, har cikin kitchen din ya bita cikin sanyin murya yace,
"mommy sannu da aiki......"
"yawwa"
"mommy na gama shiryawa gobe zan koma calabar..." ɗan sanyi mommy taji acikin ranta da taji cewa zai koma aiki gobe saboda bata son yaci gaba da zama auren nan da aka lankaya masa ya ɗore,
"Gara ka koma ai tunda zaman naka anan baida wani amfani..."
"insha Allah gobe zan tafi mommy...."
"Amma me yasa baka fada min da wuri ba, ai da anyi maka snacks kamar koda yaushe...."
"babu komai mommy, hajiya ta bani...."
"to shikenan"
Ganin yanda mommy din ta dan sauko har tana tarairayarsa yasa ya dan ji sanyi da dadi cikin ransa, 12 na dare ya kwanta bayan ya saita alarm dan yana son ya tashi kafin asubah tayi saboda gudun makara sai dai amma baccin yaƙi zuwar masa a maimakonshi ma tunani yaji yana ta bijiro masa cikin wannan lokaci wanda gaba ɗaya akan lamarinsu ne da ya shafi yaya Aliyu haidar, Anty Mimi da kuma shi, tun farko mema yasa ya yarda har yaji tausayinsu ya karɓi wannan tayin nasu? Juyi kawai yake ta faman yi har misalin karfe 1 da rabi na dare, da ya tabbatar baccin ba zai dauke shi a wannan lokaci ba sauka yayi daga kan gadon nasa ya shiga bathroom ya dauro alwala ya fito, sallar nafila yayi raka'a biyu sannan ya samu wuri ya zauna kan abin sallar tashi yana mai cigaba da yin addu'o'i har 3 saura kuma sai lokacin ya dan ji bacci a idanuwansa babu ɓata lokaci ya koma saman gadon shi ya kwanta, makara ya so yi saboda bai kwanta da wuri ba amma dai da kyar ya iya tashi ya shirya ya fita bayan yayi salla, sun yi sallama da kowa na gidan sannan ya tafi yana ji a cikin zuciyarsa wannan tafiyar tashi itace zata bawa zuciyar mommy damar hucewa cikin kankanin lokaci.
Yaya Aliyu tun ranar da aka ɗaurawa Afeef da anty Mimi aure ya fara jera lissafi wato ranar da ya dace Afeef ya saketa kamar yadda suka yi alƙawari, cikin bedroom dinta yake kwana hotunanta kafe a kowacce kusurwa ta bangon ɗakin, wani lokacin su kwana suna waya wata rana kuma su raba dare suna waya saboda irin dafin soyayyar da kowannensu ke ji cikin ransa, haka da rana da safe da yamma baya samun sukuni komai kankantarsa har sai ya kirata yaji muryar ta, sosai yanzu take jin abun yana bata tsoro dan kamar wanda Aliyun ya zautu abubuwan da yake yi a kanta sun fara wuce lissafin hankali,
Tun tana cikin bathroom tana wanka taji yana kiranta amma bata dauka ba saboda ta makara yau sosai kuma ba kowane ya makarar da ita ba face shi saboda shine ya hanata bacci suna ta faman hira har asubah, gashi yau akwai aiki shiyasa take ta sauri bata tsaya wani daukar wayar shi ba, cikin sauri ta fita ta bar gidan ta tafi asibiti kuma tana zuwa ta shiga theater, shi kuma ganin yana ta kiranta bata dauka ba yasa shi fita daga gida ya nufi asibiti dan ya san tana can tunda yau akwai aiki, daga shi sai kayan bacci ya shiga motar sa ya figeta zuwa asibiti, ta shiga theater dan haka ya zauna yana jiranta wanda ba ita ta fito ba sai 12,
"Aliyu yau baza ka fita aiki bane?" ta fada tana kallon sa bayan ta zauna kan kujerar ta,
"wallahi zan je aiki My love, in fact ma akwai wani important meeting da nake dashi but ba zan iya zuwa ba mutukar ban jiki ko kuma na ganki ba..." girgiza kai tayi cike da tausayinshi tace,
"Am fine... Dan Allah ka daina wasa da aikin ka, ina nan lafiya lau...."
"ta yaya zan iya tabbatar da hakan alhali ban sameki ba koda a waya ne?"
"Kaga ai na shiga theater ne and you know idan na fito dole zan kiraka back...."
Ajiyar zuciya ya sauke ya kalle ta cikin sanyin murya yace,
"insha Allah saura 1 week daidai Afeef ya sake ki kamar yadda muka shirya......"
"Babu problem, Allah ya kaimu...."
"yana nan ma kuwa? 2 days bana ganinsa, ko ciwon nashi ne ya tashi ko ya motsa? Bari na kirashi naji...." wayar shi ya dauka dake ajiye kan teburinta ya fara kiran layin Afeef..........✍️
KAIFI ƊAYA... ✨
*When the world called her “useless”… he called her “mine.”*💘
_KAIFI ƊAYA_ is not just a love story. It’s the story of Mimi - a doctor whose name was dragged through scandal, whose body was broken by fate… 💔
And Afeef - the man who chose to stay when everyone told him to leave. 😥
They won the fight against the world.
But can they win the fight for each other, when silence is louder than lies, and love is tested by things neither of them chose? 🥺
*One blade. One choice. One love that refuses to break.*❤️
_Kaifi Daya_ - because true love doesn’t walk away when you can’t walk anymore..😥
It's available now 07044644433
Your heart will not be the same after the last page🥰✍🏻✍🏻
#Kaifi ɗaya
#lovetriangle
#DrMimiAndAfeef
_*Ummi Shatu*_👌🏻
[7/18, 8:56 AM] Oum Jasrah: https://www.arewapen.com/book?id=6a50f2f571e75baab6622006
_A story of scandal, sacrifice and a love that refused to break, a love that says am still here._
KAIFI ƊAYA.....
NA
UMMI A'ISHA
8
***Zuba masa ido tayi kawai tana kallonsa cikin ranta tana jin wani irin bala'in tausayinshi saboda yana yin abu kamar wani wanda ya ɗan taɓu ko kuma ya zautu banda haka yanzu kalli fa a yanda ya fito ya taho office dinta dan kawai ya kirata a waya bai jita ba,ɗan tsakin da taji ya ja ne ya dawo da ita cikin hayyacinta,
"wannan yaron ko bacci yake yi bai tashi bane..... Na kira tana ta ringing bai yi picking ba"
"may be bai tashi daga bacci ba...."
"amma anya kuwa yana gari..... Nifa bana ganin shi ko a family house"
"shine dai nima ban sani ba dan na jima ban ganshi ba nima...."
"to babu matsala dai, zuwa anjima zan sake taɓa shi inji"
"ok"
"bari naje gida na shirya na fita office"
"ok to thank you"
Tashi yayi ya fita amma sai faman waiwayenta yake yi kamar yau ne ya fara ganin ta yayin da ita kuma ta janyo wani file ta bude ta fara rubutu aciki.
Bayan da Afeef ya koma bakin aikinsa gaba daya tattara maganar aurenshi da anty Mimi yayi ya ajiye a gefe dan a takaice ma shi ya manta da cewar akwai wani aurenta a kansa, baya waya da kowa sai Irfan kadai idan ya samu lokaci sai kuma mommy da daddy suma din kawai yana kiran su ne saboda ya kwantar musu da hankali domin duk ranar da basu ji shi ba hankalinsu tashi yake suyi ta tunanin ko ba ƙalau ba,kusan kullum sai yaga miss calls din yaya Aliyu amma bai taba kiran sa back ba abinda ya fara ƙonawa yaya Aliyun rai kenan shida anty Mimi dan a ganinsu wannan rainin wayo ne dan suna neman abu a wurin shi bashi ne zai bashi lasisi ko kuma damar wulakanta su ba yadda yaso,
Misalin ƙarfe 1 harda rabi na dare ya kira Irfan, yana kwance cikin dakinshi kuma dawowarshi kenan daga aiki, jin Irfan ya daga wayar ya sashi yin murmushi kafin a hankali yace,
"wai bacci kake yi?"
"wallahi idona biyu yanzun nan naje na dauko anty Mimi daga hospital na dawo da ita gida....." ai sai lokacin Afeef ya tuna da maganar auran shi da ita da kuma uban kiran wayar da yaya haidar ke ta faman yi masa babu dare ba rana,
"ohh matata ka dauko min daga aiki kenan.... Thank you for taking good care of her for me....."
Dariya Irfan yayi yace "you see your life?"
"yanzu dai menene labari? How is everyone? Ya anty Mimi hope she's fine?"
"baka da number dinta ne kake tambayata? Call her and ask....."
"yanzu ma sai da na gama waya da ita before na kiraka" ya fada cike da tsokana,
"kamar gaske...."
"am serious young man"
"yanzu dai wai zuwa yaushe zaka dawo?"
Ɗan dogon numfashi ya ja sannan a hankali yace "i don't know gaskiya.... I can't say, but idan na samu time zan zo"
Sun jima suna hira kafin suka yi sallama kowannensu ya ajiye waya, Irfan tunani yake yi cikin ransa anya kuwa anty Mimi da Afeef suna communicating? Dan bai ga alamar hakan ba dan baya mantawa tafiyar Afeef dinma shi take tambaya wai abokinsa yana nan kuwa taga bata ganin shi kwana biyu shi kuma yace ai ya koma calabar bai yi mata sallama bane? Daga haka yaga tayi shiru bata sake yin maganar ba,
A bangaren Afeef kuwa yana ajiye waya ya ɗan yi shuru na wasu yan mintuna kamar me yin tunani, iya gajeren wando ne a jikinsa tashi zaune yayi yana shawarar to ko ya kira yaya Aliyu yanzu? To kuma idan ya kirashi yanzu anya dare bai yi ba? Fasa kiran nasa yayi ya koma ya kwanta kan yar karamar katifarshi, kullum shi kadai yake kasancewa a ɗan karamin dakin nashi saboda tarbiyar da iyayenshi suka bashi duk wata rayuwar shashanci bata burge shi kuma baya cudanya da ita.