Sashe 53
Gurbin Ido Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Idanunsa ya buda a hankali sanda akayi yaji ana scanning key din office din nasa,qofar kuma ta bada qara alamun an budeta kenan,bai wani motsa ko kuma ya damu ba,saboda yasan duk duniya mutum daya ya bawa wannan damar wato jabir,shi dinne kuwa,ya sako kai cikin office din bakinsa dauke da sallama,hannunsa dauke da file yayin da idanunsa suke kan fuskar ja'afar,yayi kyau shima cikin tashi suit din da take kamanceceniya data ja'afar,ya qara haske da kuma qiba yayi fresh,alamun duk yadda yakeso haka take samuwa a gareshi.
Bakinsa ya motsa yana amsa sallamar tasa,kana ya miqe tsaye sosai saman qafafunsa,ya sanya hannu a nutse ya maida littafin inda ya daukoshi,ya rufe sannan yafara takawa zuwa kujerarsa,jabir din na biye dashi da idanuwa,yana kuma karantarsa,ransa da zuciyarsa na masa rashin dadi,don ko kowa baice komai dashi ba,yasan akwai abinda ya motsa zuciyar ja'afar din.
Sai da ya zauna sosai sannan ya tura file din gaban
"An gama hada komai,na gama nawa signing din,saura naka,zaka duba inda yake da gyara sai kayi,ka saka hannu mu miqa musu takardun, withing one to two weeks ya kamata a gama" ya qarshe maganar yana maida dubansa ga wayarsa daya zarota daga aljihu,saboda qarar shigowar text,murmushi ya subuce masa ya buda text din yana dubawa,yayin da hankalinsa kacokam ya koma kan wayar tasa,abinda yaja hankalin ja'afar,ya tsaya ya zuba masa ido,kana yadan bugi table din dake tsakaninsu.
Daga kai jabir din yayi yana dubansa,har yanzu murmushi bai bar kan fuskarsa ba
"Ina jinka"
"Baka tare dani" ya amsa masa kai tsaye da tsayayyar muryar nan tasa
"Yes.....gaskiya ne,hankalina bai wajen magana ta gaskiya,yanzu me ya rage?,inason naje gida lunch ana jirana" zube masa idanunsa yayi sosai kafin ya janyesu,kana yace masa
"Kana iya tafiya" da wani irin low tune da ya sanya tausayinsa sauka a zuciyar jabir,yafi kowa sanin yadda shaheeda tayi tattalinsa a lokacin rayuwarsa harma fiye da haka,amma a yanzu duka yayi loosing wannan caring din,dole abubuwan su dinga tabashi,duk da cewa shi yaqi bada wannan damar,yana da hope akan maimunatu shima kamar yadda yaji anni tana fada,ya sake samun gamsuwa akan yarinyar tun ranar da suka zauna sukayi magana ne tsaho a kanta da anni amma ya tattarata ya kaita makarantar kwana,annin kuma ta hana kowa masa magana,tace su xuba masa idanu suga iya nasa gudun ruwan.
A dan shurun da ya ratsa ta tsakaninsu ne tex ya shigo tasa wayar shima,sai ya jawota yana dubawa,qaramin tsaki yaja
"this is nonsense" furucin ya fita can qasan maqoshinsa,idan ba kunne kasa sosai ba ba zaka ji me yake fada ba,kira yayi ya aje wayar saman table bayan ya sakata a loud speaker,bugu biyu ya daga
"Me kake cewa ne?,ace duk gidan a rasa me daukota?" Yace da hisham kai tsaye,lumshe idanunsa hisham yayi daga wancan bangaren kafin ya amsa shi
"Babu yaaya,drivers din duka sun fita tare da abba,yana da baqin da suke zirga zirga dasu,ni kuma nan da minti goma akwai wanda zanwa surgery,kuma emergency ne har mutum biyu,kafin na gama kuma an ja lokaci" katse kiran kawai yayi,ya fara laluban number anty maama.
Itama bugu biyu ta daga suka gaisa
"Driver dinki yana kusa ki bani aronshi?"
"Wai.....ai kuwa yau tun sassafe ya debi yara abbansu yasa ya kaisu qauye"
"Ok" yace a gaggauce
"Akwai wani abu ne?"
"No,ki gaida yaran, thanks "
"Okay" itama ta bishi dashi,tasan halin kayanta fes,bama fadar zaiyi ba
"Waye ya bawa drivers na gidan nan hutu ne gaba dayansu?" Ya jefawa jabir dake nanuqe da wayarsa yana maidawa fatimansa reply na dinta tambayar,sai a sannan ya daga kai ya dubeshi,duk nema neman drivers da yakeyi yana jinsa,ya kuma san dalilin hakan,don kusan da goyon bayansa anni tayi wannan hukuncin
"Hey man,kai ne mana?,ka manta kenan ka zauna ka sani a gaba zaka fara tuhuma?" Tsaki ya sake ja yana tattare files din da suke gabansa
"Bari na fito maka a mutum,duk wannan goce gocen da kake bazai maka bafa,ka tashi kaje dauko yarinyar mutane kawai,three months bata nan amma don zaka bata just thirty to fourty minutes ka daukota a school sai ya gagara saboda adalci irin naka?" Wani kallo ya masa,tunda yaji amsar daya bayar yasan da issue din kenan,sai ya dakata daga hada takardun
"Idan kaji haushi me zai hana kaje kai" dariya ya sake sosai
"Ba dole na bace,ga dole na can tana jirana,kuma inda itace da tuni na tsufa a school din,don bazan bari Allah ya kamani da laifin rashin sauke haqqin dake wuyana ba" yana gama sai ya miqe yana 'yar dariyarsa zai fice daga office din,har ya kusa qofa sai ya tsaya
"Da zaka zo sai mu wuce gida tare ka fara yin lunch kafin ka tafi" ya fada with full caring in his voice,saidai kallo dayan da ja'afar yayi masa ya bashi amsarsa,sai ya kada kai kawai ya fice a office din yana murmushi,ya gode Allah daya bashi juriya da hikimar zama da ja'afar din,mutumin da yake jinsa tamkar cikin mahaifa guda suka kwanta dashi.
Riqe da suit dinsa a hannu ya fito,kana ya sauko kai tsaye zuwa floor din qarshe ya kuma wuce parking lot na ma'aikatar,key dinsa already yana hannunsa,tunda ya sallami driver dinsa,don yau din ya tsara lokacin tashinsa,zai iya kaiwa dare,don haka ya bashi umarnin tafiya idan akai azahar,sai gashi kuma wani abun da babu shi cikin schedule dinsa na yau ya taso masa.
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: *GURBIN IDO*
37
*AREWABOOKS:HUGUMA*
https://arewabooks.com/chapter?id=6364b8542730d61e0981706d
______________
Sanda sukai jarabawar first semester ta goma sha biyar tazo cikin su arba'in,ko kadan hakan bai mata dadi ba,saboda ta saba,har ta gama rayuwar primary dinta bata wuce ta biyar,bata nunama kowa ba sai aminanta kuma roommates dinta,afra ce tace
"Naga qoqarinki ma maimoon(sunan da suka koma ce mata kenan),a wata uku kacal kin doke mutum ashirin da biyar?" Kai ya girgiza sanda take hada kayanta,don a gobe kowa zai wuce gida hutu
"Ina qoqari a nan afreen(sunan da ita dinma take kiranta dashi),bazan iya nunawa kowa result dina ba"
"Zaki iya maimoon,i trust you,duk wanda ya iya arabic,boko bazai bashi wahala ba sam sam sam,boko minor abune akan arabic"
"Next time I will try my best in sha Allah" ta amsa mata tana sakar mata murmushi,tare da jin dadin irin qwarin gwiwar da ko yaushe afra take bata.
Washegari tana ta zuba idanun ganin wanda zayazo daukarta saiga yaa hisham,ya fito suka gaisa dasu afra,ya kuma gabatar musu da kansa da kansa a matsayin yayan maimunatu,sosai abun ya mata dadi,ya girmamasu ya kuma mutuntasu a mazauninsu na aminanta,su kansu sun nuna jin dadin hakan,afra taso su gaisa da 'yan gidansu,suga kuma sabuwar aminiyarta,to amma ya hisham din ya bada uzurin yana da patient da zai gani,dole sukayi sallama suka shiga mota.
Yana qoqarin tada motar ya lura da envelope din hannunta,wadda ke dauke da tambarin makarantar,sai ya miqa hannu
"Duk da ba'ayimin tayin ganin result din ba,nayi shishshigi,a bani na gani" idanu tadan zaro,ta yima kanta alqawarin babu wanda zai gani,har sai tayi abun arziqi,amma tana jin nauyin hisham din
"Ya hisham,don Allah.....ka bari sai next term saina hada maka da wannan din duka ka gani gaba daya" ta fada tana marairaice masa,wanda har ga Allah ita din batasan tayi ba,kamar yadda batasan mugun kyan da hakan ya qara mata ba,har sai daya janye idanunsa da sauri daga fuskarta yana fadin
"Subhanallah" cikin ransa ya furtata a hankali
"Ba matsala,Allah ya nuna mana" yadda taga yayi maganar yana tada motar ba tare da ya sake waiwayowa ba yasa taji babu dadi cikin ranta,sai taji kamar bata kyauta masa ba,don haka ta zaro ta miqa masa,sannan tayi qas da kanta tana jiran jin maganar da zai fada mata
"Kinyi qoqari sosai,ma sha Allah,wannan ne karonki na farko fa?" Ya fada cikin nuna qwarin gwiwa da kuma qarfafata,maganar tazo mata a ba zata,ta kuma bata mamaki,sannan kuma taji dadi gaki da sake samun qwarin gwiwa.
Ta zaci gidan abbi zai kaita,sai taga ya wuce da ita gidanta,bata tambayi dalili ba,bayan ya aje ta tayi masa godiya,ta kuma bashi saqon gaisuwa wajensu anni,tare da roqonsa a kawo mata amna.
Gyare gyare ta shiga yi,irin na mutumin da ya kwan biyu baya waje,sai data gama komai sannan ta sake wanka,ta kuma wuce kitchen ganin azahar har ta gota don ta samawa kanta abinda zataci.
Har zata shiga ta tuna da unaisa,sai taga bai dace tana cikin gida ba amma batasan da dawowarta ba,ko banza ta girme meta a shekaru,wannan tunanin yasa ta karkata akalarta zuwa sashen unaisan.
Knocking biyu aka tambayi waye,kai tsaye ta amsa da itace maimunatu,sai da aka dauki mintuna sannan ta bata izinin shigowa.
Zaune take saman doguwar kujerar falon nata,ta miqe qafafunta akai tana shan lemon fata,da alama tun dazun a hakan take a zaune,kawai dai batayi niyyar bata izinin shigowar bane,kallo daya tayi mata ta canza fuska ta kuma kau da kanta taci gaba da kallonta ga tv.
Koda ta gaisheta sama sama ta amsa
"Na dawo,nace bari na shigo na sanar miki" wata dariya ce ta zowa unaisa,ya tabbata ja'afar din mugun dan rainin hankali ne,hakazalika da biyu ya dauki yarinyar ya kaita makarantar kwana saboda ya raina ajinta da kwanyarta,to amma hakan yayi mata ita din,tunda ko banza kawo yanzun tana dan samun wasu sauye sauyen,duk da cewa ko sau daya bau taba hada dakin kwana da ita ba
"To yayi" tace mata kawai taci gaba da shan lemonta tana kada qafa gami da ci gaba da kallonta,ganin babu wani magana data sake hadasu sai maimunatun ta miqe zata fita
"Agwai" ta kirayeta da sunan da maimunatun tafita sanin me sunan yake nufi,sunan yadan sosa ranta,amma bata nuna ba ta waiwayo tana dubanta
"Am please idan kin tashi girkinki,ki dinga yi iya cikinki,wanda naci a baya ma shahada nayi,don ba abinci kowanne irin mutum nake ci ba,so ina da masu aiki,zasu dinga yin komai" kai ta gyada sannan tayo gaba tana bar mata dakinta.
Ga mamakinta sai taji maganganun unaisa sun dan sosa ranta kadan,abinda tun tasowarta da irin cin zarafin data gamu dashi a rayuwa bata taba jinsa akan kowa ba,ko hakan yana da nasaba da zama dasu afra?,hakan na nufin ta fara sanin kanta da kuma sanin mene ne rayuwa?. Muje zuwa dai.
Bakinsa ya motsa yana amsa sallamar tasa,kana ya miqe tsaye sosai saman qafafunsa,ya sanya hannu a nutse ya maida littafin inda ya daukoshi,ya rufe sannan yafara takawa zuwa kujerarsa,jabir din na biye dashi da idanuwa,yana kuma karantarsa,ransa da zuciyarsa na masa rashin dadi,don ko kowa baice komai dashi ba,yasan akwai abinda ya motsa zuciyar ja'afar din.
Sai da ya zauna sosai sannan ya tura file din gaban
"An gama hada komai,na gama nawa signing din,saura naka,zaka duba inda yake da gyara sai kayi,ka saka hannu mu miqa musu takardun, withing one to two weeks ya kamata a gama" ya qarshe maganar yana maida dubansa ga wayarsa daya zarota daga aljihu,saboda qarar shigowar text,murmushi ya subuce masa ya buda text din yana dubawa,yayin da hankalinsa kacokam ya koma kan wayar tasa,abinda yaja hankalin ja'afar,ya tsaya ya zuba masa ido,kana yadan bugi table din dake tsakaninsu.
Daga kai jabir din yayi yana dubansa,har yanzu murmushi bai bar kan fuskarsa ba
"Ina jinka"
"Baka tare dani" ya amsa masa kai tsaye da tsayayyar muryar nan tasa
"Yes.....gaskiya ne,hankalina bai wajen magana ta gaskiya,yanzu me ya rage?,inason naje gida lunch ana jirana" zube masa idanunsa yayi sosai kafin ya janyesu,kana yace masa
"Kana iya tafiya" da wani irin low tune da ya sanya tausayinsa sauka a zuciyar jabir,yafi kowa sanin yadda shaheeda tayi tattalinsa a lokacin rayuwarsa harma fiye da haka,amma a yanzu duka yayi loosing wannan caring din,dole abubuwan su dinga tabashi,duk da cewa shi yaqi bada wannan damar,yana da hope akan maimunatu shima kamar yadda yaji anni tana fada,ya sake samun gamsuwa akan yarinyar tun ranar da suka zauna sukayi magana ne tsaho a kanta da anni amma ya tattarata ya kaita makarantar kwana,annin kuma ta hana kowa masa magana,tace su xuba masa idanu suga iya nasa gudun ruwan.
A dan shurun da ya ratsa ta tsakaninsu ne tex ya shigo tasa wayar shima,sai ya jawota yana dubawa,qaramin tsaki yaja
"this is nonsense" furucin ya fita can qasan maqoshinsa,idan ba kunne kasa sosai ba ba zaka ji me yake fada ba,kira yayi ya aje wayar saman table bayan ya sakata a loud speaker,bugu biyu ya daga
"Me kake cewa ne?,ace duk gidan a rasa me daukota?" Yace da hisham kai tsaye,lumshe idanunsa hisham yayi daga wancan bangaren kafin ya amsa shi
"Babu yaaya,drivers din duka sun fita tare da abba,yana da baqin da suke zirga zirga dasu,ni kuma nan da minti goma akwai wanda zanwa surgery,kuma emergency ne har mutum biyu,kafin na gama kuma an ja lokaci" katse kiran kawai yayi,ya fara laluban number anty maama.
Itama bugu biyu ta daga suka gaisa
"Driver dinki yana kusa ki bani aronshi?"
"Wai.....ai kuwa yau tun sassafe ya debi yara abbansu yasa ya kaisu qauye"
"Ok" yace a gaggauce
"Akwai wani abu ne?"
"No,ki gaida yaran, thanks "
"Okay" itama ta bishi dashi,tasan halin kayanta fes,bama fadar zaiyi ba
"Waye ya bawa drivers na gidan nan hutu ne gaba dayansu?" Ya jefawa jabir dake nanuqe da wayarsa yana maidawa fatimansa reply na dinta tambayar,sai a sannan ya daga kai ya dubeshi,duk nema neman drivers da yakeyi yana jinsa,ya kuma san dalilin hakan,don kusan da goyon bayansa anni tayi wannan hukuncin
"Hey man,kai ne mana?,ka manta kenan ka zauna ka sani a gaba zaka fara tuhuma?" Tsaki ya sake ja yana tattare files din da suke gabansa
"Bari na fito maka a mutum,duk wannan goce gocen da kake bazai maka bafa,ka tashi kaje dauko yarinyar mutane kawai,three months bata nan amma don zaka bata just thirty to fourty minutes ka daukota a school sai ya gagara saboda adalci irin naka?" Wani kallo ya masa,tunda yaji amsar daya bayar yasan da issue din kenan,sai ya dakata daga hada takardun
"Idan kaji haushi me zai hana kaje kai" dariya ya sake sosai
"Ba dole na bace,ga dole na can tana jirana,kuma inda itace da tuni na tsufa a school din,don bazan bari Allah ya kamani da laifin rashin sauke haqqin dake wuyana ba" yana gama sai ya miqe yana 'yar dariyarsa zai fice daga office din,har ya kusa qofa sai ya tsaya
"Da zaka zo sai mu wuce gida tare ka fara yin lunch kafin ka tafi" ya fada with full caring in his voice,saidai kallo dayan da ja'afar yayi masa ya bashi amsarsa,sai ya kada kai kawai ya fice a office din yana murmushi,ya gode Allah daya bashi juriya da hikimar zama da ja'afar din,mutumin da yake jinsa tamkar cikin mahaifa guda suka kwanta dashi.
Riqe da suit dinsa a hannu ya fito,kana ya sauko kai tsaye zuwa floor din qarshe ya kuma wuce parking lot na ma'aikatar,key dinsa already yana hannunsa,tunda ya sallami driver dinsa,don yau din ya tsara lokacin tashinsa,zai iya kaiwa dare,don haka ya bashi umarnin tafiya idan akai azahar,sai gashi kuma wani abun da babu shi cikin schedule dinsa na yau ya taso masa.
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: *GURBIN IDO*
37
*AREWABOOKS:HUGUMA*
https://arewabooks.com/chapter?id=6364b8542730d61e0981706d
______________
Sanda sukai jarabawar first semester ta goma sha biyar tazo cikin su arba'in,ko kadan hakan bai mata dadi ba,saboda ta saba,har ta gama rayuwar primary dinta bata wuce ta biyar,bata nunama kowa ba sai aminanta kuma roommates dinta,afra ce tace
"Naga qoqarinki ma maimoon(sunan da suka koma ce mata kenan),a wata uku kacal kin doke mutum ashirin da biyar?" Kai ya girgiza sanda take hada kayanta,don a gobe kowa zai wuce gida hutu
"Ina qoqari a nan afreen(sunan da ita dinma take kiranta dashi),bazan iya nunawa kowa result dina ba"
"Zaki iya maimoon,i trust you,duk wanda ya iya arabic,boko bazai bashi wahala ba sam sam sam,boko minor abune akan arabic"
"Next time I will try my best in sha Allah" ta amsa mata tana sakar mata murmushi,tare da jin dadin irin qwarin gwiwar da ko yaushe afra take bata.
Washegari tana ta zuba idanun ganin wanda zayazo daukarta saiga yaa hisham,ya fito suka gaisa dasu afra,ya kuma gabatar musu da kansa da kansa a matsayin yayan maimunatu,sosai abun ya mata dadi,ya girmamasu ya kuma mutuntasu a mazauninsu na aminanta,su kansu sun nuna jin dadin hakan,afra taso su gaisa da 'yan gidansu,suga kuma sabuwar aminiyarta,to amma ya hisham din ya bada uzurin yana da patient da zai gani,dole sukayi sallama suka shiga mota.
Yana qoqarin tada motar ya lura da envelope din hannunta,wadda ke dauke da tambarin makarantar,sai ya miqa hannu
"Duk da ba'ayimin tayin ganin result din ba,nayi shishshigi,a bani na gani" idanu tadan zaro,ta yima kanta alqawarin babu wanda zai gani,har sai tayi abun arziqi,amma tana jin nauyin hisham din
"Ya hisham,don Allah.....ka bari sai next term saina hada maka da wannan din duka ka gani gaba daya" ta fada tana marairaice masa,wanda har ga Allah ita din batasan tayi ba,kamar yadda batasan mugun kyan da hakan ya qara mata ba,har sai daya janye idanunsa da sauri daga fuskarta yana fadin
"Subhanallah" cikin ransa ya furtata a hankali
"Ba matsala,Allah ya nuna mana" yadda taga yayi maganar yana tada motar ba tare da ya sake waiwayowa ba yasa taji babu dadi cikin ranta,sai taji kamar bata kyauta masa ba,don haka ta zaro ta miqa masa,sannan tayi qas da kanta tana jiran jin maganar da zai fada mata
"Kinyi qoqari sosai,ma sha Allah,wannan ne karonki na farko fa?" Ya fada cikin nuna qwarin gwiwa da kuma qarfafata,maganar tazo mata a ba zata,ta kuma bata mamaki,sannan kuma taji dadi gaki da sake samun qwarin gwiwa.
Ta zaci gidan abbi zai kaita,sai taga ya wuce da ita gidanta,bata tambayi dalili ba,bayan ya aje ta tayi masa godiya,ta kuma bashi saqon gaisuwa wajensu anni,tare da roqonsa a kawo mata amna.
Gyare gyare ta shiga yi,irin na mutumin da ya kwan biyu baya waje,sai data gama komai sannan ta sake wanka,ta kuma wuce kitchen ganin azahar har ta gota don ta samawa kanta abinda zataci.
Har zata shiga ta tuna da unaisa,sai taga bai dace tana cikin gida ba amma batasan da dawowarta ba,ko banza ta girme meta a shekaru,wannan tunanin yasa ta karkata akalarta zuwa sashen unaisan.
Knocking biyu aka tambayi waye,kai tsaye ta amsa da itace maimunatu,sai da aka dauki mintuna sannan ta bata izinin shigowa.
Zaune take saman doguwar kujerar falon nata,ta miqe qafafunta akai tana shan lemon fata,da alama tun dazun a hakan take a zaune,kawai dai batayi niyyar bata izinin shigowar bane,kallo daya tayi mata ta canza fuska ta kuma kau da kanta taci gaba da kallonta ga tv.
Koda ta gaisheta sama sama ta amsa
"Na dawo,nace bari na shigo na sanar miki" wata dariya ce ta zowa unaisa,ya tabbata ja'afar din mugun dan rainin hankali ne,hakazalika da biyu ya dauki yarinyar ya kaita makarantar kwana saboda ya raina ajinta da kwanyarta,to amma hakan yayi mata ita din,tunda ko banza kawo yanzun tana dan samun wasu sauye sauyen,duk da cewa ko sau daya bau taba hada dakin kwana da ita ba
"To yayi" tace mata kawai taci gaba da shan lemonta tana kada qafa gami da ci gaba da kallonta,ganin babu wani magana data sake hadasu sai maimunatun ta miqe zata fita
"Agwai" ta kirayeta da sunan da maimunatun tafita sanin me sunan yake nufi,sunan yadan sosa ranta,amma bata nuna ba ta waiwayo tana dubanta
"Am please idan kin tashi girkinki,ki dinga yi iya cikinki,wanda naci a baya ma shahada nayi,don ba abinci kowanne irin mutum nake ci ba,so ina da masu aiki,zasu dinga yin komai" kai ta gyada sannan tayo gaba tana bar mata dakinta.
Ga mamakinta sai taji maganganun unaisa sun dan sosa ranta kadan,abinda tun tasowarta da irin cin zarafin data gamu dashi a rayuwa bata taba jinsa akan kowa ba,ko hakan yana da nasaba da zama dasu afra?,hakan na nufin ta fara sanin kanta da kuma sanin mene ne rayuwa?. Muje zuwa dai.