Sashe 49
Gurbin Ido Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*
Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300
*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank
*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902
*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107
*_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: *GURBIN IDO*
36
*Arewabooks:HUGUMA*
https://arewabooks.com/chapter?id=6364b7c12730d61e09816f8b
__________________________________
"barka da warhaka" anty maama ta fada,yadan saki muryarsa kadan,duk da haka akwai heaviness din nan a cikinta dake qara masa kwarjini ya amsa mata
"Barka kadai,yasu hamood"
"Kowa yana nan lafiya qalau"
"Ma sha Allah" ya amsata a taqaice,sai ta danyi shuru kuma,ita kanta wani lokaci kwarjini yake mata,duk kuwa da cewa duk irin miskilanci da zafin kai irin nasa bai taba qin bata girmanta ba,saidai babu wani dogon magana me yawa tun dacan a tsakaninsu,shi yasa lokuta da yawa hisham dinne abokin maganarta,amma tuna wannan attitude din nasa na respect ya bata nutsuwar cewa
"Muna tare ne da hisham,yanzun yake gayamin wai kaine kace akai maimunatu boarding school?"
"Maimunatu?"ya dan maimaita sunan,sai kuma yace
"Oh.....eh,hakane,abinda anni ta buqata kenan,komawarta makaranta"
"Amma sai nakega anni bawai tana nufin a kaita makarantar kwana ba ko?" Ta fada cikin kwantar da murya
"Ban sani ba gsky,na duba kawai makarantar dake da kyau ne,kuma sai naga kamar abun arziqi nayi" shuru tayi ta jinjina kai
"Shikenan,Allah ya rufa asiri"
"Qarata ya kawo kenan?" Ya jefa mata tambayar,saita gyada kanta da sauri
"A'ah sun dai biyo ne shi da ita mu gaisa"
"Ok,yayi" ya fada kana ya sauke wayar yana kashewa ba tare da yabi ba:asin me yasa suka biyo din ba,tunda basu gaya masan xasu biyo ba.
Gefe ya aje wayar yana duban titin lagos da suke ratsawa cikin sa'a yau babu cinkoso da yawa,sai yake jinsa sakayau,ya rufe case din wannan,saura dayar,ita dinma da bata wuce lavel don boarding din ba hadasu zaiyi ko xai samuu peace of mind,haka kawai ya samu yana lallaba rayuwarshi annin ta hadashi da aiki.
**********Bakwai da rabi na safiyar litinin a pen resources academy tayi musu ita da hisham wanda shine ya kawota da kanshi,sanye take da uniform dinta da duk wani abu da sabon dalibin boarding na private school zai buqata,ba wasu kaya bane masu yawa,saboda makarantar suna da tsari ba kamar government boarding school ba,makaranta ce ta wadanda sukaci suka tada kai,saboda haka duk wanda ka gani a cikinta ba dan kuci ku bamu bane.
Tunda suka shiga makarantar ta tabbatar da haka,duba da irin motocin da suke sauke daliban da a yau suka dawo daga hutun zangon qarshe na shekara.
Sai da aka kammala komai hatta daki aka bata hisham yana zaune,bayan ya tabbatar komai yayi settling ya dubeta,murmushi yadan qwace masa ganin yadda idanunta suka tara qwalla
"Zan koma matar babban yaaya,Allah ya bada sa'a,yasa a fara a sa'a" hakanan sai taji zuciyarta ta karye,kamar wadda aka kai nisan duniya,tana qoqarin maida qwallarta ta amsa da amin,tana nan a tsaye har ya isa motarsa ya budeta ya shiga,har ya tadata sai kuma ya kashe ya sake fitowa,hannunsa dauke da madaidaicin kwali ya miqa mata
"Na manta,ga waya koda zaki buqaci communicating da mutanen gida" wayar ta kalla sannan ta maida dubanta gareshi,wannan shine karo na farko da aka soma malllaka mata waya a rayuwarta,sai tasa hannu bibbiyu ta karba tana masa godiya
"Babu komai fa" ya sake amsa mata yana murmushi,har zuciyarsa yana jin tausayinta,tun dava randa laila ta bashi labarin wacece ita,sai data ga fitarsa a makarantar,sannan ta juya jiki a sanyaye,saita duba agogon dake daure tintsiyar hannunta,lokacin shiga aji yayi,don haka ta ciro school bag dinta dake saqale a bayanta ta cusa wayar a ciki sannan ta kama hanyar da classes dinsu yake.
Da sallama ta shiga ajin,sai ta dan tsaya tana dawurwura,don ajin adan hargitse yake da hayaniyar dalibai,wanda basu ma lura da wanda ya shigo din
Ta gefanta taji alamun shigowa,saita waiwaya kadan,daliba ce kamarta take shigowa ajin,hannunta dauke da water marker da kuma wasu litattafai,suka hada idanu saita dauke kanta,ta isa gaban allo ta zube marker din,sannan tazo zata giftata,har tadan gota ta waiwayo ta dubeta
"Sabuwar daliba?" A hankali maimunatun ta gyada mata kai,sai ta waiwaya tana duban cikin class din sannan ta sake maido dubanta gareta
"Ga seat din muje ciki" hakan ya bata damar bin bayanta,har suka isa gaban wani seat,sai taga ta zauna daga gefe,kamar yadda ta karanci duk set daya yana daukan mutum biyu ne
"Zauna a nan,akwai abokiyar zamana,amma dawowarmu wannan hutun ashe ba zata dawo ba,an canza mata makaranta,saiki maye gurbin wajenta" tace da maimunatu tana dauko jakarta gami da zugeea tana fiddo da sabin exercise tana dorsawa saman desk din
"Na gode" ta amsa mata a taqaice,cike da tsarguwan kallon qurillar da daliban ke binta da shi.
Tun zamansu a wajen ta fuskanci lokaci bayan lokaci sukan hada idanu da class captain din,wadda taji suna kira da afrah Ateeq Muhammad,tana taqaitawa da afrah A muhammad,duk sanda suka hada idanun sai ta dan sake mata murmushi kawai taci gaba da abinda takeyi,itama maida mata martani take,sai taji kallon bai dameta ba.
Lokacin break har tayi gaba sai ta dawo ganin maimunatu a zaune
"Zamuje dakin cin abinci,ko kinsan hanya?" Kai ta girgiza
"Okay,kina iya tasowa mu tafi"
"Na gode" ta fada tana miqewa,ta ajjiye jakarta tabi baya afran.
Abinda ta lura afra nada kirki,tana kuma da kyakkyawar mu'amala da jama'a,hakanan tana da mutane sosai,a nutse take,bata da tarin hayaniya ko rawar kai,tare suka gama cin abincin sannan suka dawo aji.
Karfe biyu aka tashi daga makaranta,masallacin cikin makaranta taga yawancin daliban suna tafiya,bataga afran ba,don gab da zaa tashi ta fita a class din,tana buqatar koyon wasu abubuwan da kanta,don haka sai kawai tabi sahun daliban itama ta wuce zuwa masallacin.
Batayi gaggawar barin masallacin ba sai data fuskanci lokacine na komawa daki kowa ya huta,ta dauki jakarta ta nufi inda dakunan kwanan dalibai mata yake,tana tafiya ne a hankali don kada ta bace a dakin,jifa jifa tana cin karo da dalibai a verender,duk wadda tazo giftatan kuma sai ta bita da kallo,a haka ta isa dakinsu,ta murza handle din sai taji qofar a bude take,ta tura da sallama tana shiga.
Madaidaicin daki ne,mai dauke da gadon kwanan dalibai guda hudu,shimfidadden tiles qaramin toilet da kuma locker ajiyar kaya da aka bawa kowanne dalibai,wutar na'urar solar da fankar sama dake juyawa a hankali,fes dakin yake sai qamshin freshener da yake fiddawa.
Gadon da yake qasan nata gadon tunda a sama take taga mutum a kwance,ta motsa sannan ta dago tana amsa sallamar tata,suka hada idanu,sai taga afra dince,murmushi tayi mata tana miqewa daga kwanciyar da tayi
"Ah,baquwa,ashe dakinmu daya?" Murmushin itama maimunatu ta maida mata
"Ban sani ba nima sai yanzu,dazun da nazo ajjiye kayana babu kowa a dakin"
"Yanzun ma saini kadai,su feena basu shigo ba,sun tsaya karbomin magani a pharmacy" afra ta fada tana dan yatsina fuska
"Ayyah,baki da lafiya ashe?"
"Wlh,yau duka daurewa kawai nakeyi,da ciwon mara na tashi" ta fada tana cije labbanta,da alama ciwon ya motsa mata ne
"Sannu,Allah ya sawwaqe"
"Ameen na gode" ta fada tana kwantar da kanta saman qafarta,maimunatu kuma ta matsa gaba kadan,ta taka gajerun steps din da suka sadata da gadonta,ta ajjiye jakarta ta kuma canza uniform din jikinta zuwa kayan gida a dan wajen da suka kebe saboda sauya kaya.
Leqawa ta sakeyi tana yiwa afra sannu,dai dai lokacin da wasu 'yammatan guda biyu suka shigo dakin bakunansu dauke da hira cai cai,da alama wata gulmar suka qunso daga waje suka shigo da ita.
Bin maimunatu sukayi da kallo,duk da a dazun sun ganta a aji,da alama suma suna mamakin ganinta a dakinsu,duk da dama sunsan akwai sauran space na abokiyar karatunsu data canza makaranta.
Itama dan bin nasu tayi da kallo,dukkansu kana dubansu zakasan cewa kowacce daga gidan gata ta fito basai an gaya maka ba,ta amsa sallamarsu tana debe idanunta daga kallonsu,suka qaraso kusa da afra,kusan a tare suka ce da maimunatu
"Sannu New roommate" murmushi tayi musu
"Sannunku"
"Sunana fatima baqo" sai dayar ma ta kama
"Ni kuma ummu ayman buhari" ta qarashe maganar tana miqa mata hannu
"Maimunatu Abubakar muhammad" ta amsa musu tana miqa musu nata hannun itama
"Nice meeting you" suka amsa fuska sake kaman sun saba da ita dama can.
To hausawa sukace juma'ar da zatayi kyau tun daga laraba ake ganeta,dukkan alamu sun nunawa maimunatu zataji dadin zama da abokan karatun nata ainun tun a waninsu na farko,wasu irin mutane ne masu sauqin kai da kuma dadin zama ainun,yadda suke nan nan da ita da kuma haba haba sai ka zaci an jima da haduwa tare.
Takeaway mai yawan gaske suka zube musu sukaci,sunayi suna duba jikin afrah,duk da cewa da sauqi saboda maganin data sha,har sukayi sallar la'asar,sannan suka fara shirin tafiya islamiyyar cikin makarantar,wadda suke shiga hudu na yammaci
"Inaga tunda ku kun saba zuwa,kuje kada ku rasa karatunku na yau,ni zan zauna da sister afra(ta fadi kamar yadda taji suna kiran juna),idan yaso ko zuwa gobe sai na fara zuwa"abunda ya yiwa afran dadi qwarai,ta kuma sake jin maimunatun cikin ranta fiye da daxun farkon zuwanta,bayan fitarsun kuwa hira suka dinga yi sosai da afran,a nan ta fahimci dukkansu 'ya'yan manya ne,sai maimunatun taji a ranta ya kamata ta kama kanta,tunda ita din ba 'yar kowan kowa bace,amma duk da hakan sai ta saki jikinta,ta dinga dan tambayar afran game da wasu abubuwa na makarantar,ta samu haske kuwa sosai,don su tun daga js one suka fara,ba kamar ita ba data datsi ss one.
Ta fahimci team ne na masu son karatu aka hada daki guda,afra ayman da fatima,wannan yasa itama ta sake jaddada niyyarta na zage damtse tare da yin karatu tuquru haiqan,son karatunsu ne ya sanya a aji suka raba set,don kada suje kasa maida hankali,kowacce a cikinsu akwai babban alqawarin da aka yi mata daga gida na idan ta gama ta fita da sakamako me kyau a dukka record nata,to zata zabi duk abinda takeso kuma shi za'a bata,wannan yasa a tsakaninsu duk term ake samun first second and third position,saidai sukanyi exchange a tsakaninsu wata ta karbe position din wata.
Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300
*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank
*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902
*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107
*_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: *GURBIN IDO*
36
*Arewabooks:HUGUMA*
https://arewabooks.com/chapter?id=6364b7c12730d61e09816f8b
__________________________________
"barka da warhaka" anty maama ta fada,yadan saki muryarsa kadan,duk da haka akwai heaviness din nan a cikinta dake qara masa kwarjini ya amsa mata
"Barka kadai,yasu hamood"
"Kowa yana nan lafiya qalau"
"Ma sha Allah" ya amsata a taqaice,sai ta danyi shuru kuma,ita kanta wani lokaci kwarjini yake mata,duk kuwa da cewa duk irin miskilanci da zafin kai irin nasa bai taba qin bata girmanta ba,saidai babu wani dogon magana me yawa tun dacan a tsakaninsu,shi yasa lokuta da yawa hisham dinne abokin maganarta,amma tuna wannan attitude din nasa na respect ya bata nutsuwar cewa
"Muna tare ne da hisham,yanzun yake gayamin wai kaine kace akai maimunatu boarding school?"
"Maimunatu?"ya dan maimaita sunan,sai kuma yace
"Oh.....eh,hakane,abinda anni ta buqata kenan,komawarta makaranta"
"Amma sai nakega anni bawai tana nufin a kaita makarantar kwana ba ko?" Ta fada cikin kwantar da murya
"Ban sani ba gsky,na duba kawai makarantar dake da kyau ne,kuma sai naga kamar abun arziqi nayi" shuru tayi ta jinjina kai
"Shikenan,Allah ya rufa asiri"
"Qarata ya kawo kenan?" Ya jefa mata tambayar,saita gyada kanta da sauri
"A'ah sun dai biyo ne shi da ita mu gaisa"
"Ok,yayi" ya fada kana ya sauke wayar yana kashewa ba tare da yabi ba:asin me yasa suka biyo din ba,tunda basu gaya masan xasu biyo ba.
Gefe ya aje wayar yana duban titin lagos da suke ratsawa cikin sa'a yau babu cinkoso da yawa,sai yake jinsa sakayau,ya rufe case din wannan,saura dayar,ita dinma da bata wuce lavel don boarding din ba hadasu zaiyi ko xai samuu peace of mind,haka kawai ya samu yana lallaba rayuwarshi annin ta hadashi da aiki.
**********Bakwai da rabi na safiyar litinin a pen resources academy tayi musu ita da hisham wanda shine ya kawota da kanshi,sanye take da uniform dinta da duk wani abu da sabon dalibin boarding na private school zai buqata,ba wasu kaya bane masu yawa,saboda makarantar suna da tsari ba kamar government boarding school ba,makaranta ce ta wadanda sukaci suka tada kai,saboda haka duk wanda ka gani a cikinta ba dan kuci ku bamu bane.
Tunda suka shiga makarantar ta tabbatar da haka,duba da irin motocin da suke sauke daliban da a yau suka dawo daga hutun zangon qarshe na shekara.
Sai da aka kammala komai hatta daki aka bata hisham yana zaune,bayan ya tabbatar komai yayi settling ya dubeta,murmushi yadan qwace masa ganin yadda idanunta suka tara qwalla
"Zan koma matar babban yaaya,Allah ya bada sa'a,yasa a fara a sa'a" hakanan sai taji zuciyarta ta karye,kamar wadda aka kai nisan duniya,tana qoqarin maida qwallarta ta amsa da amin,tana nan a tsaye har ya isa motarsa ya budeta ya shiga,har ya tadata sai kuma ya kashe ya sake fitowa,hannunsa dauke da madaidaicin kwali ya miqa mata
"Na manta,ga waya koda zaki buqaci communicating da mutanen gida" wayar ta kalla sannan ta maida dubanta gareshi,wannan shine karo na farko da aka soma malllaka mata waya a rayuwarta,sai tasa hannu bibbiyu ta karba tana masa godiya
"Babu komai fa" ya sake amsa mata yana murmushi,har zuciyarsa yana jin tausayinta,tun dava randa laila ta bashi labarin wacece ita,sai data ga fitarsa a makarantar,sannan ta juya jiki a sanyaye,saita duba agogon dake daure tintsiyar hannunta,lokacin shiga aji yayi,don haka ta ciro school bag dinta dake saqale a bayanta ta cusa wayar a ciki sannan ta kama hanyar da classes dinsu yake.
Da sallama ta shiga ajin,sai ta dan tsaya tana dawurwura,don ajin adan hargitse yake da hayaniyar dalibai,wanda basu ma lura da wanda ya shigo din
Ta gefanta taji alamun shigowa,saita waiwaya kadan,daliba ce kamarta take shigowa ajin,hannunta dauke da water marker da kuma wasu litattafai,suka hada idanu saita dauke kanta,ta isa gaban allo ta zube marker din,sannan tazo zata giftata,har tadan gota ta waiwayo ta dubeta
"Sabuwar daliba?" A hankali maimunatun ta gyada mata kai,sai ta waiwaya tana duban cikin class din sannan ta sake maido dubanta gareta
"Ga seat din muje ciki" hakan ya bata damar bin bayanta,har suka isa gaban wani seat,sai taga ta zauna daga gefe,kamar yadda ta karanci duk set daya yana daukan mutum biyu ne
"Zauna a nan,akwai abokiyar zamana,amma dawowarmu wannan hutun ashe ba zata dawo ba,an canza mata makaranta,saiki maye gurbin wajenta" tace da maimunatu tana dauko jakarta gami da zugeea tana fiddo da sabin exercise tana dorsawa saman desk din
"Na gode" ta amsa mata a taqaice,cike da tsarguwan kallon qurillar da daliban ke binta da shi.
Tun zamansu a wajen ta fuskanci lokaci bayan lokaci sukan hada idanu da class captain din,wadda taji suna kira da afrah Ateeq Muhammad,tana taqaitawa da afrah A muhammad,duk sanda suka hada idanun sai ta dan sake mata murmushi kawai taci gaba da abinda takeyi,itama maida mata martani take,sai taji kallon bai dameta ba.
Lokacin break har tayi gaba sai ta dawo ganin maimunatu a zaune
"Zamuje dakin cin abinci,ko kinsan hanya?" Kai ta girgiza
"Okay,kina iya tasowa mu tafi"
"Na gode" ta fada tana miqewa,ta ajjiye jakarta tabi baya afran.
Abinda ta lura afra nada kirki,tana kuma da kyakkyawar mu'amala da jama'a,hakanan tana da mutane sosai,a nutse take,bata da tarin hayaniya ko rawar kai,tare suka gama cin abincin sannan suka dawo aji.
Karfe biyu aka tashi daga makaranta,masallacin cikin makaranta taga yawancin daliban suna tafiya,bataga afran ba,don gab da zaa tashi ta fita a class din,tana buqatar koyon wasu abubuwan da kanta,don haka sai kawai tabi sahun daliban itama ta wuce zuwa masallacin.
Batayi gaggawar barin masallacin ba sai data fuskanci lokacine na komawa daki kowa ya huta,ta dauki jakarta ta nufi inda dakunan kwanan dalibai mata yake,tana tafiya ne a hankali don kada ta bace a dakin,jifa jifa tana cin karo da dalibai a verender,duk wadda tazo giftatan kuma sai ta bita da kallo,a haka ta isa dakinsu,ta murza handle din sai taji qofar a bude take,ta tura da sallama tana shiga.
Madaidaicin daki ne,mai dauke da gadon kwanan dalibai guda hudu,shimfidadden tiles qaramin toilet da kuma locker ajiyar kaya da aka bawa kowanne dalibai,wutar na'urar solar da fankar sama dake juyawa a hankali,fes dakin yake sai qamshin freshener da yake fiddawa.
Gadon da yake qasan nata gadon tunda a sama take taga mutum a kwance,ta motsa sannan ta dago tana amsa sallamar tata,suka hada idanu,sai taga afra dince,murmushi tayi mata tana miqewa daga kwanciyar da tayi
"Ah,baquwa,ashe dakinmu daya?" Murmushin itama maimunatu ta maida mata
"Ban sani ba nima sai yanzu,dazun da nazo ajjiye kayana babu kowa a dakin"
"Yanzun ma saini kadai,su feena basu shigo ba,sun tsaya karbomin magani a pharmacy" afra ta fada tana dan yatsina fuska
"Ayyah,baki da lafiya ashe?"
"Wlh,yau duka daurewa kawai nakeyi,da ciwon mara na tashi" ta fada tana cije labbanta,da alama ciwon ya motsa mata ne
"Sannu,Allah ya sawwaqe"
"Ameen na gode" ta fada tana kwantar da kanta saman qafarta,maimunatu kuma ta matsa gaba kadan,ta taka gajerun steps din da suka sadata da gadonta,ta ajjiye jakarta ta kuma canza uniform din jikinta zuwa kayan gida a dan wajen da suka kebe saboda sauya kaya.
Leqawa ta sakeyi tana yiwa afra sannu,dai dai lokacin da wasu 'yammatan guda biyu suka shigo dakin bakunansu dauke da hira cai cai,da alama wata gulmar suka qunso daga waje suka shigo da ita.
Bin maimunatu sukayi da kallo,duk da a dazun sun ganta a aji,da alama suma suna mamakin ganinta a dakinsu,duk da dama sunsan akwai sauran space na abokiyar karatunsu data canza makaranta.
Itama dan bin nasu tayi da kallo,dukkansu kana dubansu zakasan cewa kowacce daga gidan gata ta fito basai an gaya maka ba,ta amsa sallamarsu tana debe idanunta daga kallonsu,suka qaraso kusa da afra,kusan a tare suka ce da maimunatu
"Sannu New roommate" murmushi tayi musu
"Sannunku"
"Sunana fatima baqo" sai dayar ma ta kama
"Ni kuma ummu ayman buhari" ta qarashe maganar tana miqa mata hannu
"Maimunatu Abubakar muhammad" ta amsa musu tana miqa musu nata hannun itama
"Nice meeting you" suka amsa fuska sake kaman sun saba da ita dama can.
To hausawa sukace juma'ar da zatayi kyau tun daga laraba ake ganeta,dukkan alamu sun nunawa maimunatu zataji dadin zama da abokan karatun nata ainun tun a waninsu na farko,wasu irin mutane ne masu sauqin kai da kuma dadin zama ainun,yadda suke nan nan da ita da kuma haba haba sai ka zaci an jima da haduwa tare.
Takeaway mai yawan gaske suka zube musu sukaci,sunayi suna duba jikin afrah,duk da cewa da sauqi saboda maganin data sha,har sukayi sallar la'asar,sannan suka fara shirin tafiya islamiyyar cikin makarantar,wadda suke shiga hudu na yammaci
"Inaga tunda ku kun saba zuwa,kuje kada ku rasa karatunku na yau,ni zan zauna da sister afra(ta fadi kamar yadda taji suna kiran juna),idan yaso ko zuwa gobe sai na fara zuwa"abunda ya yiwa afran dadi qwarai,ta kuma sake jin maimunatun cikin ranta fiye da daxun farkon zuwanta,bayan fitarsun kuwa hira suka dinga yi sosai da afran,a nan ta fahimci dukkansu 'ya'yan manya ne,sai maimunatun taji a ranta ya kamata ta kama kanta,tunda ita din ba 'yar kowan kowa bace,amma duk da hakan sai ta saki jikinta,ta dinga dan tambayar afran game da wasu abubuwa na makarantar,ta samu haske kuwa sosai,don su tun daga js one suka fara,ba kamar ita ba data datsi ss one.
Ta fahimci team ne na masu son karatu aka hada daki guda,afra ayman da fatima,wannan yasa itama ta sake jaddada niyyarta na zage damtse tare da yin karatu tuquru haiqan,son karatunsu ne ya sanya a aji suka raba set,don kada suje kasa maida hankali,kowacce a cikinsu akwai babban alqawarin da aka yi mata daga gida na idan ta gama ta fita da sakamako me kyau a dukka record nata,to zata zabi duk abinda takeso kuma shi za'a bata,wannan yasa a tsakaninsu duk term ake samun first second and third position,saidai sukanyi exchange a tsakaninsu wata ta karbe position din wata.