← Book details Gurbin Ido Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 35 OF 113

Sashe 35

Gurbin Ido Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sanda ta fita din kuwa ko sallamewa daga sallar ba'ayi ba adan masallacin dake tsukin rugar tasu,sai a hanya dab da isarta gidan bappa labaran aka idar,ta kutsa kai gidan babu cikakkiyar sallama saboda bataso daadar tasan tazo,ta nufaci dakin yuuma kanta tsaye.

Dai dai lokacin da yuuma ke tsaye tana shirin zare hijabinta daga jikinta bayan ta idar da salla,yayin da anni ke saman abun salla tana lazumi itama.

Tsorata yuuma tayi da ganin furera a irin wannan lokacin,ta matsa da baya tana amsa sallamarta sanda ta shigo ta yiwa kanta mazauni,tsaf anni ta gane matar,don haka bata katse lazuminta ba sai data cika dari cif sannan ta sauke carbin bayan ta shafa,inna furera ta fara gaidata cikin tsantsar ladabi,anni ta amsa tana dubanta a kaikaice,don tana da tabbacin kome meye ya futo da ita da asussubar fari to ba alkhairi bane.

Rai rai ta fara jerowa anni maganganun da tun a jiyan ta gama shiryawa kanta game da maimunatu,da dukkan wata siga da zatayi baqi a idanunta,anni na kallon ta,bata ce da ita komai ba hakanan bata dakatar da ita ba,har sai data dasa aya

"Kin gama?" Anni ta tambayeta

"Eh....to shine naga gwara na shaida miki,tunda dai kinga amana ce ta hadamu,bai kamata na rufeki ba kada ubangiji ya tuhumeni,ni kaina yarinyar kaffa kaffa nake da ita da kuma neman maganin tsari daga maita,shine fa kikaga mun kawo har warhaka lafiya lau bata taba kowa a cikinmu ba"

Sosai yuuma dake zaune daga gefe ta cika tayi famm,fata take annin ta bata dama ta wanke furera mara tsoron Allah data iya kaikaicewa ta yankarowa jininta mummunar qazafi da qarya har haka saboda kawai zallar hassada da baqar zuciya

"Yanzu me kikeso ayi kenan?" Anni ta tambayeta cike da gatse,wanda ita furera bata fahinta ba,sai murna data saukar mata,ta kuma karkace ta gabatar mata da gajenta,bayan ta gama kodata

"Kinga dakata baiwar Allah,kiyi ta kanki kinji,banason wannan soki burutsun,banda ma baki da hankali........idan maimunatu mayya ce ku zaku kubuta ne?,ko ce miki akayi ba wanda yasan alaqarku da ita?" Gumin tashin hankali ne ya yankowa furera,ya akayi wata halitta tasan da wannan?dama kowa kallonta yake kenan?.

"Ai....to,ai dama ita din.....maitarta ta can jikin kakarta ne.....bawai daga ubanmu bane,daga kakarta ne......sai....sai ta tsotsa daga nonon uwarta itama"

"Ke!......ki kiyayeni fa?,wallahi tallahi ina sake jadda miki kiyi ta kanki,yo banda tambadewa irin taki,ina ake irin haka?,to bari kiji na gaya miki,ki kama.kanki,idan ba haka ba in na tashi tafiya billahuwallazi kaf garken maimunatu da uwarta da kika danne kike qafafa dasu sai nasa anyi awon gaba dasu,gwara ki.saita kanki aci gaba da tafiya ahaka,wata shari'ar sai a lahira" sosai jikin inna furere ya dauki bari jin ana shirin yi mata bankada.

Ta tambayi kanta Wanne tsinannen ne yake fitar mata da sirri haka?,anya ba daadar himu bace?,babu shiri ta kwashi takalmanta a hannu ta fice don anni ta fara daga mata murya.

Abinda ya sake kada mata hanji kuma shine kallon banzan da daadar himu ta watsa mata sanda sukayi kacibus a tsakar gidan,saita qarasa daburcewa,ko taji abinda yake tafe da ita ne?,don haka ta hadiye gaisuwarta tayi waje,don ta soma zargin daadar cikin ranta,saboda tasan kaf fadin karkarar ita kadai tasan da wannan maganganun.

Tunda ta idar da sallar asuba tana zaune bata koma ba,lokaci lokaci idanunta suna kan gaje daketa sharbar bacci abinta,babu shiri ko niyyar tashi tare da ita bare ta sauke farali,har yanzu halindai ashe yana nan ta raya hakan cikin ranta.

Haka kawai tayi sha'awar tashi tayi irin ayyukan data saba yi a baya,don haka ta miqe a hankali,ta zura hannunta inda ta cusa takalmanta watannin baya sanda zata bar gidan,cikin sa'a ta samesu,murmushi ta sake,duk da sun ratattake,suna tuna mata da abubuwa masu yawan gaske da suka gabata,saita miqe dogayen qafafunta da a yanzun suka qara haske suka kuma yi luwai luwai ta zura su,sannan tayo waje.

Tana fitowa jauro na dawowa daga salla,ta gaidashi cikin girmamawa ya amsa mata cikin kulawa yana tsokanarta kan yau ta tuna kwanan ruga,tana murmushi ta soma aikin gidan,sai gashi ya fito yana tambayarta inda fureran taje

"Ban sani ba kawu,yanzu nima na futo" sai ya jinjina kai,har yayi gaba ya dawo yace mata ta aje aikin ta koma ta kwanta

"Ba komai kawu,hakan yana min dadi" kansa ya jinjina cikin tausayi da qaunar yarinyar,ya shige dakinsa,babu jimawa ya fito da koren hirami na maza jikinsa daya yafa,ya wuce dakinsu,tana jinsa yana rafkar gaje kan ta tashi tayi sallah,kana yayo waje yana ce mata zaije ya dawo,tayi masa a dawo lafiya tana ci gaba da ayyukanta,saidai har ta gams gaje bata futo ba.

Ganin ta gama saita wuce kanta tsaye zuwa haggo,tun daga nesa take kallon dabbobin cikin kewa da shauqi,tayi matuqar kewarsu ba kadan ba,amma abinda yadan taba ranta ya kuma bata mamaki,yadda yawansu kyau da tsaftarsu suka ragu sosai,taga sabbin fuskoki dake nuna an hayayyafa,to amma indai hakane me ya hana su qara yawa?.

A nutse taje ta kwance wadanda suke daure,ta zari sandar data gani a jingine a wajen,ta kuma soma korasu cikin nutsuwa da tsohuwar qwarewa zuwa makiyaya.

Kusan za'a iya cewa kallo ne ya koma sama,duk inda ta wuce dai ta kwashi fiye da rabin hankalin mutanen wajen,wasu da yawa basu ganeta ba,suna mata kallon baquwar fuska,don atamfa ce a jikinta dinkin doguwar riga,ba kayan saqi ba.

Dukka wajen data saba ta'ammali dashi a wancan lokacin sai data tsaya a wajen tana tuna komai daya wuce,daga qarshe ta dangana da qasan bishiyarta,wadda a yanzun ta qara yawa da rassa,tana shirin zama taji sallama da muryar da ta kasance sananniya a wajenta.

A nutse ta daga kai tana amsa sallamar,bafullatanin saurayin nan daya taimaki rayuwarta a shekarun baya,himu,shine yau tsaye a gabanta bayan shudewar wasu watannu masu tsaho,yana nan a yadda ta sanshi,saidai kuma yayi rama ba kamar a baya ba da yake da cikar jiki.....Ya tsinke sosai ya qara tsaho,har yanzu wannan murmushin nasa yana nan saman fuskarsa,sai ya tako daura da inda take zaune,ya zauna saman dutsen daya saba zama shima

"Maimunatu....'yammatan birni" maganar data sanya siririn murmushi kubuce mata,ta kuma soma gaidashi,ya amsa mata cikin matuqar kulawa

"Tafiya haka katsam babu bankwana maimunatu?,saidai na laluba naji wayam babu ke?" Har yanzu himu nada wata kima da daraja a ranta,yana kuma cikin jerin mutane masu muhimmanci a rayuwarta

"Kayi haquri,haka tafiyar nima tazomin,kuma a sannan bansan inda zan ganka ba" kai ya gyada,shima yasan da wannan

"Hakane,to yaya bayan rabuwa?,duk da alamu sun nuna komai yana tafiyar miki yadda ya kamata" ya fada kansa tsaye yana hango canji qarara daga wajenta,canjin da yasa ya saare,ya sake kuma sallamawa bayan kunnuwansa sunji ana zancan aurenta da wani.

Mintuna kadan ya miqe bayan zaman shuru da sukayi shi da ita

"Sallama nazo muyi,saboda nasan ba lallai bane na sake samun dama irin wannan,ban taba kawowa a raina zan rasaki ba,sai gashi qaddara ta wanzar mana da hakan,duk da zuciyata ta soki matuqar so,bazanyi jayayya ba,saboda bansan me Allah ke nufi da hakan ba,kin cancanci samun kyakkyawar rayuwa fiye da wadda nake miki tanadi,ina miki fatan alkhairi a dukka rayuwarki maimunatu" daga haka ya juya ya soma barin wajen.

"Na gode sosai" abinda ta iya gaya masa kenan tana bin bayansa da kallo,tausayinsa da kuma wani irin yanayi na cika mata zuciya,har ya bacewa ganinta.

Ko awa guda bata rufa ba inna furera ta aiko kan ta tattaro mata dabbobinta ta dawo mata dasu,tayi hakanne saboda tsoron daya cika zuciyarta kan kada ta rasa dabbobin data qwallafa rai a kansu,fitar da maimunatun tayi dasu sai take ganin kamar wani shiri ne.
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 25

Kamar jabir din ya shareshi,sai kuma ya kasa,ko babu komai yana buqatar kwantar da hankalinsa kada kuma ya birkice musu a koma 'yar gidan jiya,bayan abubuwan suna danyi kyau ba kamar can baya ba,don haka sai ya kwasa shima ya bishi.

Cikin rashin sa'a ya sameshi ya kulle kansa a dakinsa,yayi ta bugu ya bude masa amma yayi kunnen uwar shegu dashi,ya sani ya qulu sosai,kuma cikin bacin rai yake,haka dole ya haqura,saidai yana fatan kada ya jima a kulle a dakin temper tayi masa yawa.

Komawa yayi ya zauna saman kujerun falon,kam kujerar dake fuskantar dakin,lokaci lokaci yana danna wayarsa yana kuma duban qofar dakin tare da fatan ya bude,saidai har kusan awa guda da rabi ba motsinsa ko alamar budewa,abun da yadan saka jabir yaji shakka a ransa,sai ya sauka daga game din da yakeyi don dama ta fara isarsa,ya kirayi layin anni.

Gaisawa suka fara yi sannan ya gaya mata abinda yake faruwa,duk da taji fargaba itama cikin ranta amma saita dake

"Rabu dashi,zaiyi ne ma ya gama,kayi sabgarka,idan ya gaji ya fito" ta fada cikin dakiya,murmushi jabir yayi,don shi kansa yasan dakiya kawai annin tayi.

Suna gama wayar ya isa ga makunnin kayan kallonsu ya kunna tv din,sannan ya maida channel din dake kai zuwa saudi qur'an da madaidaicin sauti,ya ajjiye remote ya wuce dakinsa ya sauya kayan jikinsa daga shi sai farar singlet da boxer,ya fidda siyayyar da yayo,yakai daki sa,saura kuma ya wuce kitchen dasu.

Abinci ya fara shirya musu,yana aikin amma hankalinsa yana falo,yana yi yana leqawa ki ja'afar din ya fito,saidai har ya gaji da leqan baiga ya fito ba,tilas ya haqura har ya gama abincin.

Yana fitowa daga kitchen din yana qoqarin fidda afron din jikinsa jaafar din na fitowa a dakin,sosai jabir din yaji dadin hakan,ganin fushin baiyi tsaho ba,a yanzun ma ya sake wanka ne don kayan jikinsa na dazun ba sune yanzu ba.

"Ina zuwa?" Jabir ya tambayeshi yana fidda ruwa daga fridge

"Zamu fita da mr mickey,akwai meeting da zamuyi,so if i stay long kada ka jirani"

"Abincin fa?"

"Ka cinye kayanka" dariya ce ta qwacewa jabir,ya sani fushi yake dashi,yaji haushin that's right da ya fada,da kuma goyon bayan anni da yayi,fushinsa ne ya shafi abincinsa

"Cikinka ba nawa ba" ya bashi amsa sanda yake takawa zai fita daga falon,saidai bai waiwayo ba ya fice abinsa,kamar ma baiji abinda jabir din ya fada ba.

Diban iya wanda zai isheshi yayi ya sanya masa sauran a fridge,yasan idan ya dawo zai nema abincin da kansa,don duk abin nan nasa baya wasa da cikinsa ko kadan.
Chapter 35 · 0% Book details