Sashe 29
Gurbin Ido Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Karo na kusan biyar idanunta suka sake kaiwa kan maimunatu dake wasa da hannayen amna
"Anni a ina aka samo mana bafulatana haka?" Waiwaya tayi ta dubi maimunatu sannan ta dawo da dubanta ga munubiya
"Surukarku ce"
"Matar wa kenan?" Dan qaramin murmushi annin ta sake
"Ina fatima.....ke fadima" ta qwalawa daya daga cikin 'yammatan gidan kira ,dubanta tayi sanda ta qaraso
"Dauketa ki kaita dakinku,daga nan ki duban idan hafsatun ta farka"
"To anni" ta amsa da girmamawa,da alamu dukka cikin yaran ta fisu nutsuwa da hankali,waiwayawa tayi fuskarta dauke da murmushi ta cewa maimunatu ta taso.
Tana gaba tana biye da ita,har zuwa sanda suka isa isa qofar wani daki,ta tura ta saka kai da sallama a bakinta maimunatun na biye da ita.
Wata matashiya ce zaune saman gadon,ta jingina bayanta da fuskar gadon,sanye da wata doguwar riga cotton me yankakken hannu,kanta hula ce baqa da ta dan jata baya kadan,fuskarta babu alamun annuri,da alama itace mara lafiyan da annin taxo dubawa.
"Ya hafsa,anni tazo dubaki,tace na duba naga idan kin tashi" fuska ta yatsine,murya kuma can qasa tace
"Banga amfanin zuwa duba nin data yi ba,tunda ba zata iya maganta min komai ba" maganganun da maimunatu ta jisu wasu iri a kunnuwanta,har sai daa dan saci kallonta,wadda take qoqarin sake shigewa cikin bargo ta kuma kwanciya abinta
"Ayyah yaa hafsa,wai me yasa kike irin wadan nan maganganun ne?"
"Kinfi kowa sanin dalilin,ja'afar ne,ja'afar shine dalili" dubanta fatima tayi,sannan ta matso gefanta kadan ta zauna
"Me yasa ba zaki haqura da yaa ja'afar ba yaa hafsa?" Idanu ta zubawa fatiman,tana kuma qanqanceshi,tsahon wasu sakanni sannan ta amsa mata da
"Ashe baki da hankali fatima,hala bakisan meye ainihin haqiqanin ma'anar so ba ko?,ta yaya zan bar ja'afar?,kinsan yadda nake sonshi kuwa?,wait.....waye ma ya gaya miki ja'afar irin mutanen da ake iya haqura da soyayyarsu ne?" Kai fatima ta rausayar
"Amma dai yaa hafsa,bake kadai cikin family kike da irin wannan qudurin ba,kuna da yawa,ke surayya hannah da walida,ga madina dama sauran wadanda basu bayyana ba,kunfi kowa sanin waye yaa ja'afar tun sanda yake lafiyarshi lau ma bare yanxu da kura tayi hauka,ke kinsan wayeshi,duk cikinku bana jin akwai wadda zata iya dashi idan aka barku,wannan dakatarwar da anni tayi muku ma kamar taimakonku tayi,ta kuma tsare muku mutunci da martabarku"
"Ta barmu din yafimin,yafimin wannan kisan mummuqen......"
"Don Allah ina bandaki?" Maimunatu ta katse musayar maganganun da suke a tsakaninsu,sai a sannan fatima ta waiwayo
"Yi haquri don Allah,na barki a tsaye,gashi can" ta fada tana mata nuni da wata qofa dake kulle,takawa tayi a hankali ta nufi bandakin,saidai zuciyarta cike fal da mamakin maganganun hafsah,har yanzu dama akwai irin wannan soyayyar?,waye ne shi wanda takewa irin wannan soyayyar?,wannan tunanin ya tuna mata da himunta da kuma buderi,ko a wanne yanayi kowannensu yake ciki?,ta tabbatar himu yana can yana dakonta,yana kuma nege da shauqin ganinta,wanda kusan ita dinma tana jin hakan a ranta a kansa.
Fitsari tayi sannan ta daura alwala,ta fito daga bandakin tana gyara rolling din mayafinta
"Ba zaki gane ba fatima....na jima inason yaa ja'afar,ba zaki gane me nakeji ba a kansa" kalaman hafsa da suka sake shiga kunnuwanta kenan,ta dan kauda kanta tana jin kunya da mamakin yadda budurwar keta haqilo akan namiji,ta tayar da sallah abinta.
Kafin ta idar sun gama maganar,wanda fatima ce ta sakar mata ganin ba zata fahimci abinda takeson nuna mata ba,a nan suka zauna suna taba hira ita da fatima,wanda dukka kusan akan islamiyya ce,da alama itama mayyar islamiyyar ce kamar yadda maimunatu take,kusan bata taba ganin fatima a gidansu ba,saboda yawanci tana islamiyya,ko a makarantar boko bangaren islamic take,abinda ya bawa maimunatu sha'awa sosai,har taji itama islamic take sha'awar yi inda zata samu dama,saidai ba zata iya buda baki ta yiwa anni ko dr maganar ba.
Daya daga cikin yaran gidan ne ya leqo bayan sallar magariba,yace maimunatun tazo inji anni taci abinci zasu wuce gida,da hanzarinta ta tashi,abinda yasa fatima zolayarta
"Dama kin gaji da gidan namu,da alama so kike dama a tafi" murmushi maimunatun ta sakar mata ba tare da tace komai ba
"Allah yasa ki iya zuwa mana ma da bikin anty amira ki kwana"
"Allah ya kaimu" ta amsa mata tana murmushi,sai fatiman ta taka mata zuwa falon da annin ke zaune.
Tun kafin ta qaraso muryar mai kauri da zurfi take ratso inda suke,matashi ne mai cikar haiba da kamala zaune sosai gaban annin suna magan,da alama akwai sabo sosai a tsakaninsu,farin bafullatani sak,wanda yake diban kama ta sosai da haj munira.
"Dole cikin satin nan kije,ko fatima saita rakaki,tunda kina jin dadin maganin bai kamata a fara fashi ba,zan kirashi na gaya masa sati daya zakuyi" ya qarashe maganar yana daga kansa,dai dai sanda idanuwansa suka sauka kan fuskar maimunatu dake takowa a hankali jere da fatima.
Tamkar haduwar mayen qarfe da maganadisu haka yaji wani abu mai qarfi ya fusgeshi,duk yadda yaso ya dauke idanunsa daga kanta hakan ya gagara,harta qaraso ta soma gaidashi a darare tana lafewa daga gefan anni.
Da mamaki fatima ke satar kallon yaa khalid din,shi da baya yiwa mace kallo uku amma yau gashi ya kafe idanunsa akan maimunatu?,sai daya fuskanci fatiman na kallonsa sannan yajanye idanun nasa ya kuma bata rai yana komawa ga batunsu shida annin,saidai lokaci lokaci yana satar kallon ta.
Iya tafiya ta tafi dashi,duk da bata qarasa kalar macen da yakeson aure ba,amma fa hada komai da komai,special care kawai zata samu ta wasu bangarori ta yiwa mata fintikau.
"Nidai bansan me kakeson maidani ba khalid,wannan jewar fa ta isheni,nidai a barni,ciwo ai ba mutuwa ba,idan lokaci kuma yayi dole na tafi" anni tayi statement din qarshe tana miqewa tsaye da zummar tafiya,bayan maimunatu taqi cin abincin da aka kawo mata,sam ba zata iya ba,tana jinta ne duk a daure saboda kallon data fuskanci saurayin yana ritsata dashi,wai shin kam haka samarin family dinsu suke ko kuwa su din su biyun daga garesu ne?.
Shi ya musu tattaki har zuwa bakin motar da sunan yiwa anni rakiya,fiye da rabin hankalinsa yana kan maimunatun,duk da yana yine yana basarwa har motarsu ta daga.
Yayi tunanin da sun yafi shikenan,saidai kuma kasa nutsuwa zuciyarsa tayi,har sai da yakai kansa gida dr marwan,ya kuma sakeyin ido biyu da.maimunatu,tun daga sannan abun ya zame masa kamar wani jarrabi,duk bayan kwana biyu daga office yake zartowa nan din,baya barin gidan sai bayan sallar isha'i.
*********Karfe shida suka dawo daga islamiyya,tana sanye da babban hijabinta da ya saukar mata har qasan qafafunta,kalar blue black,abinda yasa yayi matuqar haskata tare da yi mata kyau,tana rungume da qur'aninta a qirji,laila na gefanta tana amsa waya.
Suna sallama a falon sukayi idanu biyu dashi,qirjinta yayi mugun faduwa,taja da baya kamar zata koma sai kuma ta kasa,ganin ya ganta sarai,cikin zuciyarta bata son haduwarta dashi,saboda kallon da yake tsareta dashi da kuma sanyata cikin lamuransa da yawa,har fiye dasu laila da suke jininsa.
A hankali ta biyo bayan laila kamar me tsoron wani abu zai iya kamata,tana jin laila na masa sannu da zuwa sai itama tabi sahunta,ta kuma sulale da niyyar wucewa dakinta,saidai ya tsayar da ita da tambayoyi kan karatunta,abinda ya bawa laila damar wucewa ta barsu su daya a wajen.
Sallamar hisham daga bakin qofa ya ja hankalinsu duka,suka hada idanu da dukka su biyun,take fara'ar dake saman fuskarsa ta bace bat,ya fara shigowa falon cikin rashin walwala yana faman shan qamshi.
Kowa a cikinsu cikakken matashi ne mai jin kansa,wanda ya hada komai da komai,musabaha sukayi da juna kowa yana dauke wuta,ba kamar yadda suka saba ba,har zuwa sannan kan maimunatu yana qasa,ta yiwa hisham sannu da zuwa,maimakon ya amsa,sai ya koma da baya ya zauna cikin daya daga cikin kujerun falon yana cewa
"Je kitchen ki kawomin ruwa" a hankali ta tashi tana jin wani nauyi na raguwa daga cikin zuciyarta,zamanta a wajen tana jinta ne kamar cikin wani matsatstsen keji ne da babu sakewa.
Shuru ne ya biyo baya a falon,hisham na danne danne a wayarsa,khalid kuma yana kallon news,kowanne da tunanin da yake a ransa game da dan uwansa,ba tun yau ba duka sun tsargu da juna,sun kuma fahimci mawuyaci ne idan basiu tarayya akan wani abu guda ba.
Ruwan ta kawo masa hade da cup,ya dauki gorar ruwan yana cewa
"Ba daga islamiyya kike ba?" Kai ta gyada masa
"Bita ce ta kamaceki ba ki zauna kina surutun banza ba...wuce daki ki ajjiye qur'anin hannunki" cikin jin kai da isa khalid ya gyara zamansa sosai yana kuma dubansa kai tsaye
"Dakata mana hisham?,wanne irin nonsense ne zaka same mu tare sannan kace ta wuce ciki?.... please kada ka shiga hurumin da ba naka ba" wani kallo hisham ya watsawa khalid sannan ya saki murmushi
"Nonsense?......hmmmm,dani da kai za'a samu wanda ya dace a gayawa hakan,wuce maimunatu tun raina bai fara baci ba"
"Ba zata wuce ba!" Khalid ya fada a tsawace,dai dai sanda anni ke qarasowa falon,ta bisu da kallo cikin mamakin yanayin data taras dasu.
_To fa masu karatu,khalid dinne ko hisham?,ko kuma ja'afar?,waye zaiyi wining?,muje zuwa yanzu aka fara wasan_
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 21
"Kai.....kai,meye hakan?" Anni ta dakatar dasu cikin tsawa,ganin zasu fara sa'insa a tsakaninsu
"Ya zaizo ya samemu zaune,sannan kawai yace sai ta tashi ta shiga daki anni?,wannan wanne irin raini ne?" Khalid ya fada cikin jin ciwon abinda hisham yayi masa,yana jin ya disgashi abinda ba'a taba yi masa ba
"Anni,dawowarta kenan daga makaranta,da alama ko ke bakisan ta dawo ba,don nace ta shiga ta ajjiye qur'aninta sai ya zama laifi?" Shuru ne ya biyo baya,anni tana nazartar kowannensu cikin sakannin da basu wuce biyar ba,sai taji hankalinta ya dan tashi,zata iya cewa bata taba ganin irin wannan sabanin ba a tsakanin jikokinta,wannan shine karon farko da hakan fa faru,duk da tasan dama tsakanin khalid da hisham ba jituwa bace can can,amma kuma basa cecekuce,tabbas ya kamata ta yuwa tufkar hanci da wurwuri
"Anni a ina aka samo mana bafulatana haka?" Waiwaya tayi ta dubi maimunatu sannan ta dawo da dubanta ga munubiya
"Surukarku ce"
"Matar wa kenan?" Dan qaramin murmushi annin ta sake
"Ina fatima.....ke fadima" ta qwalawa daya daga cikin 'yammatan gidan kira ,dubanta tayi sanda ta qaraso
"Dauketa ki kaita dakinku,daga nan ki duban idan hafsatun ta farka"
"To anni" ta amsa da girmamawa,da alamu dukka cikin yaran ta fisu nutsuwa da hankali,waiwayawa tayi fuskarta dauke da murmushi ta cewa maimunatu ta taso.
Tana gaba tana biye da ita,har zuwa sanda suka isa isa qofar wani daki,ta tura ta saka kai da sallama a bakinta maimunatun na biye da ita.
Wata matashiya ce zaune saman gadon,ta jingina bayanta da fuskar gadon,sanye da wata doguwar riga cotton me yankakken hannu,kanta hula ce baqa da ta dan jata baya kadan,fuskarta babu alamun annuri,da alama itace mara lafiyan da annin taxo dubawa.
"Ya hafsa,anni tazo dubaki,tace na duba naga idan kin tashi" fuska ta yatsine,murya kuma can qasa tace
"Banga amfanin zuwa duba nin data yi ba,tunda ba zata iya maganta min komai ba" maganganun da maimunatu ta jisu wasu iri a kunnuwanta,har sai daa dan saci kallonta,wadda take qoqarin sake shigewa cikin bargo ta kuma kwanciya abinta
"Ayyah yaa hafsa,wai me yasa kike irin wadan nan maganganun ne?"
"Kinfi kowa sanin dalilin,ja'afar ne,ja'afar shine dalili" dubanta fatima tayi,sannan ta matso gefanta kadan ta zauna
"Me yasa ba zaki haqura da yaa ja'afar ba yaa hafsa?" Idanu ta zubawa fatiman,tana kuma qanqanceshi,tsahon wasu sakanni sannan ta amsa mata da
"Ashe baki da hankali fatima,hala bakisan meye ainihin haqiqanin ma'anar so ba ko?,ta yaya zan bar ja'afar?,kinsan yadda nake sonshi kuwa?,wait.....waye ma ya gaya miki ja'afar irin mutanen da ake iya haqura da soyayyarsu ne?" Kai fatima ta rausayar
"Amma dai yaa hafsa,bake kadai cikin family kike da irin wannan qudurin ba,kuna da yawa,ke surayya hannah da walida,ga madina dama sauran wadanda basu bayyana ba,kunfi kowa sanin waye yaa ja'afar tun sanda yake lafiyarshi lau ma bare yanxu da kura tayi hauka,ke kinsan wayeshi,duk cikinku bana jin akwai wadda zata iya dashi idan aka barku,wannan dakatarwar da anni tayi muku ma kamar taimakonku tayi,ta kuma tsare muku mutunci da martabarku"
"Ta barmu din yafimin,yafimin wannan kisan mummuqen......"
"Don Allah ina bandaki?" Maimunatu ta katse musayar maganganun da suke a tsakaninsu,sai a sannan fatima ta waiwayo
"Yi haquri don Allah,na barki a tsaye,gashi can" ta fada tana mata nuni da wata qofa dake kulle,takawa tayi a hankali ta nufi bandakin,saidai zuciyarta cike fal da mamakin maganganun hafsah,har yanzu dama akwai irin wannan soyayyar?,waye ne shi wanda takewa irin wannan soyayyar?,wannan tunanin ya tuna mata da himunta da kuma buderi,ko a wanne yanayi kowannensu yake ciki?,ta tabbatar himu yana can yana dakonta,yana kuma nege da shauqin ganinta,wanda kusan ita dinma tana jin hakan a ranta a kansa.
Fitsari tayi sannan ta daura alwala,ta fito daga bandakin tana gyara rolling din mayafinta
"Ba zaki gane ba fatima....na jima inason yaa ja'afar,ba zaki gane me nakeji ba a kansa" kalaman hafsa da suka sake shiga kunnuwanta kenan,ta dan kauda kanta tana jin kunya da mamakin yadda budurwar keta haqilo akan namiji,ta tayar da sallah abinta.
Kafin ta idar sun gama maganar,wanda fatima ce ta sakar mata ganin ba zata fahimci abinda takeson nuna mata ba,a nan suka zauna suna taba hira ita da fatima,wanda dukka kusan akan islamiyya ce,da alama itama mayyar islamiyyar ce kamar yadda maimunatu take,kusan bata taba ganin fatima a gidansu ba,saboda yawanci tana islamiyya,ko a makarantar boko bangaren islamic take,abinda ya bawa maimunatu sha'awa sosai,har taji itama islamic take sha'awar yi inda zata samu dama,saidai ba zata iya buda baki ta yiwa anni ko dr maganar ba.
Daya daga cikin yaran gidan ne ya leqo bayan sallar magariba,yace maimunatun tazo inji anni taci abinci zasu wuce gida,da hanzarinta ta tashi,abinda yasa fatima zolayarta
"Dama kin gaji da gidan namu,da alama so kike dama a tafi" murmushi maimunatun ta sakar mata ba tare da tace komai ba
"Allah yasa ki iya zuwa mana ma da bikin anty amira ki kwana"
"Allah ya kaimu" ta amsa mata tana murmushi,sai fatiman ta taka mata zuwa falon da annin ke zaune.
Tun kafin ta qaraso muryar mai kauri da zurfi take ratso inda suke,matashi ne mai cikar haiba da kamala zaune sosai gaban annin suna magan,da alama akwai sabo sosai a tsakaninsu,farin bafullatani sak,wanda yake diban kama ta sosai da haj munira.
"Dole cikin satin nan kije,ko fatima saita rakaki,tunda kina jin dadin maganin bai kamata a fara fashi ba,zan kirashi na gaya masa sati daya zakuyi" ya qarashe maganar yana daga kansa,dai dai sanda idanuwansa suka sauka kan fuskar maimunatu dake takowa a hankali jere da fatima.
Tamkar haduwar mayen qarfe da maganadisu haka yaji wani abu mai qarfi ya fusgeshi,duk yadda yaso ya dauke idanunsa daga kanta hakan ya gagara,harta qaraso ta soma gaidashi a darare tana lafewa daga gefan anni.
Da mamaki fatima ke satar kallon yaa khalid din,shi da baya yiwa mace kallo uku amma yau gashi ya kafe idanunsa akan maimunatu?,sai daya fuskanci fatiman na kallonsa sannan yajanye idanun nasa ya kuma bata rai yana komawa ga batunsu shida annin,saidai lokaci lokaci yana satar kallon ta.
Iya tafiya ta tafi dashi,duk da bata qarasa kalar macen da yakeson aure ba,amma fa hada komai da komai,special care kawai zata samu ta wasu bangarori ta yiwa mata fintikau.
"Nidai bansan me kakeson maidani ba khalid,wannan jewar fa ta isheni,nidai a barni,ciwo ai ba mutuwa ba,idan lokaci kuma yayi dole na tafi" anni tayi statement din qarshe tana miqewa tsaye da zummar tafiya,bayan maimunatu taqi cin abincin da aka kawo mata,sam ba zata iya ba,tana jinta ne duk a daure saboda kallon data fuskanci saurayin yana ritsata dashi,wai shin kam haka samarin family dinsu suke ko kuwa su din su biyun daga garesu ne?.
Shi ya musu tattaki har zuwa bakin motar da sunan yiwa anni rakiya,fiye da rabin hankalinsa yana kan maimunatun,duk da yana yine yana basarwa har motarsu ta daga.
Yayi tunanin da sun yafi shikenan,saidai kuma kasa nutsuwa zuciyarsa tayi,har sai da yakai kansa gida dr marwan,ya kuma sakeyin ido biyu da.maimunatu,tun daga sannan abun ya zame masa kamar wani jarrabi,duk bayan kwana biyu daga office yake zartowa nan din,baya barin gidan sai bayan sallar isha'i.
*********Karfe shida suka dawo daga islamiyya,tana sanye da babban hijabinta da ya saukar mata har qasan qafafunta,kalar blue black,abinda yasa yayi matuqar haskata tare da yi mata kyau,tana rungume da qur'aninta a qirji,laila na gefanta tana amsa waya.
Suna sallama a falon sukayi idanu biyu dashi,qirjinta yayi mugun faduwa,taja da baya kamar zata koma sai kuma ta kasa,ganin ya ganta sarai,cikin zuciyarta bata son haduwarta dashi,saboda kallon da yake tsareta dashi da kuma sanyata cikin lamuransa da yawa,har fiye dasu laila da suke jininsa.
A hankali ta biyo bayan laila kamar me tsoron wani abu zai iya kamata,tana jin laila na masa sannu da zuwa sai itama tabi sahunta,ta kuma sulale da niyyar wucewa dakinta,saidai ya tsayar da ita da tambayoyi kan karatunta,abinda ya bawa laila damar wucewa ta barsu su daya a wajen.
Sallamar hisham daga bakin qofa ya ja hankalinsu duka,suka hada idanu da dukka su biyun,take fara'ar dake saman fuskarsa ta bace bat,ya fara shigowa falon cikin rashin walwala yana faman shan qamshi.
Kowa a cikinsu cikakken matashi ne mai jin kansa,wanda ya hada komai da komai,musabaha sukayi da juna kowa yana dauke wuta,ba kamar yadda suka saba ba,har zuwa sannan kan maimunatu yana qasa,ta yiwa hisham sannu da zuwa,maimakon ya amsa,sai ya koma da baya ya zauna cikin daya daga cikin kujerun falon yana cewa
"Je kitchen ki kawomin ruwa" a hankali ta tashi tana jin wani nauyi na raguwa daga cikin zuciyarta,zamanta a wajen tana jinta ne kamar cikin wani matsatstsen keji ne da babu sakewa.
Shuru ne ya biyo baya a falon,hisham na danne danne a wayarsa,khalid kuma yana kallon news,kowanne da tunanin da yake a ransa game da dan uwansa,ba tun yau ba duka sun tsargu da juna,sun kuma fahimci mawuyaci ne idan basiu tarayya akan wani abu guda ba.
Ruwan ta kawo masa hade da cup,ya dauki gorar ruwan yana cewa
"Ba daga islamiyya kike ba?" Kai ta gyada masa
"Bita ce ta kamaceki ba ki zauna kina surutun banza ba...wuce daki ki ajjiye qur'anin hannunki" cikin jin kai da isa khalid ya gyara zamansa sosai yana kuma dubansa kai tsaye
"Dakata mana hisham?,wanne irin nonsense ne zaka same mu tare sannan kace ta wuce ciki?.... please kada ka shiga hurumin da ba naka ba" wani kallo hisham ya watsawa khalid sannan ya saki murmushi
"Nonsense?......hmmmm,dani da kai za'a samu wanda ya dace a gayawa hakan,wuce maimunatu tun raina bai fara baci ba"
"Ba zata wuce ba!" Khalid ya fada a tsawace,dai dai sanda anni ke qarasowa falon,ta bisu da kallo cikin mamakin yanayin data taras dasu.
_To fa masu karatu,khalid dinne ko hisham?,ko kuma ja'afar?,waye zaiyi wining?,muje zuwa yanzu aka fara wasan_
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 21
"Kai.....kai,meye hakan?" Anni ta dakatar dasu cikin tsawa,ganin zasu fara sa'insa a tsakaninsu
"Ya zaizo ya samemu zaune,sannan kawai yace sai ta tashi ta shiga daki anni?,wannan wanne irin raini ne?" Khalid ya fada cikin jin ciwon abinda hisham yayi masa,yana jin ya disgashi abinda ba'a taba yi masa ba
"Anni,dawowarta kenan daga makaranta,da alama ko ke bakisan ta dawo ba,don nace ta shiga ta ajjiye qur'aninta sai ya zama laifi?" Shuru ne ya biyo baya,anni tana nazartar kowannensu cikin sakannin da basu wuce biyar ba,sai taji hankalinta ya dan tashi,zata iya cewa bata taba ganin irin wannan sabanin ba a tsakanin jikokinta,wannan shine karon farko da hakan fa faru,duk da tasan dama tsakanin khalid da hisham ba jituwa bace can can,amma kuma basa cecekuce,tabbas ya kamata ta yuwa tufkar hanci da wurwuri