Sashe 14
Gurbin Ido Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Gaskiya dai..." Salihu ya fada shima yana murmushi cikin mamakin halayyar maimunatun,saboda yasan halim mutane da dama kan cinikayya irin wannan,kowa kazo kana son siyan abunsa qoqari yake ya linke aibun abun ya baka shi ta fuskar da zaka gamsu da ingancinsa.
Maganar ta sanya inna furera dauke idanunta daga hararar da take danqarawa maimunatu zuwa kan anni,bayan ta wadatar fuskarta da murmushin yaqe
"Haka ai take,kuma har 'yar uwarta da muka baro a can ta fita" ta fadi tanason fidda gajenta kunya gaban surukarta da kuma baqin idanun da suke wajen
"To ma sha Allah,Allah ya dorar dasu akan hakan"
"Uhmmm...meen ameen"inna furera ta fada tana son nuna jin dadinta.
Yadda inna furera ta fada haka anni tasa salihu ya irga kudinta cas aka tafe mata,harda qaramar rawarta saboda farincikin ganin irin kudin data karba sama ta ka,lallai a duniya bata da masoyi kamar daadar himu,wadda ita tayi mata silar wannan ciniki mai gwaggwabar riba.
Har sun juya zasu wuce anni ta waiwayo tana duban maimunatu
"Jikata kema ai ya kamata ace an baki wani abu ko,saboda qoqarin nuna mana zabin qwarai da kikayi" qaramin murmushi mai cike da kunya da kuma kawaici ta sake,tayi qas da kanta ba tare da tace komai ba,kamar ma kuma taga hararar da inna furera ta fara auna mata
"Basai kin ban komai ba kaaka,haqqina ne nayi hakan don fita haqqin Allah a kaina" tabbas badon idanun da suke wajen ba ba abinda zai hana inna furera kai mata mangari,qiri qiri yarinyar nason jaza musu asara?,don batasan yawan kyautar da matar tayi nufin yi mata ba
"Gaskiya ne" anni ta fada,saita karba jakarta a hannun laila wadda duk wannan abun da ake hankalinta nakan daukar hotuna cikin wayarta kusa da dabbobin,don ta samun abun adanawa ya zame mata tarihi,kuma ta bada labarin xuwanta rugar,don kuwa da wayonta ba zata iya tuna yaushe tazo rugar na qarshe ba.
Sabbin kudi ta fitar ta irgasu a miqe ta miqa maimunatu
"Naji dadin riqe gaskiyarki,wannan kyauta ce bisa hakan" dan noqewa kadan tayi kamar ba zata karba ba,har sai da salihu ya sanya baki,sai data saci kallon inna furera taga yadda take watsa mata harara sannan tasa hannu biyu ta karba tana fadin
"Allah ya saka da alkhairi,ya maida ninkinsu"
"Ameennn" anni ta fada cikin jin dadin addu'ar maimunatun.
Bata tsammanin ko sassan nasu su anni sun bari inna furera ta miqa mata hannu,ko batayi.magana ba tasan me take nufi,shi yasa gaba daya batayi nufin amsar kudin ba,saboda tasan cewa zata raba matar da kudinta ne,ita kuma da tayi niyyar bawa ba zata mori komai a cikinsu ba,duka ta dunqule kudin hannun nata ta miqawa inna fureran,sannan ta tsugunna ta debi kayan aikinta ta fara gyara wajen bata ko waiwayeta ba.
Babu kunya babu kuma tsoron Allah ko daya a tattare da ita ta hade dukka kudaden ta irge abunta cas ta soke su tayi gaba abinta tana rera waqa,yau itakam ranta fes,mutuwa batayi mata komai ba sai rana data yi mata,banda silar mutuwar ina ita wannan dukiyar?,ina ita ina mallakar wadan nan kudade?,kudi kam sunzo mata a dai dai,tanadin bikin gajenta zata farayi tun yanzu,saboda bikin gata takeso tayi mata.
>>>>>>>>>>"sannu anni.....an gama komai ko?" Yuuma ta fada sanda take shigowa rumfarta dauke da kwanon sha da ta cikashi da damammiyar fura da nono wadda babu surkin sugar ko kadan a cikinsa
"Mun gama komai ramatu..dabbobi lafiyayyu,har sunso sufi na labaran din ma"
"Ai sunfi ma anni,sun hadu da makiyayiya mai hazaqa da iya kiwo,irin kiwon da babu ha'inci a ciki" yuuma ta fadi tana zama sosai gaban anni tana murmushi
"Ai naga alama,ko ba wata yarinya maimunatu ba?"
"Itafa,baiwar Allah" yuuma ta fada fuskarta na dan canza yanayi
"Ai tunda na shigo Allah yake hadamu,naketa ganin abubuwan mamaki daga wajen yarinyar,na jima banga me kiwo irinta ba,sannan abinda zai sake baki mamaki da ita.....wajen cinikin nan,kowacce dabba da muka nuna manaso sai datayi mana bayanin lafiyarta da sauransu,babu ha'inci" cikin gamsuwa yuuma take gyada kai
"Bata tsinta a qasa ba ai,gado ne me kyau daga wajen mahaifiyarta,Allah ya jiqan ruma"
"Allah sarki,kice marainiya ce?" Anni ta fada tana jan kwanon furar gabanta tana qoqarin budewa
"Marainiya ce,wadda aka kasa yi mata riqo na tsakani da Allah.....kinsan mahaifiyarta anni,kin tuna matar da kikaga wata balama me juna biyu a wajenta kikai sha'awarta shekarun baya can da suka shude,ta qara miki da kyautar wata akuya,akuyar da kikace ta miki albarka fiye da kowacce dabba a kiwonki?"
"Af.....af ina zan manta da wannan baiwar Allar,dama itace mahaifiyarta?"
"Itace anni" yuuma ta amsa mata tana dauko wani kwanon da ta shaqewa anni shi da dambu me dumi tana aje mata
"Allahu akhbar......." Maganar annin ta tsaya sakamakon shigowar laila tana qananun mita.
Daga kai anni tayi ta dubeta,daure take da zani daurin qirji da kuma qaramin hijab fari,sai jakar kayan wankanta dake riqe a hannunta,daya hannun nata kuma wayarta ce
"Wanne irin sakarci ne haka zaki fadowa mutane ba sallama?,banason tsiyatakun banza da wofi fa?" Cuno bakinta tayi gaba tana sauke wayar daga fuskarta tana kallon anni
"Don girman Allah anni ki karba wayar da abbi ya baki ko zamu huta da ire iren takurar su ya jabir" gyara zamanta tayi tana kallonta sosai
"To...idan kuma naqi sai yaya kenan uwata?" Hannu laila ta yarfe,bataso annin ta hutsance mata,lallabata takeson yi ta karba a wuce wajen
"Anni.....yanzu fa wanka zan shiga,ashe muna hanya daxun ya kirani banga miscal dinsa ba sai yanzu,ina daga wayar ko tsayawa amsa sallamata baiyi ba ya hauni da balbalin masifa,Ni bansan sanda ya koma haka ba wall....." Maganar tata ta katse saboda shigowar wani kiran,saita duba sannan tace
"Gashinan ma" gaba data tattar wayar harda earpiece din jiki ta miqawa anni ta juyawa tana shirin ficewa
"Wannan zaren na jiki da kika hadani dashi shi zan qaqabawa kunnena?,bada ni ba gada a maqabarta,zoki tsige abinki ki karbi naji da gayan wayar ma" dole ta dawo ta cire matan yadda ta buqata da sauri don kada kiran ya katse ta sake jazawa kanta wani sabon mita da qorafin.
*Arewabooks:Huguma*
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 12
Ajiyar zuciya ta sauke sanda ta tabbatar ta maida sarqar wa anni,ta godewa Allah da ya hani inna furera sanya son zuciyarta a gaba ta hana a maidawa anni sarqar,ta tabbata da ta aikata haka ba zata taba samun nutsuwar zuciya ba,haka zuciyarta take,bata qaunar haqqi koda qanqani a kanta,dalilin da yasa ta guji kiwon dabbobinta da bugu kenan,ta zabi horar dasu da magana.
Sosai hankalinta yayi nisa cikin zuzzurfan tunani,abinda ya sanya kwata kwata bata ankara da tahowarsa ba,sai da taji ta bugi wani abu sannan ta tsaya cak,ta kuma ja da baya da sauri tana kai dubanta gabanta.
Himu ne,sanye da kayan fulani,ya fito a bafullataninsa sak,kayan sun matuqar karbarsa sun kuma haskashi matuqa,saidai babu fara'a ko walwala kwata kwata saman fuskarsa.
Gabanta ne yayi mummunar bugawa sanda ta tuna da gargadi da kuma izayar da tasha hannun inna furera duka akan himu,abinda ya sanyata yin gaba da sauri ta rabeshi zata wuce,saidai cikin hanzarin shima ya matsa ya tare mata hanyar,da azama ta koma daya hannun nan ma ya bita ya tare,ya kare ko ina,bata da zabi illa ta roqeshi
"Don girman Allah ka bani hanya na wuce"
"Saboda me maimunatu?,me yasa kike guduna?" Tsoro ne ya sake kamata,sam bazai fahimci halin da take ciki ba,wannan tsaiwar da yayi a gabanta sai takejin kamar ana tsigar ranta
"Magana nakeso muyi dake maimunatu" wace magana?,a yanzun akwai.maganar kuwa da ita din zata fahimta?
"Kayi haquri,bazai yiwuba,ka barni na wuce"
"Dole ki tsaya ki saurareni maimunatu,don me yasa zaki saurin bada kai akan soyyayarmu?,kodai dama bakya sona?ni daya nake kidina da rawata?" Tuni hawaye ya balle mata,himu so yake kawai ya janyo mata bala'i,baisan yanayin da take ciki ba,da bai tsaya haka a gabanta ya tilasta mata sai sunyi magana ba,bayan ita bafahimta take ba,ta juya baya a matuqar razane sanda taji takun tafiya,take qafafunta suka fara rawa,sai shima ya waiwaya yana duban hanyar.
Kaf jinin jikinta sai daya daskare sanda taga inuwar mutum kuma macace a wajen,abinda ta baiwa ranta shine daada ce ko zubaida ko safiya,ta saddaqar ta gama yawo,kashinta kuma ya bushe,tun daga fuskarta zuwa tafin qafarta sukayi sanyi qalau
"Kuyi haquri,na katse muku jin dadin ku ko?,zan dan wuce ne?" Laila ta fada tana dan sakin fuskarta,ta fuskanci akwai wani abu me kama da soyayya a tsakaninsu,to amma anni tasan da haka kuwa?.
Jin baquwar murya da sautin da ba na fulani ba ya taimaka wajen dawowarta hayyacinta,matsawa laila himu yayi ta fara wucewa,abinda ya baiwa maimunatu damar yin wuf tabi bayan lailan
"Maimunatu" ya kirayi sunanta,saita qara hanzari da kyau ta fara shawarar bi ta duhuwa don kada ma ya biyota ya jawo mata jarfa
"Ina sonki.maimunatu,kuma wallahi bazan fasa sonki ba koda ke baki sona,zanci gaba da sonki har sai na sameki a matsayin matata" kalamai na qarshe kenan dataji daga bakin himu,ta qara hanzari,tana jin cewa inama itadin tana cikin nau'in mata masu hanzari wajen tafiya,lallai da tayi amfani da wannan don ganin ta sake yin nesa da ibrahim.
"Haba 'yammata,saurin me kike haka?" Muryar laila dake biye da ita ta ratsa kunnuwanta,yadda ta juyo kawai zai gaya maka har yanzu a tsorace take
"ya kike gudun wanda yake sonki?" Laila ta fada a tausashe bayan ta iso gaban maimunatu ta tsaya,ta kuma dora hannunta saman kafadar maimunatun zuciyarta na narkewa a tausayinta.
Daddadan qamshin dake tashi jikin laila maimunatu ta zuqa zuwa hancinta,laushin turaren ya sanya zuciyarta karyewa,yadda lailan ta tambayeta cikin taushi da nuna kulawa yasa rauninta ya ninku,take hawaye ya cika idanunta,a wannan lokacin gaza tareshi tayi,sai kuka ya qwace mata.
Kasa hanata laila tayi,duba na tausayi takewa maimunatu,tana kwatanta kanta a matsayinta,tana kwatanta inda itace ta yaya zata rayu babu abbi babu momma?,ya rayuwarta zata kasance?,maimunatun jaruma ce qwarai kuma abar tausayi ce ga dukka wani me tausayi.
Dole ce zata sanyata ta guji himu ba din ya cancanci a gujeshi ba,bata da yadda zatayi matuqar tana son tsira da lafiyarta da kuma rayuwarta,goge hawayen fuskarta ta fara da tafin hannunta bayan taji zuciyarta ta fara mata sanyi daga radadi da suyar da take mata.
Maganar ta sanya inna furera dauke idanunta daga hararar da take danqarawa maimunatu zuwa kan anni,bayan ta wadatar fuskarta da murmushin yaqe
"Haka ai take,kuma har 'yar uwarta da muka baro a can ta fita" ta fadi tanason fidda gajenta kunya gaban surukarta da kuma baqin idanun da suke wajen
"To ma sha Allah,Allah ya dorar dasu akan hakan"
"Uhmmm...meen ameen"inna furera ta fada tana son nuna jin dadinta.
Yadda inna furera ta fada haka anni tasa salihu ya irga kudinta cas aka tafe mata,harda qaramar rawarta saboda farincikin ganin irin kudin data karba sama ta ka,lallai a duniya bata da masoyi kamar daadar himu,wadda ita tayi mata silar wannan ciniki mai gwaggwabar riba.
Har sun juya zasu wuce anni ta waiwayo tana duban maimunatu
"Jikata kema ai ya kamata ace an baki wani abu ko,saboda qoqarin nuna mana zabin qwarai da kikayi" qaramin murmushi mai cike da kunya da kuma kawaici ta sake,tayi qas da kanta ba tare da tace komai ba,kamar ma kuma taga hararar da inna furera ta fara auna mata
"Basai kin ban komai ba kaaka,haqqina ne nayi hakan don fita haqqin Allah a kaina" tabbas badon idanun da suke wajen ba ba abinda zai hana inna furera kai mata mangari,qiri qiri yarinyar nason jaza musu asara?,don batasan yawan kyautar da matar tayi nufin yi mata ba
"Gaskiya ne" anni ta fada,saita karba jakarta a hannun laila wadda duk wannan abun da ake hankalinta nakan daukar hotuna cikin wayarta kusa da dabbobin,don ta samun abun adanawa ya zame mata tarihi,kuma ta bada labarin xuwanta rugar,don kuwa da wayonta ba zata iya tuna yaushe tazo rugar na qarshe ba.
Sabbin kudi ta fitar ta irgasu a miqe ta miqa maimunatu
"Naji dadin riqe gaskiyarki,wannan kyauta ce bisa hakan" dan noqewa kadan tayi kamar ba zata karba ba,har sai da salihu ya sanya baki,sai data saci kallon inna furera taga yadda take watsa mata harara sannan tasa hannu biyu ta karba tana fadin
"Allah ya saka da alkhairi,ya maida ninkinsu"
"Ameennn" anni ta fada cikin jin dadin addu'ar maimunatun.
Bata tsammanin ko sassan nasu su anni sun bari inna furera ta miqa mata hannu,ko batayi.magana ba tasan me take nufi,shi yasa gaba daya batayi nufin amsar kudin ba,saboda tasan cewa zata raba matar da kudinta ne,ita kuma da tayi niyyar bawa ba zata mori komai a cikinsu ba,duka ta dunqule kudin hannun nata ta miqawa inna fureran,sannan ta tsugunna ta debi kayan aikinta ta fara gyara wajen bata ko waiwayeta ba.
Babu kunya babu kuma tsoron Allah ko daya a tattare da ita ta hade dukka kudaden ta irge abunta cas ta soke su tayi gaba abinta tana rera waqa,yau itakam ranta fes,mutuwa batayi mata komai ba sai rana data yi mata,banda silar mutuwar ina ita wannan dukiyar?,ina ita ina mallakar wadan nan kudade?,kudi kam sunzo mata a dai dai,tanadin bikin gajenta zata farayi tun yanzu,saboda bikin gata takeso tayi mata.
>>>>>>>>>>"sannu anni.....an gama komai ko?" Yuuma ta fada sanda take shigowa rumfarta dauke da kwanon sha da ta cikashi da damammiyar fura da nono wadda babu surkin sugar ko kadan a cikinsa
"Mun gama komai ramatu..dabbobi lafiyayyu,har sunso sufi na labaran din ma"
"Ai sunfi ma anni,sun hadu da makiyayiya mai hazaqa da iya kiwo,irin kiwon da babu ha'inci a ciki" yuuma ta fadi tana zama sosai gaban anni tana murmushi
"Ai naga alama,ko ba wata yarinya maimunatu ba?"
"Itafa,baiwar Allah" yuuma ta fada fuskarta na dan canza yanayi
"Ai tunda na shigo Allah yake hadamu,naketa ganin abubuwan mamaki daga wajen yarinyar,na jima banga me kiwo irinta ba,sannan abinda zai sake baki mamaki da ita.....wajen cinikin nan,kowacce dabba da muka nuna manaso sai datayi mana bayanin lafiyarta da sauransu,babu ha'inci" cikin gamsuwa yuuma take gyada kai
"Bata tsinta a qasa ba ai,gado ne me kyau daga wajen mahaifiyarta,Allah ya jiqan ruma"
"Allah sarki,kice marainiya ce?" Anni ta fada tana jan kwanon furar gabanta tana qoqarin budewa
"Marainiya ce,wadda aka kasa yi mata riqo na tsakani da Allah.....kinsan mahaifiyarta anni,kin tuna matar da kikaga wata balama me juna biyu a wajenta kikai sha'awarta shekarun baya can da suka shude,ta qara miki da kyautar wata akuya,akuyar da kikace ta miki albarka fiye da kowacce dabba a kiwonki?"
"Af.....af ina zan manta da wannan baiwar Allar,dama itace mahaifiyarta?"
"Itace anni" yuuma ta amsa mata tana dauko wani kwanon da ta shaqewa anni shi da dambu me dumi tana aje mata
"Allahu akhbar......." Maganar annin ta tsaya sakamakon shigowar laila tana qananun mita.
Daga kai anni tayi ta dubeta,daure take da zani daurin qirji da kuma qaramin hijab fari,sai jakar kayan wankanta dake riqe a hannunta,daya hannun nata kuma wayarta ce
"Wanne irin sakarci ne haka zaki fadowa mutane ba sallama?,banason tsiyatakun banza da wofi fa?" Cuno bakinta tayi gaba tana sauke wayar daga fuskarta tana kallon anni
"Don girman Allah anni ki karba wayar da abbi ya baki ko zamu huta da ire iren takurar su ya jabir" gyara zamanta tayi tana kallonta sosai
"To...idan kuma naqi sai yaya kenan uwata?" Hannu laila ta yarfe,bataso annin ta hutsance mata,lallabata takeson yi ta karba a wuce wajen
"Anni.....yanzu fa wanka zan shiga,ashe muna hanya daxun ya kirani banga miscal dinsa ba sai yanzu,ina daga wayar ko tsayawa amsa sallamata baiyi ba ya hauni da balbalin masifa,Ni bansan sanda ya koma haka ba wall....." Maganar tata ta katse saboda shigowar wani kiran,saita duba sannan tace
"Gashinan ma" gaba data tattar wayar harda earpiece din jiki ta miqawa anni ta juyawa tana shirin ficewa
"Wannan zaren na jiki da kika hadani dashi shi zan qaqabawa kunnena?,bada ni ba gada a maqabarta,zoki tsige abinki ki karbi naji da gayan wayar ma" dole ta dawo ta cire matan yadda ta buqata da sauri don kada kiran ya katse ta sake jazawa kanta wani sabon mita da qorafin.
*Arewabooks:Huguma*
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 12
Ajiyar zuciya ta sauke sanda ta tabbatar ta maida sarqar wa anni,ta godewa Allah da ya hani inna furera sanya son zuciyarta a gaba ta hana a maidawa anni sarqar,ta tabbata da ta aikata haka ba zata taba samun nutsuwar zuciya ba,haka zuciyarta take,bata qaunar haqqi koda qanqani a kanta,dalilin da yasa ta guji kiwon dabbobinta da bugu kenan,ta zabi horar dasu da magana.
Sosai hankalinta yayi nisa cikin zuzzurfan tunani,abinda ya sanya kwata kwata bata ankara da tahowarsa ba,sai da taji ta bugi wani abu sannan ta tsaya cak,ta kuma ja da baya da sauri tana kai dubanta gabanta.
Himu ne,sanye da kayan fulani,ya fito a bafullataninsa sak,kayan sun matuqar karbarsa sun kuma haskashi matuqa,saidai babu fara'a ko walwala kwata kwata saman fuskarsa.
Gabanta ne yayi mummunar bugawa sanda ta tuna da gargadi da kuma izayar da tasha hannun inna furera duka akan himu,abinda ya sanyata yin gaba da sauri ta rabeshi zata wuce,saidai cikin hanzarin shima ya matsa ya tare mata hanyar,da azama ta koma daya hannun nan ma ya bita ya tare,ya kare ko ina,bata da zabi illa ta roqeshi
"Don girman Allah ka bani hanya na wuce"
"Saboda me maimunatu?,me yasa kike guduna?" Tsoro ne ya sake kamata,sam bazai fahimci halin da take ciki ba,wannan tsaiwar da yayi a gabanta sai takejin kamar ana tsigar ranta
"Magana nakeso muyi dake maimunatu" wace magana?,a yanzun akwai.maganar kuwa da ita din zata fahimta?
"Kayi haquri,bazai yiwuba,ka barni na wuce"
"Dole ki tsaya ki saurareni maimunatu,don me yasa zaki saurin bada kai akan soyyayarmu?,kodai dama bakya sona?ni daya nake kidina da rawata?" Tuni hawaye ya balle mata,himu so yake kawai ya janyo mata bala'i,baisan yanayin da take ciki ba,da bai tsaya haka a gabanta ya tilasta mata sai sunyi magana ba,bayan ita bafahimta take ba,ta juya baya a matuqar razane sanda taji takun tafiya,take qafafunta suka fara rawa,sai shima ya waiwaya yana duban hanyar.
Kaf jinin jikinta sai daya daskare sanda taga inuwar mutum kuma macace a wajen,abinda ta baiwa ranta shine daada ce ko zubaida ko safiya,ta saddaqar ta gama yawo,kashinta kuma ya bushe,tun daga fuskarta zuwa tafin qafarta sukayi sanyi qalau
"Kuyi haquri,na katse muku jin dadin ku ko?,zan dan wuce ne?" Laila ta fada tana dan sakin fuskarta,ta fuskanci akwai wani abu me kama da soyayya a tsakaninsu,to amma anni tasan da haka kuwa?.
Jin baquwar murya da sautin da ba na fulani ba ya taimaka wajen dawowarta hayyacinta,matsawa laila himu yayi ta fara wucewa,abinda ya baiwa maimunatu damar yin wuf tabi bayan lailan
"Maimunatu" ya kirayi sunanta,saita qara hanzari da kyau ta fara shawarar bi ta duhuwa don kada ma ya biyota ya jawo mata jarfa
"Ina sonki.maimunatu,kuma wallahi bazan fasa sonki ba koda ke baki sona,zanci gaba da sonki har sai na sameki a matsayin matata" kalamai na qarshe kenan dataji daga bakin himu,ta qara hanzari,tana jin cewa inama itadin tana cikin nau'in mata masu hanzari wajen tafiya,lallai da tayi amfani da wannan don ganin ta sake yin nesa da ibrahim.
"Haba 'yammata,saurin me kike haka?" Muryar laila dake biye da ita ta ratsa kunnuwanta,yadda ta juyo kawai zai gaya maka har yanzu a tsorace take
"ya kike gudun wanda yake sonki?" Laila ta fada a tausashe bayan ta iso gaban maimunatu ta tsaya,ta kuma dora hannunta saman kafadar maimunatun zuciyarta na narkewa a tausayinta.
Daddadan qamshin dake tashi jikin laila maimunatu ta zuqa zuwa hancinta,laushin turaren ya sanya zuciyarta karyewa,yadda lailan ta tambayeta cikin taushi da nuna kulawa yasa rauninta ya ninku,take hawaye ya cika idanunta,a wannan lokacin gaza tareshi tayi,sai kuka ya qwace mata.
Kasa hanata laila tayi,duba na tausayi takewa maimunatu,tana kwatanta kanta a matsayinta,tana kwatanta inda itace ta yaya zata rayu babu abbi babu momma?,ya rayuwarta zata kasance?,maimunatun jaruma ce qwarai kuma abar tausayi ce ga dukka wani me tausayi.
Dole ce zata sanyata ta guji himu ba din ya cancanci a gujeshi ba,bata da yadda zatayi matuqar tana son tsira da lafiyarta da kuma rayuwarta,goge hawayen fuskarta ta fara da tafin hannunta bayan taji zuciyarta ta fara mata sanyi daga radadi da suyar da take mata.