Sashe 19
Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Sahid ni mahaifiyar ka Binta , babu abin da zance maka tsakanina da kai , abu guda dana sani ka ci amana, kuma tana tafe domin cinka , ka je za ka gani."
Tana gama magana ta shige daki , Jibril ma ya shige dakinshi ya sanya kaya ya fita , yana fita ya ci karo da 'yan sanda tare da Umar da Jafar .
Kafin su yi masa tambayar ina Sahid, Sahid ya fito suka sashi a mota suka tafi .
Share and comment...............................📚
Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
Editing❌
_________________________________________
Page 41 & 42
Hankalin Harun duk yabi ya tashi
ganin yadda wasu abokanshi da dama an turo musu sakon ni da yake tabbatar zasu tafi training amma shi Harun bai ga wannan sako ba ko tuntuba, hakan ya sa yake bibiyar inda matsalar take .
Anan ma Umar Allah ya ba shi sa'a sai dai ba ya so ya tafi training ba tare da yaga yadda kotu za tai ga Sahid ba ,
sai dai jafar ya tabbatar masa babu abin da zai gagare shi , tun da suna da kwararran lauya , ga kuma baba GARBA shi ma ya zo.
Haka dai Umar ya hakura ya tafi kaduna ba tare da ya so ba.
Maryam ce ta fito da gudu daga daki tana sheka amai , tana gama amai ta malale a wajen tana shure-shure .
Haka cikin gaggawa mahaifiyar ta , ta kira malam na lado suka tafi asubiti.
Yadda alakar Harun da surayya take , lokacin da yake sanar da ita matsalar da ya samu , har an tafi training babu shi , ya roki surayya alfarma data mika takardunshi ga mahaifin ta ambassador, domin ya yi magana da lu'utanal a kan shi.
Haka kuwa aka yi surayya ta karba , domin a halin yanzu ma takardun suna hannun mahaifin ta , amma har yau bai samu damar magana da lu utanal ba .
Allah sarki Maryam, lamarin dai har yanzu babu dadi , malam na lado da babarta sun shiga damuwa , haka dai dactor ya sa akai mata gwaje-gwaje , daga bisani ta samu bacci
Lokacin dasu Hajjiya, matar Alaji Kabiru da zainab suka zo dubata , har suka dawo bata farka ba, Zainab dai ta ji tausayin kawartata tana kuma mata fatan samun lafiya..
Fitowar ambassador ke nan daga gidansu Surayya,
ya hau mota rike da wasu takardu a hannunshi, sannan driver ya ja mota suka tafi .
Ambassador sake kallon wannan takardun na hannunshi ya ke yi , lokaci guda kuma yana sake mamakin yadda saurayin 'yar tashi Harun ya zama mai irin wannan mummunan hali da lu'utanal ya sanar masa.
Wanda lokaci guda yana sake tuna maganar da tafi tsaya masa a rai , da lu'utanal ya fada kamar haka .
"Lokacin da Hauwa ta zo min da zancen, sai da muka bibiyi rayuwar shi , muka tabbatar da zargin da ake masa sannan muka hana shi wannan dama , irin Harun mummunan tashin hankali ne zamansu cikin al'uma, kuma bugu da kari mu kara ba su gwarin gwiwa tare da basu aiki irin na soja , ambassador hakan ba mai faruwa ba ne."
Ambassador ya yi ajiyar zuciya bayan tunanin da ya gama .
Har suka isa cikin gida, ambassador jefi jefi abin yana damunshi , daga karshe yana shiga cikin gidan ya zauna a falo
Yadda matarshi ta ganshi haka , ya sa ta fara tambayar ko lafiya, nan take ya sa ta kira masa surayya.
Bayan surayya ta zo ya mika mata takardun Harun yana cewa
"Ki maza ki kira wannan yaron ki ba shi , kar na sake jin komai daga gare shi , hatta mu'amalar ku na wargaza ta."
Dauuu ta ji gabanta ya fadi
"Rabuwa da Harun kuma yanzu." Surayya ta fad'a a cikin ranta
ta kalli ambassador tana cewa cikin harshen turanci , "Dady me ya sa kuma ? Me yake faruwa."?
Nan take ambassador ya sanar wa da Surayya komai , da irin binciken da lu'utanal sukai a kan shi , har suka haram ta masa aikin soja."
Surayya ta yi matukar mamaki da jin hakan , abin ya matukar d'aure mata kai.
Tashi ta yi ta shiga daki da nufin kiran Harun ,
Amma sai ta fasa , ta kira Hauwa ta ce ta zo tana ji ranta.
Bayan Hauwa ta Harun Surayya ta sanar mata halin da take ciki , nan Hauwa ta sake tabbatar mata da waye Harun, ta tabbatar mata yaudara ce ta kawo shi, babu yadda Surayya ta iya ,
Ta kalli Hauwa tana cewa, "To yanzu mene abin yi Hauwa."
Hauwa ta ce , "Ki kira shi ya zo."
Ko awa daya Harun bai 'ba ta ba ya karaso
Ya shigo yayi parking da motar shi , sannan ya dauki waya ya kira Surayya.
"Ya zo."
Surayya ta yi maganar sa'ilin da ta kashe wayar tana kallon Hauwa.
Hauwa ta ce , "Ta shi mu je."
Surayya ta kwashi takardun suka fita .
Tun da ya hango su ya fara washe baki domin a lissafinsa
Surayya zata gabatar masa da kawarta ne , ya sa suka taho tare .
Suna karasowa Surayya ta sake had'e ranta , ammo sam Harun bai lura da hakan ba, domin yadda ya ga kawartata Hauwa zazzafa ya sa hankalin shi ya koma kanta yana kallonta sama da kasa.
Yadda Surayya ta lura da hakan ya sa ta sake jin tsanarshi ta kuma yadda da abin da aka fada mata.
Lokaci guda ya maida kallon shi ga Surayya yana cewa
"Annurin Rayuwata, barka da fitowa."
Tasssssss Ya ji saukar mari a fuskarshi
Da gigicewa da tsananin jin zafin marin da mamaki ya kalli Surayya , hannun shi dafe a kuncinsa .
Cikin turanci Surayya ta fara magana, "Kalle ni da kyau mayaudari, azzalumi ,na tsaneka Harun ."
Ta d'ago hannunta na hagu da ta rike takardun ta watsa masa
Sannan da yaren Hausa ta cigaba da cewa , "Sai ka kwashe su , kuma kai da aikin soja har abada. Allah ya mana tsari da kai yi waje ."
"Haba Surayya waya shiga tsakaninmu haka , ban yi muki komai ba , amma...."
Kafin ya karasa maganar ta sake shara masa mari tana cewa, "Matukar baka fita a gidan nan ba ka sake magana sai na sa an kulle ka."
Harun matukar mamaki ya rufe shi ya kasa gane dalili, idan ma shi mayaudari ne ta ya ta sani. Abin ya d'aure masa kai sosai.
Ya durkusa ya d'ebi takardunsa ya shiga mota ya tafi .
Surayya ta yi ajiyar zuciya tana kallon Hauwa.
Malam na lado yana Cikin tashin hankali , jikin Maryam babu kyau , gida suka koma sakamakon tabbatarwar likita cewa Maryam tana da ciki , sun shiga tashin hankali sosai
Tana matukar jin jiki sosai ko magana bata iya wa amma haka Malam na lado ya tsaya a kanta yana mata tsawa yana tambayar wanda ya yi mata ciki .
"Maryam yanzu wannan shi ne abin da zaki bar mana , cikin shege gidan malam guda." Mahaifiyar ta ta karasa maganar cikin kuka
"Wallahi kin bamu kunya kin cutar damu."
Maryam cikin radadi tana kuka tana kokarin magana ta fara neman yafiyarsu tana sanar dasu ba ba halinta ba ne ba kuma lefinta ba ne.
"To waye ya yi miki ciki Maryam." ?Malam ya tambaya cikin zafi .
Maryam tana gumi cikin jinya tana kuka ta fada musu yadda Harun ya yaudare ta .
"Lallai wannan yaron baisan gidan da ya zo ba , zan kuwa nuna masa ni Malam na lado malumtata ba a banza take ba."
Cikin huci ya karasa maganar
"Wallahi baba sam ba zan yi abin da zai cutar daku ba , daga karshe ake tabbatar min haka halinshi yake , ya yaudari mata da yawa, dah nasan zanga irin wannan ranar da na kashe kai na kafin ta zo."
Maryam ce ta yi maganar tana kuka , yayin da mahaifinta ya yaji duk tausayinta ya kamashi.
Haka ma mahaifiyarta ita ma ta fashe da kuka tana rarrashin Maryam.
"Allah ka gani na yi kokarin tsare amanar da ka bani ta Maryam, amma ga yadda ka tsaro lamarin ka."
Malam na lado ya fada cikin matukar rauni
Sannan ya kalli Maryam yana cewa, "Shi ya sa naso ya turo iyayensa , amma tabbas na yi sakaci , na yi babban kuskuren da bazan yafe wa kaina ba."
Share and comment...........................📚
Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
Editing❌
_________________________________________
Page 43 & 44
Anan kuma cikin kotu an yi zama na farko tare da karanta irin tuhumar da ake wa Sahid, amma ya'ki yadda da wannan tuhuma , yana sanar da kotu babu wata cin amana da zai iya aikatawa ko handuma ,wanda har zata yi sanadin mutuwar Kalisa.
Jibril da babarshi ko kotun ba su halatta ba , haka alkali ya d'age shari'ar zuwa wani lokaci, tare da ba da belin Sahid.
Hauwa ce kwance kan kafar Hajjiya.
Hajjiya ta ce ,"Wai yaushe ne Abdallaah zai dawo daga Germany zamanshi ne fa ya sa bikin ku har yau ba rana. "
Hauwa ta yi Murmushi tana cewa, "Ai momy ya kusan dawowa, shi ma ya damu ya dawo fa."
Hajjiya ta ce ,"Ai gara dai ayi -ayi a wuce gun."
Hauwa ta ce ,"Yawwa momy kinga ashe wannan yaron Harun, wanda abokina Mahmud ya yi magana a kan shi , har Surayya yaje gunta."
Hajjiya ta yi dariya tana cewa, "Tabbb amma wannan yaro ko d'anbanza, yanzu shi ina Mahmud din."
Hauwa ta ce ,"Ba ya nan , amma ya ce idan ya shigo gari zai zo ya gaida Dady."
Hajjiya ta ce ,"To Allah ya kawo shi."
A halin yanzu kowa yana ta magana masu gulma da yamad'd'i suna ta yi cewa Maryam yar Malam na lado ta yi cikin shege , daga wanda zasu zagi ta da iyayenta sai masu Allah ya kyauta da fatan shiriya.......
Musamman yadda abin ya yi tsamari da suka koma asubiti aka tabbatar musu tana da cuta mai karya garkuwar jiki , nan malam hankalin shi ya sake tashi , haka suma almajiran malam duk abin bai yi musu dadi ba.
Tana gama magana ta shige daki , Jibril ma ya shige dakinshi ya sanya kaya ya fita , yana fita ya ci karo da 'yan sanda tare da Umar da Jafar .
Kafin su yi masa tambayar ina Sahid, Sahid ya fito suka sashi a mota suka tafi .
Share and comment...............................📚
Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
Editing❌
_________________________________________
Page 41 & 42
Hankalin Harun duk yabi ya tashi
ganin yadda wasu abokanshi da dama an turo musu sakon ni da yake tabbatar zasu tafi training amma shi Harun bai ga wannan sako ba ko tuntuba, hakan ya sa yake bibiyar inda matsalar take .
Anan ma Umar Allah ya ba shi sa'a sai dai ba ya so ya tafi training ba tare da yaga yadda kotu za tai ga Sahid ba ,
sai dai jafar ya tabbatar masa babu abin da zai gagare shi , tun da suna da kwararran lauya , ga kuma baba GARBA shi ma ya zo.
Haka dai Umar ya hakura ya tafi kaduna ba tare da ya so ba.
Maryam ce ta fito da gudu daga daki tana sheka amai , tana gama amai ta malale a wajen tana shure-shure .
Haka cikin gaggawa mahaifiyar ta , ta kira malam na lado suka tafi asubiti.
Yadda alakar Harun da surayya take , lokacin da yake sanar da ita matsalar da ya samu , har an tafi training babu shi , ya roki surayya alfarma data mika takardunshi ga mahaifin ta ambassador, domin ya yi magana da lu'utanal a kan shi.
Haka kuwa aka yi surayya ta karba , domin a halin yanzu ma takardun suna hannun mahaifin ta , amma har yau bai samu damar magana da lu utanal ba .
Allah sarki Maryam, lamarin dai har yanzu babu dadi , malam na lado da babarta sun shiga damuwa , haka dai dactor ya sa akai mata gwaje-gwaje , daga bisani ta samu bacci
Lokacin dasu Hajjiya, matar Alaji Kabiru da zainab suka zo dubata , har suka dawo bata farka ba, Zainab dai ta ji tausayin kawartata tana kuma mata fatan samun lafiya..
Fitowar ambassador ke nan daga gidansu Surayya,
ya hau mota rike da wasu takardu a hannunshi, sannan driver ya ja mota suka tafi .
Ambassador sake kallon wannan takardun na hannunshi ya ke yi , lokaci guda kuma yana sake mamakin yadda saurayin 'yar tashi Harun ya zama mai irin wannan mummunan hali da lu'utanal ya sanar masa.
Wanda lokaci guda yana sake tuna maganar da tafi tsaya masa a rai , da lu'utanal ya fada kamar haka .
"Lokacin da Hauwa ta zo min da zancen, sai da muka bibiyi rayuwar shi , muka tabbatar da zargin da ake masa sannan muka hana shi wannan dama , irin Harun mummunan tashin hankali ne zamansu cikin al'uma, kuma bugu da kari mu kara ba su gwarin gwiwa tare da basu aiki irin na soja , ambassador hakan ba mai faruwa ba ne."
Ambassador ya yi ajiyar zuciya bayan tunanin da ya gama .
Har suka isa cikin gida, ambassador jefi jefi abin yana damunshi , daga karshe yana shiga cikin gidan ya zauna a falo
Yadda matarshi ta ganshi haka , ya sa ta fara tambayar ko lafiya, nan take ya sa ta kira masa surayya.
Bayan surayya ta zo ya mika mata takardun Harun yana cewa
"Ki maza ki kira wannan yaron ki ba shi , kar na sake jin komai daga gare shi , hatta mu'amalar ku na wargaza ta."
Dauuu ta ji gabanta ya fadi
"Rabuwa da Harun kuma yanzu." Surayya ta fad'a a cikin ranta
ta kalli ambassador tana cewa cikin harshen turanci , "Dady me ya sa kuma ? Me yake faruwa."?
Nan take ambassador ya sanar wa da Surayya komai , da irin binciken da lu'utanal sukai a kan shi , har suka haram ta masa aikin soja."
Surayya ta yi matukar mamaki da jin hakan , abin ya matukar d'aure mata kai.
Tashi ta yi ta shiga daki da nufin kiran Harun ,
Amma sai ta fasa , ta kira Hauwa ta ce ta zo tana ji ranta.
Bayan Hauwa ta Harun Surayya ta sanar mata halin da take ciki , nan Hauwa ta sake tabbatar mata da waye Harun, ta tabbatar mata yaudara ce ta kawo shi, babu yadda Surayya ta iya ,
Ta kalli Hauwa tana cewa, "To yanzu mene abin yi Hauwa."
Hauwa ta ce , "Ki kira shi ya zo."
Ko awa daya Harun bai 'ba ta ba ya karaso
Ya shigo yayi parking da motar shi , sannan ya dauki waya ya kira Surayya.
"Ya zo."
Surayya ta yi maganar sa'ilin da ta kashe wayar tana kallon Hauwa.
Hauwa ta ce , "Ta shi mu je."
Surayya ta kwashi takardun suka fita .
Tun da ya hango su ya fara washe baki domin a lissafinsa
Surayya zata gabatar masa da kawarta ne , ya sa suka taho tare .
Suna karasowa Surayya ta sake had'e ranta , ammo sam Harun bai lura da hakan ba, domin yadda ya ga kawartata Hauwa zazzafa ya sa hankalin shi ya koma kanta yana kallonta sama da kasa.
Yadda Surayya ta lura da hakan ya sa ta sake jin tsanarshi ta kuma yadda da abin da aka fada mata.
Lokaci guda ya maida kallon shi ga Surayya yana cewa
"Annurin Rayuwata, barka da fitowa."
Tasssssss Ya ji saukar mari a fuskarshi
Da gigicewa da tsananin jin zafin marin da mamaki ya kalli Surayya , hannun shi dafe a kuncinsa .
Cikin turanci Surayya ta fara magana, "Kalle ni da kyau mayaudari, azzalumi ,na tsaneka Harun ."
Ta d'ago hannunta na hagu da ta rike takardun ta watsa masa
Sannan da yaren Hausa ta cigaba da cewa , "Sai ka kwashe su , kuma kai da aikin soja har abada. Allah ya mana tsari da kai yi waje ."
"Haba Surayya waya shiga tsakaninmu haka , ban yi muki komai ba , amma...."
Kafin ya karasa maganar ta sake shara masa mari tana cewa, "Matukar baka fita a gidan nan ba ka sake magana sai na sa an kulle ka."
Harun matukar mamaki ya rufe shi ya kasa gane dalili, idan ma shi mayaudari ne ta ya ta sani. Abin ya d'aure masa kai sosai.
Ya durkusa ya d'ebi takardunsa ya shiga mota ya tafi .
Surayya ta yi ajiyar zuciya tana kallon Hauwa.
Malam na lado yana Cikin tashin hankali , jikin Maryam babu kyau , gida suka koma sakamakon tabbatarwar likita cewa Maryam tana da ciki , sun shiga tashin hankali sosai
Tana matukar jin jiki sosai ko magana bata iya wa amma haka Malam na lado ya tsaya a kanta yana mata tsawa yana tambayar wanda ya yi mata ciki .
"Maryam yanzu wannan shi ne abin da zaki bar mana , cikin shege gidan malam guda." Mahaifiyar ta ta karasa maganar cikin kuka
"Wallahi kin bamu kunya kin cutar damu."
Maryam cikin radadi tana kuka tana kokarin magana ta fara neman yafiyarsu tana sanar dasu ba ba halinta ba ne ba kuma lefinta ba ne.
"To waye ya yi miki ciki Maryam." ?Malam ya tambaya cikin zafi .
Maryam tana gumi cikin jinya tana kuka ta fada musu yadda Harun ya yaudare ta .
"Lallai wannan yaron baisan gidan da ya zo ba , zan kuwa nuna masa ni Malam na lado malumtata ba a banza take ba."
Cikin huci ya karasa maganar
"Wallahi baba sam ba zan yi abin da zai cutar daku ba , daga karshe ake tabbatar min haka halinshi yake , ya yaudari mata da yawa, dah nasan zanga irin wannan ranar da na kashe kai na kafin ta zo."
Maryam ce ta yi maganar tana kuka , yayin da mahaifinta ya yaji duk tausayinta ya kamashi.
Haka ma mahaifiyarta ita ma ta fashe da kuka tana rarrashin Maryam.
"Allah ka gani na yi kokarin tsare amanar da ka bani ta Maryam, amma ga yadda ka tsaro lamarin ka."
Malam na lado ya fada cikin matukar rauni
Sannan ya kalli Maryam yana cewa, "Shi ya sa naso ya turo iyayensa , amma tabbas na yi sakaci , na yi babban kuskuren da bazan yafe wa kaina ba."
Share and comment...........................📚
Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
Editing❌
_________________________________________
Page 43 & 44
Anan kuma cikin kotu an yi zama na farko tare da karanta irin tuhumar da ake wa Sahid, amma ya'ki yadda da wannan tuhuma , yana sanar da kotu babu wata cin amana da zai iya aikatawa ko handuma ,wanda har zata yi sanadin mutuwar Kalisa.
Jibril da babarshi ko kotun ba su halatta ba , haka alkali ya d'age shari'ar zuwa wani lokaci, tare da ba da belin Sahid.
Hauwa ce kwance kan kafar Hajjiya.
Hajjiya ta ce ,"Wai yaushe ne Abdallaah zai dawo daga Germany zamanshi ne fa ya sa bikin ku har yau ba rana. "
Hauwa ta yi Murmushi tana cewa, "Ai momy ya kusan dawowa, shi ma ya damu ya dawo fa."
Hajjiya ta ce ,"Ai gara dai ayi -ayi a wuce gun."
Hauwa ta ce ,"Yawwa momy kinga ashe wannan yaron Harun, wanda abokina Mahmud ya yi magana a kan shi , har Surayya yaje gunta."
Hajjiya ta yi dariya tana cewa, "Tabbb amma wannan yaro ko d'anbanza, yanzu shi ina Mahmud din."
Hauwa ta ce ,"Ba ya nan , amma ya ce idan ya shigo gari zai zo ya gaida Dady."
Hajjiya ta ce ,"To Allah ya kawo shi."
A halin yanzu kowa yana ta magana masu gulma da yamad'd'i suna ta yi cewa Maryam yar Malam na lado ta yi cikin shege , daga wanda zasu zagi ta da iyayenta sai masu Allah ya kyauta da fatan shiriya.......
Musamman yadda abin ya yi tsamari da suka koma asubiti aka tabbatar musu tana da cuta mai karya garkuwar jiki , nan malam hankalin shi ya sake tashi , haka suma almajiran malam duk abin bai yi musu dadi ba.