Sashe 11
Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
.A halin yanzu Kalisa ta dawo hayyacinta , doctor Aisha tana iya yinta domin samawa Kalisa lafiya , sai dai ta tabbatar musu fitar da ita ne kawai mafita .
Jafar har gida ya je neman Sahid sai dai tun jiya mahaifinsa ya tabbatar ba ya nan , sannan dukkan SMS din sa basa tafiya .
Ran malam Aminu ya yi matukar baci sosai dana mahaifiyarsa, musamman jin halin da Kalisa ke ciki ma ya tabbatar musu gobe zai zo garin ya ga jikin nata , kuma zai nemo Sahid din in sha Allah, Jafar jikinsa duk ba dadi ya koma asubitin.
Shugaban makaranta ne da Uncle Yahaya da bayis tare da wasu malamai biyu zaune a falonsu Laila.
Gefe guda kuma ga Laila da mahaifiyarta zaune ,ga kuma barrister Adam ran shi bace .
"Dan Allah barrister Adam ka duba wannan lamarin, mun yi kuskure sosai wanda a tarihin DR.DD ba a taba irin sa ba , amma a matsayin mu na masu ilmi mu yi sulhu dan Allah barrister." Shugaban makarantar ya aje maganar cikin tausayin kanshi .
Amma barrister Adam kamar sun sake fama masa ciwo haka ya fara magana.
"A she kuna da ilmin kuka aikata hakan , ni fa na gama magana kawai ku je ku nemi lauyan da zai tsaya muku , dan haka ku fitar mini a gida kawai."
Idanun shugaban makarantar ya ciko da ruwa ya kalli barrister yana cewa, "Wannan makaranta ita ce cigabana rufin asirina wallahi sunan ta zai baci barrister ka taimake ni."
Barrister tsaye ya tashi yana cewa "Ciwon zuciya ne ya sameta yanzu a kan ku , ta ya zan share wannan lamarin kamar ba kaunar ta nake ba ko ina jin tsoron ku."
Uncle Yahaya ya yi kasa da kai cikin jin haushin kansa.
Laila kuwa ganin yadda shugaban nasu Doctor Dauda ya shiga wani yanayi ya sa taji duk tausayinshi ya kamata, cikin sanyin murya Laila ta ce ,"Dady."!
Barrister Adam ya kalleta yayin da duk kowa ya maida hankali gare ta .
"Ni ce aka yi wa komai dady amma abin kai ne ya shafa , bani da wani farin ciki sama da kai, hakan ya sa wannan ciwon dole ya barni tun da ina tare da kai."
Tai ajiyar zuciya tana sake cewa "Ina matukar girmama shugaba kuma wannan tarbiyar ku ce
Duk abin da ya faru da kai wanda ba za ka taba mancewa dashi ba kuma idan ka tuna kanajin ciwonsa to wannan shi ne Gubar Rayuwarka."
Ta aje maganar tana kallon uncle Yahaya ,yayin da ya yi kasa da kanshi .
Mahaifinta ta kalla barrister Adam tana cewa "Dady dacter ba shi da laifi dan Allah ka janye karar."
Kowa ya kalleta cikin mamaki tare da sa'ke-sa'ke kala-kala da kowa ya ke yi a ransa.
Cikin wani Murmushin ta kaici barrister Adam ya ce "Babu ruwanki Laila wannan maganar kar na sake jinta a bakin ki , dole ne na dauki mataki, shin ko baki san wanne kalar jiwo suka jawo miki ba ne , ke ce kawai Allah ya bani kuma duk wanda ya yi kuskure irin wannan dole hankali na ya tashi idan ban dauki mataki ba Laila."
Cikin hawaye Laila ta tashi tsaye tana kallon barrister da dukkan girmamawa ta fara magana.
"Dady ni kaina nasan kana kaunata ,
amma wannan shi ne Gubar Rayuwata domin ba zan taba mancewa ba amma dan Allah dady ka janye karar."
Ta karasa maganar yayin da wasu hawaye suka zubo mata.
Hakan ya sa barrister Adam ya kalli Uncle Yahaya yana cewa .
Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
*AUTAR MARUBUTA CE*✍🏻👼🏻
🌹__________🌹_________🌹__________🌹_________🌹
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_🤲🏼
<><><🌹><><><>🌹<><><>🌹<><><><>🌹<><><><><>🌹<><>
Page 23 & 24
"Laila ina kaunar ta." Ya fad'awa Yahaya
sannan ya kalli doctor ya ce "Na janye karar tare da sharadin matukar Laila ta mutu sanadin wannan ciwon to akwai babban tashin hankali."
"Babu abin da zai samu Laila in sha Allah barrister, sannan na yi alkawarin duk in da magani yake zan ke nema mata har ta sami lafiya."
Shugaban ya yi maganar cikin tashin hankali da rawar murya
"Lafiya ta Allah ce kuma ni zan cigaba da nema mata magani , dan haka zaku iya tafiya nasan kun bar d'alubai a makaranta."
Barrister Adam yana gama maganar ya shige ciki .
Sannan suka yi sallama da Hajjiya da Laila suka fito
DR Dauda cikin fusata ya fito ranshi matukar bace suka dauki hanyar makaranta, babu wanda ya ce da kowa komai har suka isa makarantar
Suna shiga shugaba ya sa a fito assembly hakan ya sa wasu malaman mamaki da tunani
Bayan kowa ya fito suma malaman suka hallara
Kowa yana iya ganin 'bacin rai da damuwa a fuskar dactor,
Bai jira wani gabatar da abin da aka saba ba ya fara magana
"Wato duk kun debi zancen Laila kun yada a gari ta fadi ta kamu da ciwo , shi ke nan
ina jan kunnenku da duk yarinyar da wani malami ya ce yana sonta suka fara soyayya zamu dauki mummunan mataki wallahi a kan su."
Ya kalli Uncle Yahaya sannan ya ce " Daga yau mun sallami Yahaya a wannan makaranta, babu wanda zaike kawo mana farmaki ba mu dakatar dashi ba , idan kunne yaji ."
'Dalubai suka karasa masa maganar cikin murya mai karfi
Wani abu ne ya tirnike zuciyar uncle Yahaya da abin da shugaba ya yi masa .
Hakan ya sa bayan ya koma office ya je ya same shi
"Shugaba sallama ta fa kayi gaban d'alubai." Uncle Yahaya ya yi maganar cikin maraici
haka shi ma shugaba ya fara magana "Hukuncin da zan maka ke nan domin haka ne ya dace da kai , kuma kaji ka sani ko albashi ba zan biyaka ba , zan yi amfani dashi na gyara 'barnar da kamin cikin makaranta, fitar mini a office."
Uncle Yahaya ya fita cikin damuwa ya nufi gida .
koda yaje gidan ya ga ya masa duhu kakarshi ta bar masa duniya , babu wani hanyar samun kud'i da yake dashi yanzu, bare ya nemi matan da ya saba , duk yaji duniya ta masa zafi sosai .
Yana cikin wannan yanayin ne sai ga kiran Fa'iza ya shigo masa , ba tare da ya boye yanayin da yake ciki ba ya fara magana da ita .
Da baba anje da Nabila ne zaune a d'akin Kalisa dake asubiti,
a wannan lokacin ne baba ta kàlli Kalisa tana cewa "Yau dai Kalisa na ga jikin naki da sauki Allah ya dorar dashi."
Kalisa cikin zuciyar ta ta ayyana cewa "Kawai dauriya nake baba , amma Allah ne yasan abin da nake ji."
Nabila ce ta ce "Amma aunty Kalisa cikin ba ya ciwo ko."?
Kalisa tai murmushi kawai
Umar da Jafar ne suka shigo a lokacin tare da sallama
" Ina kuka shiga ne haka tun safe."?
Baba anje ta fad'a bayan ta amsa sallamar
Umar ne ya fara magana yana kallon Kalisa cikin kauns
"Tun da har yau babu labarin Sahid a kan me zamu zauna to baba , mun fita neman kud'in da za a mata aiki , kuma a halin yanzu mun sami dubu dari biyar ."
Nabila ce ta ce "To yaya Jafar me zai hana mu siyar da gidan da muke ciki."
Jafar yayi ajiyar zuciya tare da cewa "Nabila komai fa yana hannun wannan azzalumin babu takardun gidan ."
Umar ya yi ajiyar zuciya
Kalisa ce cikin wata muryar tsananin wahala ta ce "Akwai takardun wani gidan momy da dady ya bata , nasan zamu sami kudaden da zasu isa idan aka siyar."
"Alhamdulillah Allah mun gode maka." Baba ta yi maganar
Jafar ya ce aiko ba wasa za a yi ba yau za a siyar dashi in sha Allah komai zai tafi daidai."
Umar ya ce "In sha Allah kuwa."
Kalisa ta kira Umar kusa da ita cikin kasa da murya ta ce "Ina matukar kaunar ka."
Koda yaji hakan sai ya ja da baya cikin tausayi da wasu hawaye a cikin idanunsa
Sannan ya dago ya kalleta ya ce "Ni ma ina kaunar ki Kalisa zaki samu lafiya in sha Allah."
Baba anje ta ce "Allah kai ne abin godiya, ka bawa Kalisa lafiya."
Nabila ta amsa da "Amenn." tare da sake cewa "A gaskiya ya kamata a sanar da baba Garba duk ba su san abin dake faruwa ba."
Baba anje ta ce "Gaskiya ne za a sanar dasu."
Sallama da aka yi ne ya sa duk hankulansu ya koma kan kofar
Mahaifan Sahid ne suka shigo
nan aka basu wajen zama zamansu ke nan Kalisa ta fara shure- shure
hakan ya tayar da hankalin kowa saida aka kira dactor Aisha
bayan ta zo ta mata abin da ya dace har ta samu bacci .
Cikin tashin hankali malam Aminu yake tambayar dactor "Yarinya meke damunta haka."
"Baba tana dauke da mummunan ciwo a cikinta, kuma kullum tsanani yake karawa , sannan da fari kasar waje za a kaita , amma a halin yanzu an sami asubitin da za mata aikin , kud'in ne ba su samu ba , kuma ni gaskiya babu abin da zan iya mata kawai aiki take bukata , sannan a gwajin da mukai dalilin accident din nan karfen da ya tsagata ta sami cancer., Amma in sha Allah da zarar an mata aiki komai mai wucewa ne ."
Bayan ta gama ta musu sallama ta fita
Malam Aminu ya ce "In sha Allah."
Umar ya yi ajiyar zuciya yana cewa da Jafar "Mu je a nemi dillalai wannan ba abin zama ba ne Jafar."
Jafar ya ce "To yaya Umar."
Ya tashi cikin kasala da matukar damuwar da yake ciki .
Kafin su kai ga hanyar fita wani saurayi ya shigo cikin d'akin tare da sallama, nan take malam Aminu ya shaida shi ya caf ki sunan shi
"Sani."
Saurayin ya amsa tare da gashshe shi , sannan ya kalli Jafar yana cewa "Don Allah ka yi hakuri tun shekaran jiya MD Sahid ya bani sako a company amma ban kawo ba na mance ."
Jafar har gida ya je neman Sahid sai dai tun jiya mahaifinsa ya tabbatar ba ya nan , sannan dukkan SMS din sa basa tafiya .
Ran malam Aminu ya yi matukar baci sosai dana mahaifiyarsa, musamman jin halin da Kalisa ke ciki ma ya tabbatar musu gobe zai zo garin ya ga jikin nata , kuma zai nemo Sahid din in sha Allah, Jafar jikinsa duk ba dadi ya koma asubitin.
Shugaban makaranta ne da Uncle Yahaya da bayis tare da wasu malamai biyu zaune a falonsu Laila.
Gefe guda kuma ga Laila da mahaifiyarta zaune ,ga kuma barrister Adam ran shi bace .
"Dan Allah barrister Adam ka duba wannan lamarin, mun yi kuskure sosai wanda a tarihin DR.DD ba a taba irin sa ba , amma a matsayin mu na masu ilmi mu yi sulhu dan Allah barrister." Shugaban makarantar ya aje maganar cikin tausayin kanshi .
Amma barrister Adam kamar sun sake fama masa ciwo haka ya fara magana.
"A she kuna da ilmin kuka aikata hakan , ni fa na gama magana kawai ku je ku nemi lauyan da zai tsaya muku , dan haka ku fitar mini a gida kawai."
Idanun shugaban makarantar ya ciko da ruwa ya kalli barrister yana cewa, "Wannan makaranta ita ce cigabana rufin asirina wallahi sunan ta zai baci barrister ka taimake ni."
Barrister tsaye ya tashi yana cewa "Ciwon zuciya ne ya sameta yanzu a kan ku , ta ya zan share wannan lamarin kamar ba kaunar ta nake ba ko ina jin tsoron ku."
Uncle Yahaya ya yi kasa da kai cikin jin haushin kansa.
Laila kuwa ganin yadda shugaban nasu Doctor Dauda ya shiga wani yanayi ya sa taji duk tausayinshi ya kamata, cikin sanyin murya Laila ta ce ,"Dady."!
Barrister Adam ya kalleta yayin da duk kowa ya maida hankali gare ta .
"Ni ce aka yi wa komai dady amma abin kai ne ya shafa , bani da wani farin ciki sama da kai, hakan ya sa wannan ciwon dole ya barni tun da ina tare da kai."
Tai ajiyar zuciya tana sake cewa "Ina matukar girmama shugaba kuma wannan tarbiyar ku ce
Duk abin da ya faru da kai wanda ba za ka taba mancewa dashi ba kuma idan ka tuna kanajin ciwonsa to wannan shi ne Gubar Rayuwarka."
Ta aje maganar tana kallon uncle Yahaya ,yayin da ya yi kasa da kanshi .
Mahaifinta ta kalla barrister Adam tana cewa "Dady dacter ba shi da laifi dan Allah ka janye karar."
Kowa ya kalleta cikin mamaki tare da sa'ke-sa'ke kala-kala da kowa ya ke yi a ransa.
Cikin wani Murmushin ta kaici barrister Adam ya ce "Babu ruwanki Laila wannan maganar kar na sake jinta a bakin ki , dole ne na dauki mataki, shin ko baki san wanne kalar jiwo suka jawo miki ba ne , ke ce kawai Allah ya bani kuma duk wanda ya yi kuskure irin wannan dole hankali na ya tashi idan ban dauki mataki ba Laila."
Cikin hawaye Laila ta tashi tsaye tana kallon barrister da dukkan girmamawa ta fara magana.
"Dady ni kaina nasan kana kaunata ,
amma wannan shi ne Gubar Rayuwata domin ba zan taba mancewa ba amma dan Allah dady ka janye karar."
Ta karasa maganar yayin da wasu hawaye suka zubo mata.
Hakan ya sa barrister Adam ya kalli Uncle Yahaya yana cewa .
Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
*AUTAR MARUBUTA CE*✍🏻👼🏻
🌹__________🌹_________🌹__________🌹_________🌹
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_🤲🏼
<><><🌹><><><>🌹<><><>🌹<><><><>🌹<><><><><>🌹<><>
Page 23 & 24
"Laila ina kaunar ta." Ya fad'awa Yahaya
sannan ya kalli doctor ya ce "Na janye karar tare da sharadin matukar Laila ta mutu sanadin wannan ciwon to akwai babban tashin hankali."
"Babu abin da zai samu Laila in sha Allah barrister, sannan na yi alkawarin duk in da magani yake zan ke nema mata har ta sami lafiya."
Shugaban ya yi maganar cikin tashin hankali da rawar murya
"Lafiya ta Allah ce kuma ni zan cigaba da nema mata magani , dan haka zaku iya tafiya nasan kun bar d'alubai a makaranta."
Barrister Adam yana gama maganar ya shige ciki .
Sannan suka yi sallama da Hajjiya da Laila suka fito
DR Dauda cikin fusata ya fito ranshi matukar bace suka dauki hanyar makaranta, babu wanda ya ce da kowa komai har suka isa makarantar
Suna shiga shugaba ya sa a fito assembly hakan ya sa wasu malaman mamaki da tunani
Bayan kowa ya fito suma malaman suka hallara
Kowa yana iya ganin 'bacin rai da damuwa a fuskar dactor,
Bai jira wani gabatar da abin da aka saba ba ya fara magana
"Wato duk kun debi zancen Laila kun yada a gari ta fadi ta kamu da ciwo , shi ke nan
ina jan kunnenku da duk yarinyar da wani malami ya ce yana sonta suka fara soyayya zamu dauki mummunan mataki wallahi a kan su."
Ya kalli Uncle Yahaya sannan ya ce " Daga yau mun sallami Yahaya a wannan makaranta, babu wanda zaike kawo mana farmaki ba mu dakatar dashi ba , idan kunne yaji ."
'Dalubai suka karasa masa maganar cikin murya mai karfi
Wani abu ne ya tirnike zuciyar uncle Yahaya da abin da shugaba ya yi masa .
Hakan ya sa bayan ya koma office ya je ya same shi
"Shugaba sallama ta fa kayi gaban d'alubai." Uncle Yahaya ya yi maganar cikin maraici
haka shi ma shugaba ya fara magana "Hukuncin da zan maka ke nan domin haka ne ya dace da kai , kuma kaji ka sani ko albashi ba zan biyaka ba , zan yi amfani dashi na gyara 'barnar da kamin cikin makaranta, fitar mini a office."
Uncle Yahaya ya fita cikin damuwa ya nufi gida .
koda yaje gidan ya ga ya masa duhu kakarshi ta bar masa duniya , babu wani hanyar samun kud'i da yake dashi yanzu, bare ya nemi matan da ya saba , duk yaji duniya ta masa zafi sosai .
Yana cikin wannan yanayin ne sai ga kiran Fa'iza ya shigo masa , ba tare da ya boye yanayin da yake ciki ba ya fara magana da ita .
Da baba anje da Nabila ne zaune a d'akin Kalisa dake asubiti,
a wannan lokacin ne baba ta kàlli Kalisa tana cewa "Yau dai Kalisa na ga jikin naki da sauki Allah ya dorar dashi."
Kalisa cikin zuciyar ta ta ayyana cewa "Kawai dauriya nake baba , amma Allah ne yasan abin da nake ji."
Nabila ce ta ce "Amma aunty Kalisa cikin ba ya ciwo ko."?
Kalisa tai murmushi kawai
Umar da Jafar ne suka shigo a lokacin tare da sallama
" Ina kuka shiga ne haka tun safe."?
Baba anje ta fad'a bayan ta amsa sallamar
Umar ne ya fara magana yana kallon Kalisa cikin kauns
"Tun da har yau babu labarin Sahid a kan me zamu zauna to baba , mun fita neman kud'in da za a mata aiki , kuma a halin yanzu mun sami dubu dari biyar ."
Nabila ce ta ce "To yaya Jafar me zai hana mu siyar da gidan da muke ciki."
Jafar yayi ajiyar zuciya tare da cewa "Nabila komai fa yana hannun wannan azzalumin babu takardun gidan ."
Umar ya yi ajiyar zuciya
Kalisa ce cikin wata muryar tsananin wahala ta ce "Akwai takardun wani gidan momy da dady ya bata , nasan zamu sami kudaden da zasu isa idan aka siyar."
"Alhamdulillah Allah mun gode maka." Baba ta yi maganar
Jafar ya ce aiko ba wasa za a yi ba yau za a siyar dashi in sha Allah komai zai tafi daidai."
Umar ya ce "In sha Allah kuwa."
Kalisa ta kira Umar kusa da ita cikin kasa da murya ta ce "Ina matukar kaunar ka."
Koda yaji hakan sai ya ja da baya cikin tausayi da wasu hawaye a cikin idanunsa
Sannan ya dago ya kalleta ya ce "Ni ma ina kaunar ki Kalisa zaki samu lafiya in sha Allah."
Baba anje ta ce "Allah kai ne abin godiya, ka bawa Kalisa lafiya."
Nabila ta amsa da "Amenn." tare da sake cewa "A gaskiya ya kamata a sanar da baba Garba duk ba su san abin dake faruwa ba."
Baba anje ta ce "Gaskiya ne za a sanar dasu."
Sallama da aka yi ne ya sa duk hankulansu ya koma kan kofar
Mahaifan Sahid ne suka shigo
nan aka basu wajen zama zamansu ke nan Kalisa ta fara shure- shure
hakan ya tayar da hankalin kowa saida aka kira dactor Aisha
bayan ta zo ta mata abin da ya dace har ta samu bacci .
Cikin tashin hankali malam Aminu yake tambayar dactor "Yarinya meke damunta haka."
"Baba tana dauke da mummunan ciwo a cikinta, kuma kullum tsanani yake karawa , sannan da fari kasar waje za a kaita , amma a halin yanzu an sami asubitin da za mata aikin , kud'in ne ba su samu ba , kuma ni gaskiya babu abin da zan iya mata kawai aiki take bukata , sannan a gwajin da mukai dalilin accident din nan karfen da ya tsagata ta sami cancer., Amma in sha Allah da zarar an mata aiki komai mai wucewa ne ."
Bayan ta gama ta musu sallama ta fita
Malam Aminu ya ce "In sha Allah."
Umar ya yi ajiyar zuciya yana cewa da Jafar "Mu je a nemi dillalai wannan ba abin zama ba ne Jafar."
Jafar ya ce "To yaya Umar."
Ya tashi cikin kasala da matukar damuwar da yake ciki .
Kafin su kai ga hanyar fita wani saurayi ya shigo cikin d'akin tare da sallama, nan take malam Aminu ya shaida shi ya caf ki sunan shi
"Sani."
Saurayin ya amsa tare da gashshe shi , sannan ya kalli Jafar yana cewa "Don Allah ka yi hakuri tun shekaran jiya MD Sahid ya bani sako a company amma ban kawo ba na mance ."