Sashe 14
Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Nasan duk abin da kike dan bamu sanar da dady ba ne , kuma wallahi yau sai ya san komai." Mahmud ya fada yana nuna Zainab da yatsa
"ka fada mana, ko tsoron hakan nake ka dameni ka ishi Rayuwata, kai azzalumi ne mara tausayi."
Wani saukar mari da taji a fuskarta ya sa tai shiru ta rike gurin , tana kallon Mahmud da mamakin ya mare ta .
Kafin ta ce komai taji muryar Harun yana cewa "Security ga shi nan."
Yana nunawa security na kula da gidan Mahmud.
Suka sashi gaba domin ya fita a gurin , kawai kallon Harun ya yi , ya wuce ya fita .
Share and comment...............................📚
Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
No editing
_______________________________________
*AUTAR MARUBUTA CE*✍🏻👼🏻
🌹__________🌹_________🌹__________🌹_________🌹
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_🤲🏼
<><><🌹><><><>🌹<><><>🌹<><><><>🌹<><><><><>🌹<><>
Page 29 & 30
Cikin mummunan 'bacin rai Mahmud ya fito , duk ya rasa mene yake masa dadi , kawai ya nufi gida kanshi tsaye , har ya isa gida yanayin shi bai canza ba , yana shiga falo ya ci karo da Alaji Kabiru shi da Ahmad suna zaune.
Yanayin yadda ya musu sallama a ciki ya sa suka tambayi mene yake faruwa .
Bai boyewa Alaji komai ba , haka shi ma Ahmad ya sake bada tabbacin abin da Mahmud ya fada .
Cikin bacin rai Alaji Kabiru ya kallesu yana cewa "Mutanen banza ku tashi Ku bani guri , duk kunsan da wannan baku fada mini ba saida abin ya kai haka ."
Ya karasa maganar lokacin da Hajjiya ta shigo ,
"A yi hakuri dady , mun yi zaton zata gyara ne ." Mahmud ya bada hakuri.
"Zaku bani guri ko sai na ci mutuncinku ."
Suka tashi ya yin da kafin su fita suna iya jin karashen maganar tasa
"Ta zo ta same ni , ina nan ina zaman jiranta ."...
LEGOS
Abokan Abdul Salim ne a d'akinshi suna ta shaye shayensu da bushe bushe .
Wani daga cikin su da ba ya iya magana sai ya karkata baki ya ce " Kai Abdul yarinyar nan taka fa , naji an ce ta aje kato a gidanta ."
Abdul na kokarin jan shisha ya ce "Ai na sani dan uwanta ne , ta fada mini komai."
"Kai dama baka da kishi ai koda yake ita karuwa ina ruwanta koma waye." Mari ya ji an d'auke shi dashi , yayin da duk abokan suka razana .
"Kar ka kuma kiran matar da zan aura karuwa, da yau a ce Fa'iza ba za ta aure ni ba , sai na wulakantata , amma tana sona, kar na sake ji ."
Kowa yasha jinin jikinshi, su abokanshi sun sani sarai ba sanshi take ba , amma sun bari duniya ta fada masa domin ba zai yadda dasu ba .
Uncle Yahaya dai asara ta tabbata , ba shi da abin yi , hatta kudin kashewa Fa'iza ke ba shi amma a haka suna shirin yin aure , ba tare da Abdul ya sani ba ,
Mu je zuwa Fa'iza zancen duniya ba ya buya.
ABUJA
Har yanzu sai dai saukin Allah, jikinta babu dadi Nabila ce rike da ita tana tsala kukan bakin ciki "Aunty Kalisa wallahi lafiyarki tafi komai a kan mene zaki bari a karbo ni , bayan bama da wasu kudaden , ke ce damuwarmu , amma yanzu bamu da wata dama." Rurutaccen kuka suke yi baki da yansu, sai dai abin da basu sani sani ba a halin yanzu Kalisa bata iya magana.
Tsanani ya kai ya wuce tunaninsu , ita kanta dactor Aisha tana mamakin yadda Kalisa ta kai har yanzu a raye, bayan tsananin da matakin da ciwonta ya haura.
"Likita , Likita likita ." Jafar da Nabila suka fita da gudu suna kiran dactor, wasu nurse ne su biyu suka shigo sukayi kan ita Kalisa data sassan kare , Umar ganin bai gamsu da nurse dinta ba fita neman doctor Aisha
da gaggawa Aisha ta taho gurin Kalisa, ya yin da taci karo da wannan nurse din su biyu , nan take suka ja baya suka bata guri .
"Baba Yaya Kalisa mutuwa za tai." Nabila ta yi maganar tana rushewa da kuka , baba anje bata iya cewa komai ba , domin a yadda take kallon Kalisa yanzu ita ma ta cire rai , domin a halin yanzu numfashi ya gagara ,
cikin kokari da sanin aiki na dactor Aisha aka sawa Kalisa oxygen machine
, wanda daga nan ne aka samu sauki ta koma kamar matacciya .
"A gaskiya ku dauketa ku koma gida , tunda har yau fitar da ita ya gagara , nasan halin da kuke ciki , amma hakan ba yana nufin ku zuba idanu ba , domin taya Allah kiyo yafi Allah na nan , ciwonta ya wuce duk yadda kuke tunani , musamman ma cancer dake kafarta wacce take cigaba da yawo."
Doctor Aisha ta yi maganar tana kallon kowanne a cikin su .
Ba tare data jira wani ya ce komai ba ta fita yayin da wannan nurses din suma suka fita da fatan samun lafiya .
Baba Garba ya kalli , baba anje yana cewa "Gaskiya ne wannan, duk abin da yake faruwa daga Allah ne , ya kamata mu tashi zuwa jibi a fitar da Kalisa a samo mata lafiya."
Baba anje dai ta kasa cewa komai, sai wani ajiyar zuciya da ta yi mai cike da fargaba tana kallon Kalisa.
"Zan je na sayar da gadon gidanmu , amma ba wani kud'i ba ne mai yawa." Umar ya yi maganar yana kallon Baba Garba
Baba Garba ya mayar masa da cewa "Ni ma yau zan tafi kauye, zan tattaro duk abin kadara ta da kiyo , a siyar dasu in sha Allah." Ya mike yana cewa
"Bari na tafi ba a bori da sanyin jiki , zan kuma tun-tu'bi duk mutanen kirki cikin 'yan uwa zasi wani abun."
Ya aje maganar lokacin da yakai kofar fita nan sukai masa sallama da fatan alheri
ajiyar zuciya Jafar ya yi tare da kallon can gefe guda idanunsa kamar zai yi kuka, sallamar da aka shigo ana yi ne ya sa ya dawo da kallon sa bakin kofa
"Ahh Jibril kai ne." Cewar Umar
Jibril ya gaida baba anje ,Wanda nan suma suka sami damar yi masa ta'aziyya
ya kalli Kalisa dake kwance da oxygen idanu a rufe yana cewa "Allah ya bata lafiya dan annabi."
Duk tare suka amsa da amin , wanda ya kalli Nabila yana sake cewa "Sannu ke ma Nabila, haka Allah yake kudurarsa , amma da wannan azzalumin Sahid ya bada kud'i n nan ai na tabbatar komai zai zo da sauki."
"Haka ne ." Jafar ya fada a takaice yana kallon Kalisa yayarshi wacce bata san inda kanta yake ba kwana guda babu abinci.
A lokacin Jibril ya kalli Jafar lokaci guda yana had'a kallo da baba anje yana cewa "Sahid jinin mu ne babu yadda muka iya , kuma bamu da bakin ba ku hakuri ku dauki duk matakin da ya dace dashi."
Ya ciro wasu
makudan kudade daga jikinshi yana ajiyewa gaban baba anje yana cewa "Wannan ku had'a ayi amfani dashi wajen lafiyarta amma babu yawa."
"Allah sarki, Allah ya saka muku da alheri." Baba anje ke nan
Jafar ya kai ido kan kudaden wanda kallo guda ya musu ya gane dubu dari biyu ne, Sannan shi ma ya mika godiya, shi ma Umar haka .........
Haka har wajen dare Kalisa jiki babu dadi , su ma Umar da Jafar a wannan dare suna ta kokarin samo wannan kud'i, haka bangaren baba garba kowa yana ta kokarin sa .
🌹Rayawa da kashewa duk na Allah ne, kuma duk yadda ya yi babu mai tuhuma , amma muna yiwa Kalisa fatan samun lafiya ta dawo kamar yadda take dah.🌹
Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
No editing
__ _____________________________________
*AUTAR MARUBUTA CE*✍🏻👼🏻
🌹__________🌹_________🌹__________🌹_________🌹
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_🤲🏼
<><><🌹><><><>🌹<><><>🌹<><><><>🌹<><><><><>🌹<><>
Page 31 & 32
A wannan daren Zainab ta ci matukar kuka , duk ranta babu dadi , domin Alaji Kabiru ya matukar taka mata burki ya mata abin da yake mata ciwo , babban abin da yake mata ciwo take yawan tunawa wai ita dady yau , ya mara ya kuma kirata da sha sha sha,
bugu da kari ya amshi wayarta duk saboda Mahmud, sannan aka yabi Mahmud , abin yana mata ciwo ta ci kuka har gari ya waye .
Da safiya ta yi , ta fito cikin lambun gidan nasu ko taji wani saukin ,
yadda ta ga Mahmud yana motsa jiki cikin lambun tare da kwanciyar hankali ya sa ta ji duk ta kuma tsanar shi.
"Hankalin ka ya kwanta ." Ta yi maganar lokacin data sha gabanshi
Mahmud dakatawa ya yi yana fuskantarta, wanda wannan lokacin ne da ya dubi idanunta ya san taci matukar kuka, amma ba tare da ya bayyana mata ya gane ba ya fara cewa "Eh kam na ji dadi , tun da yanzu bakya cikin hadari irin na Harun." Ya karasa maganar yana korawa da ruwan jarkar dake hannunshi .
Wata sabuwar 'kufula Zainab ttaa sake yi da jin hakan "Ka rabani da farin cikina , kasa dady ya mareni , kasa yayana Ahmad ya dena kulani , wallahi kai masifa ne , dan Allah ka koma garin ku kai ma ka yi rayuwarka haba ." Cikin bacin rai Zainab ta karasa maganar
Mutuwar tsaye ya yi shi kuwa Mahmud, mamaki ya cikashi da jin wannan zance na Zainab,
komai yaji ya sire masa , wai shi ne masifa
"Zainab na yi miki gata .Amma sam ba za ki gane hakan ba yanzu, ni yayanki ne , ko ba komai ban can can ci wannan kalaman naki ba ." Bai jira komai daga gareta ba , domin shi ma ba iya abin dake bakinsa ba ke nan , amma ya wuce ya tafi, ya barta a gun , .
"ka fada mana, ko tsoron hakan nake ka dameni ka ishi Rayuwata, kai azzalumi ne mara tausayi."
Wani saukar mari da taji a fuskarta ya sa tai shiru ta rike gurin , tana kallon Mahmud da mamakin ya mare ta .
Kafin ta ce komai taji muryar Harun yana cewa "Security ga shi nan."
Yana nunawa security na kula da gidan Mahmud.
Suka sashi gaba domin ya fita a gurin , kawai kallon Harun ya yi , ya wuce ya fita .
Share and comment...............................📚
Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
No editing
_______________________________________
*AUTAR MARUBUTA CE*✍🏻👼🏻
🌹__________🌹_________🌹__________🌹_________🌹
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_🤲🏼
<><><🌹><><><>🌹<><><>🌹<><><><>🌹<><><><><>🌹<><>
Page 29 & 30
Cikin mummunan 'bacin rai Mahmud ya fito , duk ya rasa mene yake masa dadi , kawai ya nufi gida kanshi tsaye , har ya isa gida yanayin shi bai canza ba , yana shiga falo ya ci karo da Alaji Kabiru shi da Ahmad suna zaune.
Yanayin yadda ya musu sallama a ciki ya sa suka tambayi mene yake faruwa .
Bai boyewa Alaji komai ba , haka shi ma Ahmad ya sake bada tabbacin abin da Mahmud ya fada .
Cikin bacin rai Alaji Kabiru ya kallesu yana cewa "Mutanen banza ku tashi Ku bani guri , duk kunsan da wannan baku fada mini ba saida abin ya kai haka ."
Ya karasa maganar lokacin da Hajjiya ta shigo ,
"A yi hakuri dady , mun yi zaton zata gyara ne ." Mahmud ya bada hakuri.
"Zaku bani guri ko sai na ci mutuncinku ."
Suka tashi ya yin da kafin su fita suna iya jin karashen maganar tasa
"Ta zo ta same ni , ina nan ina zaman jiranta ."...
LEGOS
Abokan Abdul Salim ne a d'akinshi suna ta shaye shayensu da bushe bushe .
Wani daga cikin su da ba ya iya magana sai ya karkata baki ya ce " Kai Abdul yarinyar nan taka fa , naji an ce ta aje kato a gidanta ."
Abdul na kokarin jan shisha ya ce "Ai na sani dan uwanta ne , ta fada mini komai."
"Kai dama baka da kishi ai koda yake ita karuwa ina ruwanta koma waye." Mari ya ji an d'auke shi dashi , yayin da duk abokan suka razana .
"Kar ka kuma kiran matar da zan aura karuwa, da yau a ce Fa'iza ba za ta aure ni ba , sai na wulakantata , amma tana sona, kar na sake ji ."
Kowa yasha jinin jikinshi, su abokanshi sun sani sarai ba sanshi take ba , amma sun bari duniya ta fada masa domin ba zai yadda dasu ba .
Uncle Yahaya dai asara ta tabbata , ba shi da abin yi , hatta kudin kashewa Fa'iza ke ba shi amma a haka suna shirin yin aure , ba tare da Abdul ya sani ba ,
Mu je zuwa Fa'iza zancen duniya ba ya buya.
ABUJA
Har yanzu sai dai saukin Allah, jikinta babu dadi Nabila ce rike da ita tana tsala kukan bakin ciki "Aunty Kalisa wallahi lafiyarki tafi komai a kan mene zaki bari a karbo ni , bayan bama da wasu kudaden , ke ce damuwarmu , amma yanzu bamu da wata dama." Rurutaccen kuka suke yi baki da yansu, sai dai abin da basu sani sani ba a halin yanzu Kalisa bata iya magana.
Tsanani ya kai ya wuce tunaninsu , ita kanta dactor Aisha tana mamakin yadda Kalisa ta kai har yanzu a raye, bayan tsananin da matakin da ciwonta ya haura.
"Likita , Likita likita ." Jafar da Nabila suka fita da gudu suna kiran dactor, wasu nurse ne su biyu suka shigo sukayi kan ita Kalisa data sassan kare , Umar ganin bai gamsu da nurse dinta ba fita neman doctor Aisha
da gaggawa Aisha ta taho gurin Kalisa, ya yin da taci karo da wannan nurse din su biyu , nan take suka ja baya suka bata guri .
"Baba Yaya Kalisa mutuwa za tai." Nabila ta yi maganar tana rushewa da kuka , baba anje bata iya cewa komai ba , domin a yadda take kallon Kalisa yanzu ita ma ta cire rai , domin a halin yanzu numfashi ya gagara ,
cikin kokari da sanin aiki na dactor Aisha aka sawa Kalisa oxygen machine
, wanda daga nan ne aka samu sauki ta koma kamar matacciya .
"A gaskiya ku dauketa ku koma gida , tunda har yau fitar da ita ya gagara , nasan halin da kuke ciki , amma hakan ba yana nufin ku zuba idanu ba , domin taya Allah kiyo yafi Allah na nan , ciwonta ya wuce duk yadda kuke tunani , musamman ma cancer dake kafarta wacce take cigaba da yawo."
Doctor Aisha ta yi maganar tana kallon kowanne a cikin su .
Ba tare data jira wani ya ce komai ba ta fita yayin da wannan nurses din suma suka fita da fatan samun lafiya .
Baba Garba ya kalli , baba anje yana cewa "Gaskiya ne wannan, duk abin da yake faruwa daga Allah ne , ya kamata mu tashi zuwa jibi a fitar da Kalisa a samo mata lafiya."
Baba anje dai ta kasa cewa komai, sai wani ajiyar zuciya da ta yi mai cike da fargaba tana kallon Kalisa.
"Zan je na sayar da gadon gidanmu , amma ba wani kud'i ba ne mai yawa." Umar ya yi maganar yana kallon Baba Garba
Baba Garba ya mayar masa da cewa "Ni ma yau zan tafi kauye, zan tattaro duk abin kadara ta da kiyo , a siyar dasu in sha Allah." Ya mike yana cewa
"Bari na tafi ba a bori da sanyin jiki , zan kuma tun-tu'bi duk mutanen kirki cikin 'yan uwa zasi wani abun."
Ya aje maganar lokacin da yakai kofar fita nan sukai masa sallama da fatan alheri
ajiyar zuciya Jafar ya yi tare da kallon can gefe guda idanunsa kamar zai yi kuka, sallamar da aka shigo ana yi ne ya sa ya dawo da kallon sa bakin kofa
"Ahh Jibril kai ne." Cewar Umar
Jibril ya gaida baba anje ,Wanda nan suma suka sami damar yi masa ta'aziyya
ya kalli Kalisa dake kwance da oxygen idanu a rufe yana cewa "Allah ya bata lafiya dan annabi."
Duk tare suka amsa da amin , wanda ya kalli Nabila yana sake cewa "Sannu ke ma Nabila, haka Allah yake kudurarsa , amma da wannan azzalumin Sahid ya bada kud'i n nan ai na tabbatar komai zai zo da sauki."
"Haka ne ." Jafar ya fada a takaice yana kallon Kalisa yayarshi wacce bata san inda kanta yake ba kwana guda babu abinci.
A lokacin Jibril ya kalli Jafar lokaci guda yana had'a kallo da baba anje yana cewa "Sahid jinin mu ne babu yadda muka iya , kuma bamu da bakin ba ku hakuri ku dauki duk matakin da ya dace dashi."
Ya ciro wasu
makudan kudade daga jikinshi yana ajiyewa gaban baba anje yana cewa "Wannan ku had'a ayi amfani dashi wajen lafiyarta amma babu yawa."
"Allah sarki, Allah ya saka muku da alheri." Baba anje ke nan
Jafar ya kai ido kan kudaden wanda kallo guda ya musu ya gane dubu dari biyu ne, Sannan shi ma ya mika godiya, shi ma Umar haka .........
Haka har wajen dare Kalisa jiki babu dadi , su ma Umar da Jafar a wannan dare suna ta kokarin samo wannan kud'i, haka bangaren baba garba kowa yana ta kokarin sa .
🌹Rayawa da kashewa duk na Allah ne, kuma duk yadda ya yi babu mai tuhuma , amma muna yiwa Kalisa fatan samun lafiya ta dawo kamar yadda take dah.🌹
Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
No editing
__ _____________________________________
*AUTAR MARUBUTA CE*✍🏻👼🏻
🌹__________🌹_________🌹__________🌹_________🌹
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_🤲🏼
<><><🌹><><><>🌹<><><>🌹<><><><>🌹<><><><><>🌹<><>
Page 31 & 32
A wannan daren Zainab ta ci matukar kuka , duk ranta babu dadi , domin Alaji Kabiru ya matukar taka mata burki ya mata abin da yake mata ciwo , babban abin da yake mata ciwo take yawan tunawa wai ita dady yau , ya mara ya kuma kirata da sha sha sha,
bugu da kari ya amshi wayarta duk saboda Mahmud, sannan aka yabi Mahmud , abin yana mata ciwo ta ci kuka har gari ya waye .
Da safiya ta yi , ta fito cikin lambun gidan nasu ko taji wani saukin ,
yadda ta ga Mahmud yana motsa jiki cikin lambun tare da kwanciyar hankali ya sa ta ji duk ta kuma tsanar shi.
"Hankalin ka ya kwanta ." Ta yi maganar lokacin data sha gabanshi
Mahmud dakatawa ya yi yana fuskantarta, wanda wannan lokacin ne da ya dubi idanunta ya san taci matukar kuka, amma ba tare da ya bayyana mata ya gane ba ya fara cewa "Eh kam na ji dadi , tun da yanzu bakya cikin hadari irin na Harun." Ya karasa maganar yana korawa da ruwan jarkar dake hannunshi .
Wata sabuwar 'kufula Zainab ttaa sake yi da jin hakan "Ka rabani da farin cikina , kasa dady ya mareni , kasa yayana Ahmad ya dena kulani , wallahi kai masifa ne , dan Allah ka koma garin ku kai ma ka yi rayuwarka haba ." Cikin bacin rai Zainab ta karasa maganar
Mutuwar tsaye ya yi shi kuwa Mahmud, mamaki ya cikashi da jin wannan zance na Zainab,
komai yaji ya sire masa , wai shi ne masifa
"Zainab na yi miki gata .Amma sam ba za ki gane hakan ba yanzu, ni yayanki ne , ko ba komai ban can can ci wannan kalaman naki ba ." Bai jira komai daga gareta ba , domin shi ma ba iya abin dake bakinsa ba ke nan , amma ya wuce ya tafi, ya barta a gun , .