Sashe 13
Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gubar Rayuwata⚡🌹
By
Fatima Abdallaah kano
. (Autar marubuta)
______________________________________
*AUTAR MARUBUTA CE*✍🏻👼🏻
🌹__________🌹_________🌹__________🌹_________🌹
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_🤲🏼
<><><🌹><><><>🌹<><><>🌹<><><><>🌹<><><><><>🌹<><>
Page 27 & 28
Duk hankalinsu ya gama tashi matukar gaske, har magariba ta yi amma babu labarin Nabila , da tananan sun tabbatar yanzu Kalisa tana India, amma duk inda ya dace a duba kuma a tambaya an yi , sai dai babu wani cigaba.
Allah ya kawo sauki da mafita , haka rayuwar take, kowa da kalar tashi kaddarar.
Washe gari
Jibril ne zaune kusa da mahaifiyar shi yana rarrashinta , tun da garin Allah ya waye take kuka
Cikin tausayin mahaifiyar tashi Jibril ya ce "Babata dan Allah ki jure wannan jarabawar , wallahi komai mai wucewa ne ."
Cikin rashin gwarin gwiwa ya karasa maganar
Cikin kuka tana face majina tana gogewa da zaninta ta ce "Wallahi Jibril kaninka ya yi asara duniya d lahira , domin ba zan yafe masa, ya je indai duniya ce , wanda ba su zo ba ma jiransu take , sai ta sashi kukan da babu hankicin da zai share masa."😭
Ta kuma fashewa da kuka
Jibril duk ya kasa cewa komai domin zuciyar shi shi daya yasan zugin da take masa .
Kasar waje
Sahid ne ya fito daga asubitin kashi yana dingishi , guri ya samu ya zauna
iska mai dadin gaske ce ke kai wa tana dawowa , ga duk kan alamu yana jin dadinta fiye da su mazauna kasar
Lokaci guda kuma ya hade rai yana magana shi daya , yayin da ya hango wani gurgu bisa keke ana turashi
" Allah ka raba mu da wannan masifar kawai a yankewa mutum kafarsa ,
wannan asubitin za su min komai ba sai na koma Nigeria ba , Allah sarki babata da na ce ciwo zata daukon magani ,
ni da na koma Nigeria sai na yi aure na haihu da baturiya ,daga nan ma Pakistan zan wuce."
Ya aje maganar yana kallon ambulance din da suka shigo asubitin.
A d'azu jikin Kalisa ya rikice sosai da sosai , nan hankalinsu ya tashi
sun yi kokarin fitar da ita , amma Kalisa ta ce bazata bar kasar nan ba ba tare da tasan halin da kanwarta ke ciki ba .
Duk da an sanar da 'yan sanda amma har yanzu ba ta sauya zani ba
Fitar kannen Umar ke nan daga asubitin , su biyu mace dana miji
macen tana kuka da wannan yanayi data gansu a ciki. To ya za ai da lamarin ubangiji
Umar ya matukar ramewa sosai , su baba anje ma ba a cewa komai ga su Jafar da Garba , abin dai sai wanda ya gani.
Jingum suka yi duk din su a dakin
wayar Jafar da take ruri ne kawai ya sa ake jin wani sauti
da kasala ya cirota a aljihunsa tare d amsa kiran yana karawa a kunne .
Koda jin wata kakkausar murya ce ke magana hakan ya sa ya tashi tsaye , yayin da duk hankulansu suka dawo wajenshi
Da alamar magana da kai Umar yake tambaya ko lafiya, hakan ya sa Jafar ya sata a sautin da kowa kan iya jin abin da ake cewa
"Na ce kai ne Jafar."
Aka fad'a cikin muryar rashin girmamawa, cikin faduwar gaba Jafar ya amsa da shi ne
Aka ci gaba da magana kamar haka "To wallahi mu harkar mu babu karanta , da zarar mun baka lokaci ba kai amfani da shi ba komai na faruwa, mu ne muka dauke kanwarka , kud'in fansa muke so , idan kuma ka shigo da 'yan sanda cikin kasuwancin mu to ku shirya jana'izarta."
Yana gama maganar ya kashe wayar
Tare da dukkan tashin hankali da matukar hanzari duk suka tashi , su baba anje da Garba tare da salati suna kiran sunan Allah suka tashi .
Kalisa ma kana iya hangen mummunan tashin hankali a kan idanunta, cikin tsananin ciwo da fargaba tare da tashin hankali gami da juriya ta fara magana.
"Mun shiga uku Jafar , ka dubi rayuwar data riskemu a bayansu momy, Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un."
Ta karasa maganar cikin ciwo tana Ajiyar zuciya tare da hawaye .
Yadda Umar ya kalli masoyiyarshi Kalisa duk wani tausayin ta ya kama shi , duk da bata da lafiya sannan ga baba anje ga Garba, amma tana daukar lamarin 'yan uwanta a kanta .Matsawa ya yi kusa da ita a sa'ilin da yake jin kamar ya sa hannu ya goge hawayen dake gangaro mata kana ya rungumeta ya rarrasheta .
Amma ina duk ya kasa ma cewa da ita komai ya juya ya fita.
Tun da lamarin ya faru babu wanda ya yi wani yunkuri , domin yadda Kalisa ta damu da lamarin Nabila duk abin sai ya sake d'aga musu hankali.
Babu inda kowa ya motsa har dare ya yi , idan ka ga wani a cikinsu ya fita ,to bai wuce ya nuna damuwar shi a waje ba , sannan ya dawo , domin duk dakon kiran kidnappers din suke .
Ai kuwa wajen karfe goman dare , sai ga wata sabuwar number ana kiran Jafar, hakan ya sa duk suka mayar da hankali ga kiran, sannan Garba ya ce ya saka a speaker.
"Kana jina." Ha kan da aka fad'a ya tabbatar musu muryar wannan azzalumin ce ta d'azu
Cikin rawar murya Jafar ya ce "Ina jin ka."
"Zuwa gobe na baku, da karfe 4 na yamma, idan baku amsheta ba , zamu hada ta cikin masu bakuntar lahira gobe , Million 3 za ku aiko."
Ya kashe wayar daga can bangaren .
"Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un, yanzu ya zami , kud'in aikin Kalisa ne kawai damu bayan fafutukar da akai aka had'a su , ina zamu sa kanmu 😭
Yanzu da Sahid ya bamu kud'i ko million dari ce ai ba wahala za tai fa."
Baba anje ta yi maganar tana rushewa da kuka .
"Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un." Garba ya fad'a yana samun guri ya zauna
Cikin rawar murya tare da fargabar abubuwan da suke faruwa Jafar ya ce "Dole a fitar da Kalisa baba Garba, tun da wannan kudin...."
Kalisa ce ta dakatar da Jafar cikin ciwo tana cewa "Babu inda zani sai Nabila ta dawo , dukkan abin da aka tara dan zuwa neman lafiya ta ,a halin yanzu Nabila ce mabukaci , ita jini na ce ,dan haka kawai ku karbota Jafar." Ta aje maganar tana wani irin nishi .
Baba anje kuka ta sake fashewa dashi tana neman taimakon Allah.
Baba Garba ma ya kasa cewa komai ,
KANO
Mahmud ne a zaune a falo kamar kullum, cikin zuciyar shi ya fara tunanin ya kamata ya koma gida, domin wani abokin sa ya tabbatar masa aikin da suka nema koyaushe za a iya kiransu .
Zainab ce dake kwas kwas kwas da takalmi ta dawo dashi cikin hayyacinsa .ko kallon inda yake bata yi ba ta wuce ta gabanshi .
Ganin suturar dake jikinta ya tabbatar masa fita za tai
zama ya gyara yayin da ta kai bakin kofa tana kokarin budewa ya ce "Ina zuwa."?
Wani zafin takaici ta ji a ranta " Zan je gidansu wata ne , kuma momy ta sani , ba sai ka tuhume ni ba."
Duk jikin Mahmud wani iri ya masa domin ya tabbatar Zainab ba gaskiya ta fad'a masa ba , wajen Harun zata ,haka zuciyar shi ta ba shi.
"A dawo lafiya". Abin da ya fada ke nan ya koma ya yi lakaf kamar ya saduda .
Hakan ya sa Zainab ta fita
Zumbur ya yi ya tashi kamar wanda aka tsikara ya zura wayarshi a aljihu ya fita ya bi bayanta.
Yana binta a baya- a baya har tasha kwana ta nufi bayan gidansu , wanda hakan ya tabbatar wa da Mahmud abin da yake tunani, tana tsallaka titi ya ga ta doshi wani babban gidan abinci da hutawa mai suna Shuwa Love , mamaki ne ya sake rufe shi ya ci gaba da binta , wanda harta shiga ciki bata san yana bibiyarta ba .
Sahun kujera number ta goma sha bakwai ta hangi Harun yana zaune yana jiranta, hakan ya sa ta nufi wajen shi cikin farin ciki.
" Ohh Zainab! Wajen wannan wawan kika sake zuwa ya Allah. " Ya yi maganar cikin tsananin haushi da bacin rai .
Daga inda yake labe yake hangosu ya kalli hagu da damar sa , sannan ya nufi inda suke
Zainab wani yarrrr take ji duba da yadda Harun yake kallonta kamar mai shirin fada mata kah yana daga zaune
"Masoyi wannan wanne irin kallo ne."?
Zainab ta tambayi Harun cikin ya'ke tare da murmushi wanda lokaci guda zaka gane duk hankalinta bai kwanta da kallon ba .
Ajiyar zuciya ya yi yana kokarin fara magana , sai dai kafin ya kai ga cewa komai
Mahmud ya tsaya 'kyem a kansu rike da kugunsa
Duk mikewa tsaye sukai suna kallonshi , ba tare da ya bari wani a cikinsu ya ce komai ba , ya fara magana "Sannu ku, ashe nan kika taho."
Tare da duk bacin rai Zainab ta fara magana"Wato bibiya ta kake , amma wallahi ka bani kunya , wannan wacce irin. "..
" Shiru mara kunya." Mahmud ya fada cikin zafi da hassala, ni yayanki ne , amma ni kike fadawa wannan maganganun , saboda duk kin ga na zama wani zato .
Rashin hankalinki ya wuce tunanina , kwakwalwarki ta dena aiki , kin zabi mutumin da yake da burin kashe ni ."
Sauri Harun ya yi ya tari numfashin Mahmud, wanda a wannan lokaci duk mutanen dake zaune a wajen hankalinsu yana wajensu suna ji da kallon hayaniyar tasu .
"Ta ya zan kashe ka Mahmud, ai ko ba komai kai abokina ne kuma yayan Zainab, ka dena min kazafi dan baka so na ." Ya yi maganar cikin muryar tausayi da marairaicewa .
Hakan ne ya matukar hassala Mahmud, cikin fusata ya yi sauri ya daki kirjin Harun da hannu biyunsa , wanda sai da ya kai kasa
har kasan rigarshi ya yage , sakamakon kujerar da ya bige ta rike shi .
By
Fatima Abdallaah kano
. (Autar marubuta)
______________________________________
*AUTAR MARUBUTA CE*✍🏻👼🏻
🌹__________🌹_________🌹__________🌹_________🌹
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_🤲🏼
<><><🌹><><><>🌹<><><>🌹<><><><>🌹<><><><><>🌹<><>
Page 27 & 28
Duk hankalinsu ya gama tashi matukar gaske, har magariba ta yi amma babu labarin Nabila , da tananan sun tabbatar yanzu Kalisa tana India, amma duk inda ya dace a duba kuma a tambaya an yi , sai dai babu wani cigaba.
Allah ya kawo sauki da mafita , haka rayuwar take, kowa da kalar tashi kaddarar.
Washe gari
Jibril ne zaune kusa da mahaifiyar shi yana rarrashinta , tun da garin Allah ya waye take kuka
Cikin tausayin mahaifiyar tashi Jibril ya ce "Babata dan Allah ki jure wannan jarabawar , wallahi komai mai wucewa ne ."
Cikin rashin gwarin gwiwa ya karasa maganar
Cikin kuka tana face majina tana gogewa da zaninta ta ce "Wallahi Jibril kaninka ya yi asara duniya d lahira , domin ba zan yafe masa, ya je indai duniya ce , wanda ba su zo ba ma jiransu take , sai ta sashi kukan da babu hankicin da zai share masa."😭
Ta kuma fashewa da kuka
Jibril duk ya kasa cewa komai domin zuciyar shi shi daya yasan zugin da take masa .
Kasar waje
Sahid ne ya fito daga asubitin kashi yana dingishi , guri ya samu ya zauna
iska mai dadin gaske ce ke kai wa tana dawowa , ga duk kan alamu yana jin dadinta fiye da su mazauna kasar
Lokaci guda kuma ya hade rai yana magana shi daya , yayin da ya hango wani gurgu bisa keke ana turashi
" Allah ka raba mu da wannan masifar kawai a yankewa mutum kafarsa ,
wannan asubitin za su min komai ba sai na koma Nigeria ba , Allah sarki babata da na ce ciwo zata daukon magani ,
ni da na koma Nigeria sai na yi aure na haihu da baturiya ,daga nan ma Pakistan zan wuce."
Ya aje maganar yana kallon ambulance din da suka shigo asubitin.
A d'azu jikin Kalisa ya rikice sosai da sosai , nan hankalinsu ya tashi
sun yi kokarin fitar da ita , amma Kalisa ta ce bazata bar kasar nan ba ba tare da tasan halin da kanwarta ke ciki ba .
Duk da an sanar da 'yan sanda amma har yanzu ba ta sauya zani ba
Fitar kannen Umar ke nan daga asubitin , su biyu mace dana miji
macen tana kuka da wannan yanayi data gansu a ciki. To ya za ai da lamarin ubangiji
Umar ya matukar ramewa sosai , su baba anje ma ba a cewa komai ga su Jafar da Garba , abin dai sai wanda ya gani.
Jingum suka yi duk din su a dakin
wayar Jafar da take ruri ne kawai ya sa ake jin wani sauti
da kasala ya cirota a aljihunsa tare d amsa kiran yana karawa a kunne .
Koda jin wata kakkausar murya ce ke magana hakan ya sa ya tashi tsaye , yayin da duk hankulansu suka dawo wajenshi
Da alamar magana da kai Umar yake tambaya ko lafiya, hakan ya sa Jafar ya sata a sautin da kowa kan iya jin abin da ake cewa
"Na ce kai ne Jafar."
Aka fad'a cikin muryar rashin girmamawa, cikin faduwar gaba Jafar ya amsa da shi ne
Aka ci gaba da magana kamar haka "To wallahi mu harkar mu babu karanta , da zarar mun baka lokaci ba kai amfani da shi ba komai na faruwa, mu ne muka dauke kanwarka , kud'in fansa muke so , idan kuma ka shigo da 'yan sanda cikin kasuwancin mu to ku shirya jana'izarta."
Yana gama maganar ya kashe wayar
Tare da dukkan tashin hankali da matukar hanzari duk suka tashi , su baba anje da Garba tare da salati suna kiran sunan Allah suka tashi .
Kalisa ma kana iya hangen mummunan tashin hankali a kan idanunta, cikin tsananin ciwo da fargaba tare da tashin hankali gami da juriya ta fara magana.
"Mun shiga uku Jafar , ka dubi rayuwar data riskemu a bayansu momy, Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un."
Ta karasa maganar cikin ciwo tana Ajiyar zuciya tare da hawaye .
Yadda Umar ya kalli masoyiyarshi Kalisa duk wani tausayin ta ya kama shi , duk da bata da lafiya sannan ga baba anje ga Garba, amma tana daukar lamarin 'yan uwanta a kanta .Matsawa ya yi kusa da ita a sa'ilin da yake jin kamar ya sa hannu ya goge hawayen dake gangaro mata kana ya rungumeta ya rarrasheta .
Amma ina duk ya kasa ma cewa da ita komai ya juya ya fita.
Tun da lamarin ya faru babu wanda ya yi wani yunkuri , domin yadda Kalisa ta damu da lamarin Nabila duk abin sai ya sake d'aga musu hankali.
Babu inda kowa ya motsa har dare ya yi , idan ka ga wani a cikinsu ya fita ,to bai wuce ya nuna damuwar shi a waje ba , sannan ya dawo , domin duk dakon kiran kidnappers din suke .
Ai kuwa wajen karfe goman dare , sai ga wata sabuwar number ana kiran Jafar, hakan ya sa duk suka mayar da hankali ga kiran, sannan Garba ya ce ya saka a speaker.
"Kana jina." Ha kan da aka fad'a ya tabbatar musu muryar wannan azzalumin ce ta d'azu
Cikin rawar murya Jafar ya ce "Ina jin ka."
"Zuwa gobe na baku, da karfe 4 na yamma, idan baku amsheta ba , zamu hada ta cikin masu bakuntar lahira gobe , Million 3 za ku aiko."
Ya kashe wayar daga can bangaren .
"Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un, yanzu ya zami , kud'in aikin Kalisa ne kawai damu bayan fafutukar da akai aka had'a su , ina zamu sa kanmu 😭
Yanzu da Sahid ya bamu kud'i ko million dari ce ai ba wahala za tai fa."
Baba anje ta yi maganar tana rushewa da kuka .
"Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un." Garba ya fad'a yana samun guri ya zauna
Cikin rawar murya tare da fargabar abubuwan da suke faruwa Jafar ya ce "Dole a fitar da Kalisa baba Garba, tun da wannan kudin...."
Kalisa ce ta dakatar da Jafar cikin ciwo tana cewa "Babu inda zani sai Nabila ta dawo , dukkan abin da aka tara dan zuwa neman lafiya ta ,a halin yanzu Nabila ce mabukaci , ita jini na ce ,dan haka kawai ku karbota Jafar." Ta aje maganar tana wani irin nishi .
Baba anje kuka ta sake fashewa dashi tana neman taimakon Allah.
Baba Garba ma ya kasa cewa komai ,
KANO
Mahmud ne a zaune a falo kamar kullum, cikin zuciyar shi ya fara tunanin ya kamata ya koma gida, domin wani abokin sa ya tabbatar masa aikin da suka nema koyaushe za a iya kiransu .
Zainab ce dake kwas kwas kwas da takalmi ta dawo dashi cikin hayyacinsa .ko kallon inda yake bata yi ba ta wuce ta gabanshi .
Ganin suturar dake jikinta ya tabbatar masa fita za tai
zama ya gyara yayin da ta kai bakin kofa tana kokarin budewa ya ce "Ina zuwa."?
Wani zafin takaici ta ji a ranta " Zan je gidansu wata ne , kuma momy ta sani , ba sai ka tuhume ni ba."
Duk jikin Mahmud wani iri ya masa domin ya tabbatar Zainab ba gaskiya ta fad'a masa ba , wajen Harun zata ,haka zuciyar shi ta ba shi.
"A dawo lafiya". Abin da ya fada ke nan ya koma ya yi lakaf kamar ya saduda .
Hakan ya sa Zainab ta fita
Zumbur ya yi ya tashi kamar wanda aka tsikara ya zura wayarshi a aljihu ya fita ya bi bayanta.
Yana binta a baya- a baya har tasha kwana ta nufi bayan gidansu , wanda hakan ya tabbatar wa da Mahmud abin da yake tunani, tana tsallaka titi ya ga ta doshi wani babban gidan abinci da hutawa mai suna Shuwa Love , mamaki ne ya sake rufe shi ya ci gaba da binta , wanda harta shiga ciki bata san yana bibiyarta ba .
Sahun kujera number ta goma sha bakwai ta hangi Harun yana zaune yana jiranta, hakan ya sa ta nufi wajen shi cikin farin ciki.
" Ohh Zainab! Wajen wannan wawan kika sake zuwa ya Allah. " Ya yi maganar cikin tsananin haushi da bacin rai .
Daga inda yake labe yake hangosu ya kalli hagu da damar sa , sannan ya nufi inda suke
Zainab wani yarrrr take ji duba da yadda Harun yake kallonta kamar mai shirin fada mata kah yana daga zaune
"Masoyi wannan wanne irin kallo ne."?
Zainab ta tambayi Harun cikin ya'ke tare da murmushi wanda lokaci guda zaka gane duk hankalinta bai kwanta da kallon ba .
Ajiyar zuciya ya yi yana kokarin fara magana , sai dai kafin ya kai ga cewa komai
Mahmud ya tsaya 'kyem a kansu rike da kugunsa
Duk mikewa tsaye sukai suna kallonshi , ba tare da ya bari wani a cikinsu ya ce komai ba , ya fara magana "Sannu ku, ashe nan kika taho."
Tare da duk bacin rai Zainab ta fara magana"Wato bibiya ta kake , amma wallahi ka bani kunya , wannan wacce irin. "..
" Shiru mara kunya." Mahmud ya fada cikin zafi da hassala, ni yayanki ne , amma ni kike fadawa wannan maganganun , saboda duk kin ga na zama wani zato .
Rashin hankalinki ya wuce tunanina , kwakwalwarki ta dena aiki , kin zabi mutumin da yake da burin kashe ni ."
Sauri Harun ya yi ya tari numfashin Mahmud, wanda a wannan lokaci duk mutanen dake zaune a wajen hankalinsu yana wajensu suna ji da kallon hayaniyar tasu .
"Ta ya zan kashe ka Mahmud, ai ko ba komai kai abokina ne kuma yayan Zainab, ka dena min kazafi dan baka so na ." Ya yi maganar cikin muryar tausayi da marairaicewa .
Hakan ne ya matukar hassala Mahmud, cikin fusata ya yi sauri ya daki kirjin Harun da hannu biyunsa , wanda sai da ya kai kasa
har kasan rigarshi ya yage , sakamakon kujerar da ya bige ta rike shi .