← Book details Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 22

Sashe 10

Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dacter ya dago kai yana magana cikin tsafi ,"To yanzu mene mafitar."
Yanayin yadda ya yi maganar suka sha jinin jikinsu , musamman ma Uncle Yahaya.

Tafiya suke cikin mota , Umar yana tu'ka su
kallon Kalisa ya yi yana cewa, "Ki ce dai gidan nasu da nisa. ga shi kauye, to ina zai aje min ke saboda rashin kunya."

Dariya Kalisa tai tana cewa, "Wallahi kuwa da nisa."
Umar ya yi tsaki yana cewa "Ai wallahi ya bani mamaki, dama fa shi dan kauye bai san arziki ba , sai ka yi masa rana ya tashi ya yi maka dare , yanzu ina amfanin wannan, garin nasu duk daji."

Wani gau suka ji wata babbar mota ta bige su , a sa'ilin da sam ba su ganta ba
hakan ya sa motar ta su ta kwace ta nufi daji
"Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un, abin da suke fad'a ke nan

Umar ya bude murfin kofa
da nufin su fi ce a irin wannan gudun da motar take " Kalisa fita , fita kar kiji tsoron komai. "

Amma ina Kalisa duk ta rude rigarta ta makale
" Kai ka fita Umar ka fitaaaaaaa". Kalisa ta karasa maganar a yanayin firgici da ta ga sun kusa dukan wani dutse .

Kauuuu motar ta bigi dutse ta tashi sama , a lokacin suka fado kasa dukkansu , yayin da motar ta kama da wuta tun daga saman sannan ta fad'o kasa .

Kalisa ko shurawa ba tai ba

matukin waccen motar yana ganin haka ta faru kawai ya gudu abin sa ya bar su .Duk da shima yaji rauni .

Cikin mummunan yanayi Umar ya tashi kanshi duk jini , yana tashi ya fad'i kasa yaja jikinshi da kyer ya nufi Kalisa.

Yanayin tashin da ya yi mata ya tabbatar masa fa ta mutu bugu da kari wani karfe da ya gani a cikin gwiwarta ya tsagata .

Wani tashin hankali ne ya ziyarce sa ya kwalla ihu yana kiran sunanta da dukkan muryar da Allah ya hore masa.

Share ,like and comment...........📚
Gubar Rayuwata⚡🌹

By
Fatima Abdallaah kano
( Autar marubuta)

*AUTAR MARUBUTA CE*✍🏻👼🏻
🌹__________🌹_________🌹__________🌹_________🌹
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_🤲🏼
<><><🌹><><><>🌹<><><>🌹<><><><>🌹<><><><><>🌹<><>

Page 21&22

Cikin tsantsar mazantaaka Umar ya yi jarumta ya nemi mutane
Allah ya taimaa ka wasu mutane suka kawo dauki .Wanda har motar asubiti da 'yan sanda suka karaso
Yadda Umar ya ga an dauki Kalisa ya sake tabbatar masa Kalisa ta tafi ta barshi

Timm ya fadi kasa kamar matacce , asubitin cikin gari aka karasa dasu , tare da turasu emergency
Sai ga su Nabila sha'be -sha'be cikin kuka da matukar tashin hankali
suna isa wajen doctor ya fito daga d'akin Umar
da sauri suka tare shi , Jafar ne ya ce "Ya jikin na su likita."?

Baba Anje cikin damuwa ta kallo likita tana sauran amsa

" Ita macen tana ICU room, gaskiya akwai bukatar a yi mata aiki, shi na mijin yana sume , amma nan da anjuma..... "

Likita maganar da yaji a bayansa ne ya sa su duk baba anje saurin juyawa
"Likita ya jikin Kalisa ta." Umar ya fad'a cikin wasu ruwan hawaye dake shirin zubo masa
"Haba malam ka koma ka kwanta , komai zai iya faruwa da kai a wannan yanayi kana bukatar hutu da kulawa."
Dactor ya yi maganar yana kallon Umar
Umar ya karaso gabansu , kawai Nabila ta fashe da kuka ta rungume Jafar

ita ma baba anje duk tausayin Umar ya rufe ta da ganin ciwon dake tare dashi
"Dan Allah yaya Umar ka je ka huta a halin yanzu kaji abin da doctor ya ce ."
Jafar ya yi maganar Nabila kwance a kirjinsa yana rike da hannun Umar.

Umar ya janye hannunshi tare da fara cewa ," Ni bana jin komai Jafar , yanzu kawai Kalisa ce damuwar , domin karku mance akwai bukatar yi mata aiki tun kafin wannan accident din."

Wasu zafafan hawaye suka zubo masa sannan ya ci gaba da cewa ,"Na ga karfe ya huda gwiwar Kalisa, na ji zafi a zuciyata kuma na bayar ta rasu , yanzu kawai lafiya zamu nema mata. "

Baba anje cikin tashin hankali ta ce "Gaskiya ne , innalillahi wa inna'ilaihir raji'un."

Dactor ya ce "Tom gaskiya ciwonta ni bazan iya dubata ba , ku jira kwana biyu likita yana zuwa." Yana gama maganar ya wuce

Ba zato sukaji Umar ya shako sa ,"Kai wanne mara hankali ne , har gobe zamu jira tana cikin wannan yanayin, ina imaninka da tausayinka ka je fa su."?

Likita da ya ji shakar sa ta yi yawa cikin wahala ya fisge ya hankade Umar "Kai mahaukacin ina ne , bari na kira security su fitar da kai." Dactor din ya karasa maganar ya nufi wajen masu gadi

Umar ya ce , "Mu dauki Kalisa mu koma babban asubitin dactor Aisha hakan zai fi."

Nabila ta yi ajiyar zuciya tana kiran sunan Allah .

Mahmud ne ya fito waje yana duban yanayin anguwar yadda tsarinta kullum yake sake burgeshi , duba ga manyan gidaje da sanyin anguwar
hakan ya sa har yau ya kasa komawa gida, har Aminu ya koma , amma shi ba shi da niyya , amma babban dalilin 'kin komawarsa a kan Zainab ne .

Sake bude idanunshi ya yi yana sake kallon abin da ya hango daga gefe ,
kofar gidan wani mutum malam na lado , wanda har almajirai yana dasu

Mahmud ido ya sake zubawa yana kallon ikon Allah

"Mene Harun yake yi anan".
Mahmud ya tambayi kanshi .

Daga bisani lokacin da Harun ya kula da Mahmud ya yi murmushi ya nufo wajensa.

" Malam Mahmud me ake kuma anan." Harun ya tambaya lokacin da ya karaso gaban shi

Mahmud zuciyarshi wata irin tafasa take masa kamar ya kai masa duka, amma ya daure ya kalle shi yana cewa "Mene ka zo yi a wannan anguwar."?

Harun ya sheke da dariya har da tafawa , sannan ya ce ," Mahmud ni wallahi ma dariya kake bani , to mene ya dameka dani, sannan kuma kar ka yi zaton na bar Zainab, Wallahi ban bar ta ba , kai ne kamin shamaki da ita , amma wallahi kasa a ranka da zarar na zama soja wallahi sai na kawar da kai dan na samu Zainab, ka rubuta ka aji ye ni Harun ni ne ajalinka. "

Ajiyar zuciya Mahmud ya yi yana cewa, " Mu yi mu gani , kar kai tunanin dan ka 'bata Asma'u na ya zamo ina jin tsoron ka......."

Mahmud bai karasa maganar ba Harun ya dakatar dashi da cewa ,"Zan yi wulakanci idan nasa kaki , wallahi Mahmud sai na wulakantaka, zaka gani."

Ya wuce ya yi tafiyarsa

Ran Mahmud ya matukar baci sosai , gida ya shiga cikin bacin rai , ya shiga cikin lambu ya kasa tsaye ya kasa zaune , kawai maganar Harun ce take masa yawo , cikin ranshi yake sake nanata zancen
"Tabbas Harun azzalumi ne , zai aikata duk abin da yake so, yanzu mene mafita."?

Mahmud ya dafa kanshi da ya farai masa ciwo " To ko dai na shigar dashi kara. "?
Ya tambayi kanshi , tare da bada amsa kuma
" Gaskiya 'a'a wannan ba shawara ba ce ."
Ya tsuguna kamar mai shirin yin kuka , sannan ya tashi tsaye yana kallon sararin sama yana ajiyar zuciya.

Da sauri ya dawo da kanshi kasa tare da rudewa da farin cikin shawarar da ta zo masa,
da sauri ya shiga cikin gidan ya wuce d'akinshi ya dauko wayarshi dake caji ya zauna a bakin gado .

Sannan ya fara danna wayar yana cewa, "Hhh kwananka ya kare Harun." A daidai lokacin yana kiran numbar Hauwa 'yar gidan lu'utanal

Kamar jira take karaf ta dauki kiran "Ya Mahmud manyan gari kwana biyu." Ta yi maganar cikin yaren turanci

Murmushi Mahmud ya farayi sannan ya ce "Ke dai bari Hauwa ai kasar ta ku ce , wallahi ina cikin tashin hankali."

"Subhanallahi yayana meke damunka." Hauwa tai maganar cikin tsantsar kulawa

Nan take Mahmud ya fara zuba kai tsaye "Wallahi Hauwa Harun ba shi da imani mazunaci ne yadda kika san ba dan halak ba , azzalumi ne , mata yake lalatawa ke har HIV yana d ita ."

Jin ya yi shiru ne ya sa ta kwashe da dariya 😂

"Au dariya zaki mini." Ya yi maganar cikin haushi

Hauwa cikin dariya ta ce ,"Yi hakuri, nasan daga ji haushin sa kake ji , domin nasan da yana kusa da kai sai Allah. To amma ni mene nawa a ciki."

Mahmud ya sanar mata da komai tun daga waye Harun , har zuwa yau din nan , tare da neman alfarma ta sanar d mahaifin ta Lu'utanan

nan Hauwa ita ma ranta ya baci ta kashe waya ta fita falo

Mahaifiyarta Hajjiya Bilkisu na zaune ta fad'a jikinta ta kamata .

"To mene kuma ko sirikin nawa ne." Hajjiyan ta fad'a

Hauwa ta tashi ta bata rai tana cewa "Momy wani ne ..."

Lu"utanan Sadik ya shigo ya tari numfashinta yana cewa "Ya taba ki ko me? fad'a min mamana."

"Dady a cikin sojojin da zaku diba akwai Haruna Sani mu'a zu , irin wannan d'auri ne ya dace dasu." Ta karasa maganar cikin kwalla

Hakan ya sa Lu'utanal hankalinsa ya tashi "Manana waye ne shi mene ya miki."

Nan ta fad'a masa waye Harun kuma da kalar barnar da yake da kuma wacce zai idan ya samu aikin soja .

Nan ita ma Hajjiya Bilkisu tai Allah wadai dashi
yayin da Lu'utanal Sadiq Muhammad ya tabbatar wa Hauwa za ai bincike a kan shi .

"Yawwa dady ina so zanje gidansu Surayya, domin tun da ta dawo daga America bamu had'u ba."

"Okay gidan ambassador koh."? Lu'utanal ya tambaya.

" Eh can dady."

"To ki bari idan na samu lokaci sai mu je tare."

Hauwa ta ce ,"Okay dady."
Chapter 10 · 0% Book details