Sashe 5
Fatalwar Deborah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Keɓaɓiyar duniya ce wacce aka tanada domin ɓatattun ruhika waɗanda suka kasa gane inda za su dosa” ya bani amsa.
“Kana nufin nan ba Zimbabwe ba ne?”
Wani kallo yayi min na wani lokaci kafin yayi ɗan ƙyaci ya ce “wannan duniyar da taku abubuwa biyu ne mabanbanta,iya ruhi kawai ke shigowa a nan amma ke ban san ta ya aka kika zo nan ba alhalin babu wani tabo da ke nuna kin aikata wani zunubin”
“Don Allah ka taimaka min na koma gidana” na faɗa ina hawaye.
Ya ce “dole sai na san wanda ya turo ki izuwa nan”
“Kamar yaya?”
“Ina nufin matsafi,aljani ko bokan da ya cillo ki nan”
“Deborah ce”
Ina faɗar sunanta sai yanayin fuskarsa ya canza ya bayyanar da razani,amma ban san me yasa ba ya kwantar min da hankali wurin cewa “ko ma dai wace ce za ki fita in kin so sannan in kin yi niyya don babu abin da ya fi abin bautar Musulmi ƙarfi ”
Wata ajiyar zuciya na sauke da tunanin a yau zan koma gida amma sai na ji yana mai ci gaba da cewa “za ki biyo ni mu je can gidana in kin huta sai na faɗa miki hanyoyin da za ki bi ki koma duniyarku”
Duk da ban so haka ba amma na yi yadda ya ce ɗin na take masa baya har muka isa wani kogo,ko kafin na kai ga tambayarsa me za mu yi a nan sai na ga ya rikiɗe ya koma maciji .Na yi baya da sauri ina waro ido,yayin da shi kuma ya soma magana “kar ki ji tsoro domin ni ɗin aljani ne ba mutum ba,ki kama kogon gam za ki tsinci kanki a ciki”
Na girgiza masa kai don ba zan yarda na shiga cikin wuri tare da aljani ba.
“Ba ki da sauran lokaci ki yi sauri ki shiga na fara jin ƙamshin Deborah muddin ta tarar da ke nan to shi kenan fa ba zan iya yi miki komai ba” bai gama rufe bakinsa ba na soma jin sawun takunta,jiki na rawa na yi yadda ya ce kamar ƙyaftawar ido sai gani cikin kogon wanda ke ɗauke da abubuwan ban mamaki.
Daga inda nake ciki na ji muryar Deborah na cewa “Baba tsoho ba ka ga wani ruhi yana shawagi ba ta nan wurin?”
“Babu wani baƙon ruhi da ya shigo nan duk yau” ya bata amsa,sai ta yi gaba shi kuma ya shigo yana mai kallona kafin ya rikiɗe ya koma mutum.Wata step ya soma takawa ni ma na take masa baya har muka isa can saman ƙatuwar bishiyar,na waro ido ina kallon duniyarmu ya bil'adama.
Ya tsinko wani fure ya murza shi yana mai furta wasu harufa sai ga gidana ya bayyana,haka yayi ta tafiya da tunanina har muka shiga babban falo Uncle Salem na gani a zaune duk hankalinsa a hargitse,yayin da bokanyar gidanmu ke zuga shi kan cewa babu wani ɓata da na yi akwai dai inda na je na ɓuya abin da ya fi ban mamaki jin wai tana faman cewa sati guda rabona da gida.Baba tsoho kamar ya san abin da ke raina sai cewa yayi “kin yi doguwar tafiya ne shi yasa,kika yi kwanakin nan” bai ida rufe baki ba duk komai ya ɓace daga idonmu wanda na lura yayi daidai ne da shigowar wata baƙuwar fuska a falon wacce alamu suka nuna kuma ƴar aiki ce....
[28/02 08:22] MRS SADAUKI: *FATALWAR DEBORAH*🐲
MAKARANTAR MATSAFA 2 ☠️
```LoVe aNd HoRrOr story```👽
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}
*SADAUKARWA :* Ga malaman makaranta
*FCWA*☀️
________________________
08
“Da matsala fa,ina ga Deborah ce ta ɗauki siffar bil'adama ta je gidanki da sunan ƴar aiki” Baba tsoho ya faɗa fuskarsa cike da damuwa.
Cike da tashin hankali na ce “ta ya aka yi ka gane?”
“Ita kaɗai ce mai ƙarfin ikon da za ta iya katse min dubana kai tsaye daga shigowarta,yanzu abin da ya kamata a yi ki je ki kwanta ki huta zan fara binciken hanyar da za ki bi ki koma gida kafin nan da wata uku”
“Wata uku kuma? Ni da nake son na koma tun yau” na faɗa a rikice.
Wani kallo yayi min kafin ya ce “kina tunanin tafiya daga ɓoyayyar duniya zuwa duniyar bil'adama abu ne mai sauƙi? To tsaya ki ji ita kanta Deborah farkon ranar da za ta keta hijabin da ke tsakaninmu da ku sai da ta ɗauki kusan shekara guda currr.In taƙaice miki zancen a ƙaramin misali sai kin yi tafiyar wata biyu kafin ki isa can,shi ma sai in na samu aljani mai matuƙar gudu”
Wani gumi ne ya rufe ni nan take,a duniyarmu na sha jin cewa aljani na iya yin abu kamar ƙyaftawar ido amma a nan ga shi yana yi min zancen watanni biyu.Sam ban yarda da shi ba,don haka na ƙudurta a raina zan fita daga kogon nan na je na nemi hanyar da kaina.
Kan wani gadon ganye na je na kwanta kamar yadda ya ce,na lumshe idona amma ba da niyyar yin bacci ba.Sai da na bari hankalinsa ya ɗauku kan aikin da yake yi jikin wani allon ƙarfe sai na yi saurin sauka daga gadon na je na dafa kogon nan take na tsinci kaina a fili.
Gudu na soma ina waiwaiye har sai da na yi nisa sosai sannan na tsaya yin tafiya,cikin ikon Allah na hangi hanyoyi biyu daga nan ma ina tsinkayen kwalta.Na saki murmushi don kuwa na san in ba a duniyarmu ba babu inda ke da kwalta ina dab da bin ɗaya daga cikin hanyoyin kwatsam wani dodo ya bayyana a gabana.Tsoro ya kama ni ,ga shi ina son yin baya amma tamkar shukar da aka dasa haka na kasa motsi.
“Barka da zuwa hanyar tsirar ruhin da ya ɓata” dodon ya faɗa yana wangale min baki nan muninsa ya ƙara bayyana,hanya ya bani da nufin na wuce.Abin da ya faɗa na maimaita a zuci sai na fahimci eh lalle ina kan hanyar daidai kenan, wannan karon ina cira ƙafata sai ta bar ƙasa haka na bi hanyar nan na soma tafiya duk yadda nake tsinkayen kwaltar amma na kasa kawowa a gare ta.
Ga yunwa ga ƙishi ga gajiya,sai na ɗan sunkuya ina mai riƙe gwiwaina kamar mai yin sallah daidai nan idona yayi tozali da wani ɗan rame kamar gurbin tanda sai ruwa ke ɓulbulowa.Jikina har rawa yake wurin duƙawa na soma sha,sam ban farga ba na ji ni tsundum cikin ruwa na nitse ciki hatta kaina.Ina ɗaga kaina sai na ga wasu ƴan masu mugun kyawu suna wasar kos,yayin da kuma ɗaya daga cikinsu ke gefe tana saƙar hannu.Ido muka haɗa da ita sai ta sakar min murmushi kafin ta yi min alama da hannu na zo,ƙafafuwana a sanyaye na soma tafiya kwacal! Kwacal ! Cikin ruwan har na isa gare ta.
Duk ƴan matan suka maido hankalinsu gare ni,suna masu karon baki wurin cewa “waooo! Bil'adama a duniyarmu?”
“Ku yi min shuru ku ci gaba da wasarku,ke kuma zauna nan” ta dube ni tare da nuna min wani Kunkuru🐢 ni tsoronsa ma ya kama ni ganin yadda yake ziro kai yana maida shi kuma ciki, amma a haka na daure na zauna.
Tsakiyar idona ta kafe da kallo har sai da na ji wani abu na huda fatata yana ratsa ɓargona,a nan take kuma tsikar jikina ta tashi duk gashin da ke hannuna yayi wani tsiri-tsiri da shi ban gama yin mamaki ba na ga wani abu ya soma fita daga hudodin yana zubewa...
Ga waɗanda ke son shiga paid group sai su yi min magana kai tsaye ta WhatsApp numberta +22795045822.
A page 10 zan dakata da free page in sha Allah
[28/02 10:07] MRS SADAUKI: *FATALWAR DEBORAH*🐲
MAKARANTAR MATSAFA 2 ☠️
```LoVe aNd HoRrOr story```👽
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}
*SADAUKARWA :* Ga malaman makaranta
*FCWA*☀️
________________________
9_10
★DEBORAH
Ta daɗe tana kwaɗayin dawowa duniyar bil'adama tun shekaru ɗari da ashirin da suka gabata,sai dai ba ta samu ƙwaƙwaran dalilin da za ta faɗawa al'ummarta na ɓoyayyar duniya waɗanda take mulka ba.Sai a ranar da idonta suka yi gamdakatar da Uncle Salem ta ji wata hatsababiyar ƙaunarsa ta shiga ranta,ta yi ƙoƙarin danne muradinta sai dai hutar sonsa sai ƙara azalzala take yi a ranta.Yanayin yadda yake kula da Nafisa shine abin da take so tun lokacin da ta na raye,sai dai babu namijin da ke da jarumtar tunkararta da zancen so ballantana har ya kai ga ririta ta dukkan hatsabiban matsafa da bokaye tsoronta suke.
A ranar da ta zo ta shigar da Uncle Salem faɗa da niyyar dama don ta kasance matarsa ta dare ne a duniyar mafarki,shi yasa ta sanar da shi cewa dukkan komai yana da farashi.
A yanzu da ta faso duniyar bil'adama ba ta ga abin da zai mayar da ita ɓoyayyar duniya ba,farkon zuwanta a jikin Abidah ta yi wa baƙin ruhinta masauki.Cikin shu'umancin da ta saba yi ta juyar da kwanyar Mamar Sadauki ta saka mata kishin Nafisa,don sai in rikici ne ya shiga a tsakaninsu ne za ta samun yadda take so.Korar bayi masu yi wa Nafisa hidima duk tsarinta ne,kuma birninta ya cika duk an sallame su.
A wannan ranar ce kuma ta bazama neman gangar jikin da za ta ɗauka,dole tana buƙatar na cikakkiyar mace mai hankali wannan yasa ta fita tsakar dare neman raunatacen ruhin da za ta nakasa ta ɗauke gangar jikin.
Gida-gida ta dinga bi har Allah ya kai ta gidan Sakina ƙawar Nafisa,tun kallon farko ta gane ta.Tsaye ta yi tana kallon yadda Sakina ke zazzaga wa mijinta ruwan masifa tana cewa “ wallahi sai ka sake ni,ba zan zauna kullum kana tafiyarka daji kana barina a gida ba kamar wata mai gadi .Ka sake ni na je na auri wani wanda ya san mutumcina,ai MIJI GOMA BA UBA GOMA BA NE(littafin Sadiya AbdulRak kenan)”
Cikin rarrashi ya ce “Sakina ki ajiye hankalinki da kyau ki yi wa kanki karatun tanutsu don kar ki je ki yi BONONO(Mom Afra) daga baya ki zo kina cizon yatsa”
“Wa ya faɗa maka ƘWAƘWALWAR KIFI( Emilia) ce da ni da ban san abin da zai fishe ni dare ba?”
“Kana nufin nan ba Zimbabwe ba ne?”
Wani kallo yayi min na wani lokaci kafin yayi ɗan ƙyaci ya ce “wannan duniyar da taku abubuwa biyu ne mabanbanta,iya ruhi kawai ke shigowa a nan amma ke ban san ta ya aka kika zo nan ba alhalin babu wani tabo da ke nuna kin aikata wani zunubin”
“Don Allah ka taimaka min na koma gidana” na faɗa ina hawaye.
Ya ce “dole sai na san wanda ya turo ki izuwa nan”
“Kamar yaya?”
“Ina nufin matsafi,aljani ko bokan da ya cillo ki nan”
“Deborah ce”
Ina faɗar sunanta sai yanayin fuskarsa ya canza ya bayyanar da razani,amma ban san me yasa ba ya kwantar min da hankali wurin cewa “ko ma dai wace ce za ki fita in kin so sannan in kin yi niyya don babu abin da ya fi abin bautar Musulmi ƙarfi ”
Wata ajiyar zuciya na sauke da tunanin a yau zan koma gida amma sai na ji yana mai ci gaba da cewa “za ki biyo ni mu je can gidana in kin huta sai na faɗa miki hanyoyin da za ki bi ki koma duniyarku”
Duk da ban so haka ba amma na yi yadda ya ce ɗin na take masa baya har muka isa wani kogo,ko kafin na kai ga tambayarsa me za mu yi a nan sai na ga ya rikiɗe ya koma maciji .Na yi baya da sauri ina waro ido,yayin da shi kuma ya soma magana “kar ki ji tsoro domin ni ɗin aljani ne ba mutum ba,ki kama kogon gam za ki tsinci kanki a ciki”
Na girgiza masa kai don ba zan yarda na shiga cikin wuri tare da aljani ba.
“Ba ki da sauran lokaci ki yi sauri ki shiga na fara jin ƙamshin Deborah muddin ta tarar da ke nan to shi kenan fa ba zan iya yi miki komai ba” bai gama rufe bakinsa ba na soma jin sawun takunta,jiki na rawa na yi yadda ya ce kamar ƙyaftawar ido sai gani cikin kogon wanda ke ɗauke da abubuwan ban mamaki.
Daga inda nake ciki na ji muryar Deborah na cewa “Baba tsoho ba ka ga wani ruhi yana shawagi ba ta nan wurin?”
“Babu wani baƙon ruhi da ya shigo nan duk yau” ya bata amsa,sai ta yi gaba shi kuma ya shigo yana mai kallona kafin ya rikiɗe ya koma mutum.Wata step ya soma takawa ni ma na take masa baya har muka isa can saman ƙatuwar bishiyar,na waro ido ina kallon duniyarmu ya bil'adama.
Ya tsinko wani fure ya murza shi yana mai furta wasu harufa sai ga gidana ya bayyana,haka yayi ta tafiya da tunanina har muka shiga babban falo Uncle Salem na gani a zaune duk hankalinsa a hargitse,yayin da bokanyar gidanmu ke zuga shi kan cewa babu wani ɓata da na yi akwai dai inda na je na ɓuya abin da ya fi ban mamaki jin wai tana faman cewa sati guda rabona da gida.Baba tsoho kamar ya san abin da ke raina sai cewa yayi “kin yi doguwar tafiya ne shi yasa,kika yi kwanakin nan” bai ida rufe baki ba duk komai ya ɓace daga idonmu wanda na lura yayi daidai ne da shigowar wata baƙuwar fuska a falon wacce alamu suka nuna kuma ƴar aiki ce....
[28/02 08:22] MRS SADAUKI: *FATALWAR DEBORAH*🐲
MAKARANTAR MATSAFA 2 ☠️
```LoVe aNd HoRrOr story```👽
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}
*SADAUKARWA :* Ga malaman makaranta
*FCWA*☀️
________________________
08
“Da matsala fa,ina ga Deborah ce ta ɗauki siffar bil'adama ta je gidanki da sunan ƴar aiki” Baba tsoho ya faɗa fuskarsa cike da damuwa.
Cike da tashin hankali na ce “ta ya aka yi ka gane?”
“Ita kaɗai ce mai ƙarfin ikon da za ta iya katse min dubana kai tsaye daga shigowarta,yanzu abin da ya kamata a yi ki je ki kwanta ki huta zan fara binciken hanyar da za ki bi ki koma gida kafin nan da wata uku”
“Wata uku kuma? Ni da nake son na koma tun yau” na faɗa a rikice.
Wani kallo yayi min kafin ya ce “kina tunanin tafiya daga ɓoyayyar duniya zuwa duniyar bil'adama abu ne mai sauƙi? To tsaya ki ji ita kanta Deborah farkon ranar da za ta keta hijabin da ke tsakaninmu da ku sai da ta ɗauki kusan shekara guda currr.In taƙaice miki zancen a ƙaramin misali sai kin yi tafiyar wata biyu kafin ki isa can,shi ma sai in na samu aljani mai matuƙar gudu”
Wani gumi ne ya rufe ni nan take,a duniyarmu na sha jin cewa aljani na iya yin abu kamar ƙyaftawar ido amma a nan ga shi yana yi min zancen watanni biyu.Sam ban yarda da shi ba,don haka na ƙudurta a raina zan fita daga kogon nan na je na nemi hanyar da kaina.
Kan wani gadon ganye na je na kwanta kamar yadda ya ce,na lumshe idona amma ba da niyyar yin bacci ba.Sai da na bari hankalinsa ya ɗauku kan aikin da yake yi jikin wani allon ƙarfe sai na yi saurin sauka daga gadon na je na dafa kogon nan take na tsinci kaina a fili.
Gudu na soma ina waiwaiye har sai da na yi nisa sosai sannan na tsaya yin tafiya,cikin ikon Allah na hangi hanyoyi biyu daga nan ma ina tsinkayen kwalta.Na saki murmushi don kuwa na san in ba a duniyarmu ba babu inda ke da kwalta ina dab da bin ɗaya daga cikin hanyoyin kwatsam wani dodo ya bayyana a gabana.Tsoro ya kama ni ,ga shi ina son yin baya amma tamkar shukar da aka dasa haka na kasa motsi.
“Barka da zuwa hanyar tsirar ruhin da ya ɓata” dodon ya faɗa yana wangale min baki nan muninsa ya ƙara bayyana,hanya ya bani da nufin na wuce.Abin da ya faɗa na maimaita a zuci sai na fahimci eh lalle ina kan hanyar daidai kenan, wannan karon ina cira ƙafata sai ta bar ƙasa haka na bi hanyar nan na soma tafiya duk yadda nake tsinkayen kwaltar amma na kasa kawowa a gare ta.
Ga yunwa ga ƙishi ga gajiya,sai na ɗan sunkuya ina mai riƙe gwiwaina kamar mai yin sallah daidai nan idona yayi tozali da wani ɗan rame kamar gurbin tanda sai ruwa ke ɓulbulowa.Jikina har rawa yake wurin duƙawa na soma sha,sam ban farga ba na ji ni tsundum cikin ruwa na nitse ciki hatta kaina.Ina ɗaga kaina sai na ga wasu ƴan masu mugun kyawu suna wasar kos,yayin da kuma ɗaya daga cikinsu ke gefe tana saƙar hannu.Ido muka haɗa da ita sai ta sakar min murmushi kafin ta yi min alama da hannu na zo,ƙafafuwana a sanyaye na soma tafiya kwacal! Kwacal ! Cikin ruwan har na isa gare ta.
Duk ƴan matan suka maido hankalinsu gare ni,suna masu karon baki wurin cewa “waooo! Bil'adama a duniyarmu?”
“Ku yi min shuru ku ci gaba da wasarku,ke kuma zauna nan” ta dube ni tare da nuna min wani Kunkuru🐢 ni tsoronsa ma ya kama ni ganin yadda yake ziro kai yana maida shi kuma ciki, amma a haka na daure na zauna.
Tsakiyar idona ta kafe da kallo har sai da na ji wani abu na huda fatata yana ratsa ɓargona,a nan take kuma tsikar jikina ta tashi duk gashin da ke hannuna yayi wani tsiri-tsiri da shi ban gama yin mamaki ba na ga wani abu ya soma fita daga hudodin yana zubewa...
Ga waɗanda ke son shiga paid group sai su yi min magana kai tsaye ta WhatsApp numberta +22795045822.
A page 10 zan dakata da free page in sha Allah
[28/02 10:07] MRS SADAUKI: *FATALWAR DEBORAH*🐲
MAKARANTAR MATSAFA 2 ☠️
```LoVe aNd HoRrOr story```👽
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}
*SADAUKARWA :* Ga malaman makaranta
*FCWA*☀️
________________________
9_10
★DEBORAH
Ta daɗe tana kwaɗayin dawowa duniyar bil'adama tun shekaru ɗari da ashirin da suka gabata,sai dai ba ta samu ƙwaƙwaran dalilin da za ta faɗawa al'ummarta na ɓoyayyar duniya waɗanda take mulka ba.Sai a ranar da idonta suka yi gamdakatar da Uncle Salem ta ji wata hatsababiyar ƙaunarsa ta shiga ranta,ta yi ƙoƙarin danne muradinta sai dai hutar sonsa sai ƙara azalzala take yi a ranta.Yanayin yadda yake kula da Nafisa shine abin da take so tun lokacin da ta na raye,sai dai babu namijin da ke da jarumtar tunkararta da zancen so ballantana har ya kai ga ririta ta dukkan hatsabiban matsafa da bokaye tsoronta suke.
A ranar da ta zo ta shigar da Uncle Salem faɗa da niyyar dama don ta kasance matarsa ta dare ne a duniyar mafarki,shi yasa ta sanar da shi cewa dukkan komai yana da farashi.
A yanzu da ta faso duniyar bil'adama ba ta ga abin da zai mayar da ita ɓoyayyar duniya ba,farkon zuwanta a jikin Abidah ta yi wa baƙin ruhinta masauki.Cikin shu'umancin da ta saba yi ta juyar da kwanyar Mamar Sadauki ta saka mata kishin Nafisa,don sai in rikici ne ya shiga a tsakaninsu ne za ta samun yadda take so.Korar bayi masu yi wa Nafisa hidima duk tsarinta ne,kuma birninta ya cika duk an sallame su.
A wannan ranar ce kuma ta bazama neman gangar jikin da za ta ɗauka,dole tana buƙatar na cikakkiyar mace mai hankali wannan yasa ta fita tsakar dare neman raunatacen ruhin da za ta nakasa ta ɗauke gangar jikin.
Gida-gida ta dinga bi har Allah ya kai ta gidan Sakina ƙawar Nafisa,tun kallon farko ta gane ta.Tsaye ta yi tana kallon yadda Sakina ke zazzaga wa mijinta ruwan masifa tana cewa “ wallahi sai ka sake ni,ba zan zauna kullum kana tafiyarka daji kana barina a gida ba kamar wata mai gadi .Ka sake ni na je na auri wani wanda ya san mutumcina,ai MIJI GOMA BA UBA GOMA BA NE(littafin Sadiya AbdulRak kenan)”
Cikin rarrashi ya ce “Sakina ki ajiye hankalinki da kyau ki yi wa kanki karatun tanutsu don kar ki je ki yi BONONO(Mom Afra) daga baya ki zo kina cizon yatsa”
“Wa ya faɗa maka ƘWAƘWALWAR KIFI( Emilia) ce da ni da ban san abin da zai fishe ni dare ba?”