Sashe 12
Fatalwar Deborah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya ɗan jan numfashi kafin ya ce “ ina kewarki Naf”
Na yi ƴar dariya kafin na ce “ Uncle tun da ka fasa tafiya me zai hana ka zo nan ɗin ka yi kwana biyu?”
Ya ce “ kika ce ɗaki ɗaya ne tal inda aka sauke ku”
Na ce “ eh amma ai ba za a rasa wurin da za ka kwanta ba ko da hotel ne”
Yayi ƴar dariya kafin ya ce “ to zan duba na gani,amma Please ki kula min da kanki sosai banda magana da maza ko da kuwa shugaban makarantar ne ban so”
Na ce “ to Uncle in sha Allah,amma yaushe za ka zo?”
“ Sai zuwa wani satin Naf,yanzu akwai binciken da zan yi”
Kafin na basa amsa sai da na juya na dubi Inna A'i wacce ta zagaya toilet a karo na uku tun lokacin da na soma waya,ina son tambayarta lafiya amma saukar numfashin Uncle a kunnena yasa na ƙara mayar da hankali wurinsa.
“ To Uncle zan fara lissafin kwanaki tun yanzu”
“Faɗa min me za ki shirya min na special?” tambayar da yayi min kenan wacce na ji wani banbarakwai don har wani salo na daban amon muryarsa ke fitarwa.Kamar zai yi kuka na ji yana cewa “ Please Naf faɗa min mana kar ki ji kunyata ” hakan kuwa ya ƙara ɗaure jijiyoyina na rasa amsar da zan basa,daga can toilet na soma jiyo saurin nishin Inna A'i cikin azaba babu wani tunani na kashe kiran Uncle ɗin tare da nufar toilet ɗin ina tambayar lafiya.Ba ta bani amsa ba sai ƙofar toilet ɗin da ta buɗe ƙiiii da kanta,daga inda nake tsaye na hangi Inna A'i zaune kan wc tuni ta fita hayyacinta don da alamu gudawa ce take ta yi.
Tsakaka na gani kan katanga tana saukowa kamar za ta faɗo bisa kanta da mugun sauri na ɗauki takalme ina kiran sunan Allah na kashe tsakar,ta kuwa faɗo ƙasa bindinta ya rabu da gangar jikinta da mugun sauri kuma ta bi ta ƙafafuna shuuu ta fice ta bar guntun bindin wanda sai motsi yake.
Daidai nan Inna A'i ta soma kelaya amai kamar hanjinta za su faɗo,ba tare da tsantsani ko ƙyanƙyaminta ba na taimaka mata ta yi wanka ,bayan nan na sa abin kwashe shara na saka bindin tsakakar sannan na wanke toilet ɗin na rufe ƙofa.Ina zuwa tuni Inna A'i ta yi bacci,ni ma sai na raɓa gefenta na kwanta.
Washegari bugun ƙofar ɗakinmu ne ya tashe mu,yadda ake jijiga ƙofar kamar za a ɓallata yasa muka kalli juna kafin na miƙe na je na buɗe,da sauri na yi baya ina kallon shugaban makarantar da mamakin abin da ya zo nema a yanzu ko ƙarfe shidda ba ta yi ba.Yadda kuma yake yi min wani kallon tsaf yasa na sha jinin jikina......
Ga mai son shiga paid group 500 ne via
2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank
Sai ya turo min da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822
[28/02 10:12] MRS SADAUKI: *MAKARANTAR MATSAFA*☠️
```LoVe aNd HoRrOr story```👽
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}
*SADAUKARWA :* Ga dukkan Malaman makaranta.
*FCWA*☀️
________________________
6-7
Na haɗiye wasu yawu muƙut, Allah na gani ba na cikin mutane masu mugun tsoron nan don za a iya kirana jaruma kai tsaye amma kallon idon headmaster kaɗai sai da suka hautsana hanjin cikina.
“ Barka da warhaka shugaba!” na samu bakina dakyar ya furta.
Ya saki wani murmushi wanda kana gani ka san ba na jin daɗi ba ne kafin ya ce “ lafiya! Ina son duba toilet ne don ganin ko gyaran da aka yi yayi” ya faɗa cikin wani irin amo.
Kamar na ce masa wane gyara kuma amma sai na basa wuri ya shigo,cike da girmamawa ya gaishe da Inna A'i wacce ke zaune har yanzu a inda na bar ta kafin ya shiga cikin toilet ɗin na take masa baya kuwa.Dube-dube na ga yana yi kamar mai neman wani abu amma ban kawo komai ba don na yi tunanin ko gyaran ne a gaske yake dubawa .
Fuskarsa duk ta nuna alamun ƙin jin daɗi har zai fito sai kuma ya tsaya cak yana cewa “jinin mene ne can?”
Inda ya nuna na duba sai na ga daidai wurin da na kashe katsakakar jiya ne,amma ai na wanke toilet ɗin sosai ta ya aka yi jinin bai fita ba.
Yadda ya watso min idonsa masu matuƙar dafi yasa na soma inda-inda,“ dama...dama jiya ne da Innarmu ta shiga ta ga tsakaka...” da sauri ya katse ni “ kenan ita ce ta buge mata bindi? ”
Tsuru-tsuru na yi don ina tsoron kar ya kore ni ya ce ba zan koya ba,ya ƙanƙance ido ya ce “mu nan garin ba a kashe ƙwari ban san daga wane wajen kuka fito ba” sai kuma ya fita ni ma na take masa baya,ina kallon yadda ya bi Inna A'i da wani mugun kallo kafin ya fita.
Ɗakin na rufe bayan na gama kallon yadda har a wajen sai da yayi ta dube-dube.
Ko da na juyo sai na ga tuni ta shiga toilet,sai na jira ta fito sannan na shiga ni ma na yi alwala na fito na yi sallah sannan na zauna na yi Azkhar ɗin safe.
“ Ina kwana Innarmu? Ya ƙarfin jikin naki?” na faɗa bayan na gama komai.
“ Alhamdullah ai na ma warware,ina ga kajin jiya ne suka buga min ciki don na yi doguwar tafiya” ta bani amsa .
Na ce “ ai kuwa dai ,yanzu ki kwanta ki huta dai zuwa an jima sai ki yi mana girki”
Ta ce “ a'a na fa warke yanzu zan shiga kitchen“ tana gama faɗa ta miƙe kuwa,ni kuma na ɗauki wayata nan na ci karo da miss call ɗin Uncle Salem ya fi goma duk yayi su ne bayan na kashe kiransa na jiya.Ɓangaren saƙo na duba sai na ga text ɗinsa yana bani haƙuri tare da alƙawarin ba zai sake ba.
Kiransa na yi sai dai sam lambar ba ta shiga,duk sai na ji babu daɗi haka na kunna data na soma yin shat ban ajiye wayar ba sai da na ga ta kusa mutuwa sannan na saka ta caji.Ina shirin shiga wanka na ji ana shelar ana son ganin dukkanin malaman da suka zo a ɗakin meeting da ke cikin makaranta da misalin ƙarfe takwas da rabi .
★Uncle Salem
Cikin kaɗaicin son kasancewa da Nafisa ya soma bijiro mata da sabbin abubuwan da za ta fahimci shi mijinta ne amma da dukkan alamu ya ga sam ita a iya uban kawai ta yi masa matsuguni.Jin ta kashe masa waya yayi tunanin kunya da kuma fushi ne yasa ta datse kiran,hakan yasa yayi ta jera mata su da ya ga ta ƙi ɗauka sai ya tura mata text tare da kashe wayar ya rungume pilow.Zuwa yanzu haƙurinsa da juriyarsa sun yi ƙasa sosai,yana matuƙar son kasancewa da ita a duk cikin sati ranar juma'a da asabar kawai a bai yin azumi duk don kare mutumcinsa.Sau ɗaya tak ya taɓa neman auren wata wacce dama ita ce take haukan sonsa,amma an zo yin auren aka fasa saboda bai da wani asali.
Idonsa sun kaɗa sun yi jajur saboda abu biyu da suka haɗe masa, feeling da kuma fushin Naf wanda a duniya in akwai abin da yake guje ma to bayansa yake shi yasa a kowane lokaci yake yi mata abin da take so.Ko da kuwa iyayenta sun so nuna masa illar gatan da yake yi mata sai ya ce musu har yanzu Naf yarinya ce.Sai dai a jiya da Daddy ya ce masa ya ci a ce ta tare da kuma yadda ya ga surarta cikin doguwar rigar da ta lafe jikinta duk ta fitar da shap ɗinta sai yake ji a ransa eh za ta iya ɗaukar nauyin buƙatarsa.
Juyi yayi ta yi a daren,da ya ga dai sam baccin ba fa zai zo ba sai ya miƙe ya je watso ruwa tare da zama kan dadduma yayi ta lazumi bayan raka'o'i biyu da yayi.Sai daf da asubah ya samu bacci,amma duk da haka ana kiran sallah sai da ya je masjid da ke nan cikin Company ya dawo ya ƙara komawa bacci.Bai farka ba sai wuraren ƙarfe goma na safiya,wani wankan ya sake tare da shirya wa cikin wando tree quater na sojawa da kuma rigarsa t-shirt ita ma ta kakin soja.Bai ɗora hulla ba ya dai saka farin gilashi kafin ya ɗauki key ɗin motarsa ta aiki da kuma wayarsa.Sai da ya fito a hanya ne ya kunna ta,bayan ya shiga mota ne ya ga saƙon cewa Nafisa ta so kiransa amma ba ta same shi ba.Ya ɗan saki murmushi yana jin zuciyarsa ta yi sanyi ko ba komai yana da tabbacin ta sauko daga fushin da take.Kiranta yayi har sau biyu,a na uku ne Inna A'i ta ɗauka ta shaida masa ta fita.
★ƘWARGWAM
Ko da na fito daga wanka tuni Inna A'i ta soya min dankali da kuma ƙwai,na yi zaune na ci na ƙoshi kafin na jawo kayan kwalliyata na shafa mai da turare har da hoda.Bayan nan na zaɓo doguwar riga ta tambaya ƴar côte d'ivoire,sosai ta amshe ni sai na zaɓo hijabi da jaka da kalmi duk waɗanda za su hau da ita.
Ina shirin fita ita ma Inna A'i ta fito daga kitchen hannunta riƙe da kwanon miya na jiya,ta ce “ ashe ba ki ci abincin nan ba dubi yadda duk yayi tsutsotsi ya lalace”
Na dubi cikin kwanon na ga babu kyawun gani manyan tsutsotsi ne ke ta yawo suna shige da fice cikin ragowar naman kajin.Da mamaki na ce “ amma kuma abincin har ya isa lalacewa haka?”
“ Ni ma haka na ce,ko ƙila zafi” Inna A'i ta faɗa .
Na ce “ kawai ki zubar ki wanke kwanukan sai ki mayar musu ,ga key nan in za ki fita ki rufe ɗakin na tafi sai na dawo”
“Allah ya tsare hanya”
Na yi ƴar dariya kafin na ce “ Uncle tun da ka fasa tafiya me zai hana ka zo nan ɗin ka yi kwana biyu?”
Ya ce “ kika ce ɗaki ɗaya ne tal inda aka sauke ku”
Na ce “ eh amma ai ba za a rasa wurin da za ka kwanta ba ko da hotel ne”
Yayi ƴar dariya kafin ya ce “ to zan duba na gani,amma Please ki kula min da kanki sosai banda magana da maza ko da kuwa shugaban makarantar ne ban so”
Na ce “ to Uncle in sha Allah,amma yaushe za ka zo?”
“ Sai zuwa wani satin Naf,yanzu akwai binciken da zan yi”
Kafin na basa amsa sai da na juya na dubi Inna A'i wacce ta zagaya toilet a karo na uku tun lokacin da na soma waya,ina son tambayarta lafiya amma saukar numfashin Uncle a kunnena yasa na ƙara mayar da hankali wurinsa.
“ To Uncle zan fara lissafin kwanaki tun yanzu”
“Faɗa min me za ki shirya min na special?” tambayar da yayi min kenan wacce na ji wani banbarakwai don har wani salo na daban amon muryarsa ke fitarwa.Kamar zai yi kuka na ji yana cewa “ Please Naf faɗa min mana kar ki ji kunyata ” hakan kuwa ya ƙara ɗaure jijiyoyina na rasa amsar da zan basa,daga can toilet na soma jiyo saurin nishin Inna A'i cikin azaba babu wani tunani na kashe kiran Uncle ɗin tare da nufar toilet ɗin ina tambayar lafiya.Ba ta bani amsa ba sai ƙofar toilet ɗin da ta buɗe ƙiiii da kanta,daga inda nake tsaye na hangi Inna A'i zaune kan wc tuni ta fita hayyacinta don da alamu gudawa ce take ta yi.
Tsakaka na gani kan katanga tana saukowa kamar za ta faɗo bisa kanta da mugun sauri na ɗauki takalme ina kiran sunan Allah na kashe tsakar,ta kuwa faɗo ƙasa bindinta ya rabu da gangar jikinta da mugun sauri kuma ta bi ta ƙafafuna shuuu ta fice ta bar guntun bindin wanda sai motsi yake.
Daidai nan Inna A'i ta soma kelaya amai kamar hanjinta za su faɗo,ba tare da tsantsani ko ƙyanƙyaminta ba na taimaka mata ta yi wanka ,bayan nan na sa abin kwashe shara na saka bindin tsakakar sannan na wanke toilet ɗin na rufe ƙofa.Ina zuwa tuni Inna A'i ta yi bacci,ni ma sai na raɓa gefenta na kwanta.
Washegari bugun ƙofar ɗakinmu ne ya tashe mu,yadda ake jijiga ƙofar kamar za a ɓallata yasa muka kalli juna kafin na miƙe na je na buɗe,da sauri na yi baya ina kallon shugaban makarantar da mamakin abin da ya zo nema a yanzu ko ƙarfe shidda ba ta yi ba.Yadda kuma yake yi min wani kallon tsaf yasa na sha jinin jikina......
Ga mai son shiga paid group 500 ne via
2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank
Sai ya turo min da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822
[28/02 10:12] MRS SADAUKI: *MAKARANTAR MATSAFA*☠️
```LoVe aNd HoRrOr story```👽
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}
*SADAUKARWA :* Ga dukkan Malaman makaranta.
*FCWA*☀️
________________________
6-7
Na haɗiye wasu yawu muƙut, Allah na gani ba na cikin mutane masu mugun tsoron nan don za a iya kirana jaruma kai tsaye amma kallon idon headmaster kaɗai sai da suka hautsana hanjin cikina.
“ Barka da warhaka shugaba!” na samu bakina dakyar ya furta.
Ya saki wani murmushi wanda kana gani ka san ba na jin daɗi ba ne kafin ya ce “ lafiya! Ina son duba toilet ne don ganin ko gyaran da aka yi yayi” ya faɗa cikin wani irin amo.
Kamar na ce masa wane gyara kuma amma sai na basa wuri ya shigo,cike da girmamawa ya gaishe da Inna A'i wacce ke zaune har yanzu a inda na bar ta kafin ya shiga cikin toilet ɗin na take masa baya kuwa.Dube-dube na ga yana yi kamar mai neman wani abu amma ban kawo komai ba don na yi tunanin ko gyaran ne a gaske yake dubawa .
Fuskarsa duk ta nuna alamun ƙin jin daɗi har zai fito sai kuma ya tsaya cak yana cewa “jinin mene ne can?”
Inda ya nuna na duba sai na ga daidai wurin da na kashe katsakakar jiya ne,amma ai na wanke toilet ɗin sosai ta ya aka yi jinin bai fita ba.
Yadda ya watso min idonsa masu matuƙar dafi yasa na soma inda-inda,“ dama...dama jiya ne da Innarmu ta shiga ta ga tsakaka...” da sauri ya katse ni “ kenan ita ce ta buge mata bindi? ”
Tsuru-tsuru na yi don ina tsoron kar ya kore ni ya ce ba zan koya ba,ya ƙanƙance ido ya ce “mu nan garin ba a kashe ƙwari ban san daga wane wajen kuka fito ba” sai kuma ya fita ni ma na take masa baya,ina kallon yadda ya bi Inna A'i da wani mugun kallo kafin ya fita.
Ɗakin na rufe bayan na gama kallon yadda har a wajen sai da yayi ta dube-dube.
Ko da na juyo sai na ga tuni ta shiga toilet,sai na jira ta fito sannan na shiga ni ma na yi alwala na fito na yi sallah sannan na zauna na yi Azkhar ɗin safe.
“ Ina kwana Innarmu? Ya ƙarfin jikin naki?” na faɗa bayan na gama komai.
“ Alhamdullah ai na ma warware,ina ga kajin jiya ne suka buga min ciki don na yi doguwar tafiya” ta bani amsa .
Na ce “ ai kuwa dai ,yanzu ki kwanta ki huta dai zuwa an jima sai ki yi mana girki”
Ta ce “ a'a na fa warke yanzu zan shiga kitchen“ tana gama faɗa ta miƙe kuwa,ni kuma na ɗauki wayata nan na ci karo da miss call ɗin Uncle Salem ya fi goma duk yayi su ne bayan na kashe kiransa na jiya.Ɓangaren saƙo na duba sai na ga text ɗinsa yana bani haƙuri tare da alƙawarin ba zai sake ba.
Kiransa na yi sai dai sam lambar ba ta shiga,duk sai na ji babu daɗi haka na kunna data na soma yin shat ban ajiye wayar ba sai da na ga ta kusa mutuwa sannan na saka ta caji.Ina shirin shiga wanka na ji ana shelar ana son ganin dukkanin malaman da suka zo a ɗakin meeting da ke cikin makaranta da misalin ƙarfe takwas da rabi .
★Uncle Salem
Cikin kaɗaicin son kasancewa da Nafisa ya soma bijiro mata da sabbin abubuwan da za ta fahimci shi mijinta ne amma da dukkan alamu ya ga sam ita a iya uban kawai ta yi masa matsuguni.Jin ta kashe masa waya yayi tunanin kunya da kuma fushi ne yasa ta datse kiran,hakan yasa yayi ta jera mata su da ya ga ta ƙi ɗauka sai ya tura mata text tare da kashe wayar ya rungume pilow.Zuwa yanzu haƙurinsa da juriyarsa sun yi ƙasa sosai,yana matuƙar son kasancewa da ita a duk cikin sati ranar juma'a da asabar kawai a bai yin azumi duk don kare mutumcinsa.Sau ɗaya tak ya taɓa neman auren wata wacce dama ita ce take haukan sonsa,amma an zo yin auren aka fasa saboda bai da wani asali.
Idonsa sun kaɗa sun yi jajur saboda abu biyu da suka haɗe masa, feeling da kuma fushin Naf wanda a duniya in akwai abin da yake guje ma to bayansa yake shi yasa a kowane lokaci yake yi mata abin da take so.Ko da kuwa iyayenta sun so nuna masa illar gatan da yake yi mata sai ya ce musu har yanzu Naf yarinya ce.Sai dai a jiya da Daddy ya ce masa ya ci a ce ta tare da kuma yadda ya ga surarta cikin doguwar rigar da ta lafe jikinta duk ta fitar da shap ɗinta sai yake ji a ransa eh za ta iya ɗaukar nauyin buƙatarsa.
Juyi yayi ta yi a daren,da ya ga dai sam baccin ba fa zai zo ba sai ya miƙe ya je watso ruwa tare da zama kan dadduma yayi ta lazumi bayan raka'o'i biyu da yayi.Sai daf da asubah ya samu bacci,amma duk da haka ana kiran sallah sai da ya je masjid da ke nan cikin Company ya dawo ya ƙara komawa bacci.Bai farka ba sai wuraren ƙarfe goma na safiya,wani wankan ya sake tare da shirya wa cikin wando tree quater na sojawa da kuma rigarsa t-shirt ita ma ta kakin soja.Bai ɗora hulla ba ya dai saka farin gilashi kafin ya ɗauki key ɗin motarsa ta aiki da kuma wayarsa.Sai da ya fito a hanya ne ya kunna ta,bayan ya shiga mota ne ya ga saƙon cewa Nafisa ta so kiransa amma ba ta same shi ba.Ya ɗan saki murmushi yana jin zuciyarsa ta yi sanyi ko ba komai yana da tabbacin ta sauko daga fushin da take.Kiranta yayi har sau biyu,a na uku ne Inna A'i ta ɗauka ta shaida masa ta fita.
★ƘWARGWAM
Ko da na fito daga wanka tuni Inna A'i ta soya min dankali da kuma ƙwai,na yi zaune na ci na ƙoshi kafin na jawo kayan kwalliyata na shafa mai da turare har da hoda.Bayan nan na zaɓo doguwar riga ta tambaya ƴar côte d'ivoire,sosai ta amshe ni sai na zaɓo hijabi da jaka da kalmi duk waɗanda za su hau da ita.
Ina shirin fita ita ma Inna A'i ta fito daga kitchen hannunta riƙe da kwanon miya na jiya,ta ce “ ashe ba ki ci abincin nan ba dubi yadda duk yayi tsutsotsi ya lalace”
Na dubi cikin kwanon na ga babu kyawun gani manyan tsutsotsi ne ke ta yawo suna shige da fice cikin ragowar naman kajin.Da mamaki na ce “ amma kuma abincin har ya isa lalacewa haka?”
“ Ni ma haka na ce,ko ƙila zafi” Inna A'i ta faɗa .
Na ce “ kawai ki zubar ki wanke kwanukan sai ki mayar musu ,ga key nan in za ki fita ki rufe ɗakin na tafi sai na dawo”
“Allah ya tsare hanya”