Sashe 4
Fatalwar Deborah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ai ita ba ta laifi matar gwal ce,ina ce duk abin da ta yi daidai ne ta mayar da kai malaho sai abin da take so ake yi a gidan nan tana ƙaryar ita jinin sarauta ce an wani kawo bayi suna yi mata ayyukan da ita ce ta dace ta yi su.Ko kunya ba ta ji ƴan aiki ne ke yi wa mijinta girki yana ci ita kuma tana can tana yawon ta zubar tana gogayya da ƙatti da sunan aiki.To daga yau in dai ni ce uwarka to ya zama dole a kori bayin can daga gidan nan,a bar iya A'i”
“Mama kar ki manta Inna A'i ko can ba ƴar aiki ba ce,kuma Nafisa yarinya ce ba za ta iya yin ayyukan gidan nan ba ita ɗaya a bar ko mutum ɗaya ne sai ya dinga kama mata”
“Ba dai a cikin bayin Victoria Falls ba,ka sallame su ni nan da kaina zan nemo ma ƴar aiki ka tashi ka tafi Allah yi ma albarka”
Ya miƙe yana mai cewa “amen” kafin ya fice....
[27/02 02:52] MRS SADAUKI: *FATALWAR DEBORAH*🐲
MAKARANTAR MATSAFA 2 ☠️
```LoVe aNd HoRrOr story```👽
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}
*SADAUKARWA :* Ga malaman makaranta
*FCWA*☀️
________________________
06
Ina nan zaune tare da yara Uncle Salem ya fito,a yanayin fuskarsa kawai na fahimci ba abu mai daɗi ne Mama ta sanar da shi ba amma na basar na ci gaba da fitar da chocolat da ke cikin ledar da ya bani ina nunawa Abdallah shi kuma yana karanta sunayensu.
Bai ce komai ba yayi sama,ni ma na ƙi tanka shi na yi zamana dukkan sallolina ma a ɗakin Inna A'i na yi su har isha'i.Abinci kuwa kasa ci na yi sai su Abdallah da na saka gaba suka ci na kuma umarce su da su wuce can ɗakin kakarsu tun da a can suke kwana,na yi Inna A'i sallama na fito.
Tun da na soma taka step nake jin tamkar ana take min baya har wata guguwa-guguwa nake ji haɗi da wani numfashi kamar na kumurci,amma a haka na daure na haura sama direct kuma ɗakin Uncle na shiga.
Kiciɓis muka yi da shi ya fito daga bedroom ɗinsa ƙugunsa ɗaure da towel yana goge kuma sumar kansa da ɗan ƙarami.
Na ɗan ja ajiyar zuciya kafin na je na karɓi towel ɗin na zauna da shi ina goge masa ruwan.
“Naf!” ya faɗa can ƙasan maƙoshi,na ce “uhum!”
“Mu je ki yi wanka” ya faɗa tare da tashi tsaye ya ja ni muka shiga can uwar ɗaka,sai da yayi mana addu'a sannan muka shiga toilet ɗin.Ruwan ɗumi ya cika min bahon wankan da su na shige,sai a lokacin ya fita ya bar ni na soma wanka ina ayyana abubuwa da yawa a raina har na gama na fito ɗaure da towel ɗinsa.
Bayan na shafa lotion da turare na saka kayan baccin da ya fitar min,sai a lokacin ya rufe laptop ɗinsa yana tsokana ta.“A zo a sama wa Mohamed ƙanwa”
Murmushi kawai na yi , ya rungumo ni tare da ja na muka yi baya muka zube kan bed.“Wai kin san da ina mahaukacin son ki?” yayi min tambayar da bai bani damar basa amsa ba saboda bakinmu da haɗe wuri guda yana kissing a hankali kuma yake shafar cikina zuwa ƙasa.Dakyar na aro jarumtar fitar da duk damuwata na ajiye hankali muka faranta ran juna,a yau ma Uncle ya ƙara dasa min wani sonsa na musamman a zuciya .A ɗan kunyace na yunƙura zan tashi amma ya mayar da ni tare da yi min raɗa a kunne,a shagwaɓe na daki ƙirjinsa na ce “uncle kana ƙara girma amma kana abubuwan yara” wata shu'umar dariya yayi ya ce “au kar dai a ce kallon tsoho kike yi min? Baby duka nawa nake da ba zan kasance da ke sau biyu ba?”
“Ni dai a bar ni na huta bacci nake ji” na faɗa ina ƙara ƙoƙarin tashi amma ya ɗora hannunsa kan cikina yana mai cewa “ki jira na haɗo miki lafiyayen abinci dai baby sai ki ji ƙarfin kula da mijinki”
Yana gama faɗar haka ya tashi ya kimtsa tare da fita,ni kuwa na lafe cikin blanket ina murmushi.
Uncle Salem kuwa shi kansa yunwar yake ji don kalaman Mama kasa barinsa sukuni suka yi ballantana har yayi tunanin cin abinci.
Ƙasa ya sauka tare da shiga kitchen,tray ya samu ya soma ɗora duk abin da za su ci yana tsaka da yin aikin gabansa Mama ta shigo hannunta riƙe da na Abidah.
A ɗan kunyace ya ce “Mama fitowa kika yi?”
“Eh Abidah ce tace min yunwa take ji shi ne na zo kitchen don sama mata abin da za ta ci” ita ma Mamar ta faɗa tana mai kallon trayn da ya zuba fruits kamar yadda Abidah ke kallo.
Shi kuwa ƙaramin plate ya samu ya soma yayanka mata yana mai farawa da Bismillah kamar yadda abin ya zame masa jiki babu abin da zai yi ba tare da ya ambaci sunan Allah ba.
Yana miƙawa Abidah amma ta ƙi karɓa a ƙarshe ma dai cewa ta yi ba ta jin yunwar,da Mama ta kama hannunta don su koma sai ta tsira kuka tana mai cewa “ni wurin Abba zan tafi”
Uncle kuwa sanin halin da ya baro Nafisa ,sannan da wanda shi kansa yake ciki na larurarsa sai ya kuwa ya murje ido ya ce “Mama ki tafi da ita ki rarrashe ta za ta bari,Abidar Mama ki bar kuka kin ji ko ? Gobe zan saya miki zuma” ya faɗi haka ne saboda duk rigimar da take in ambaci zuma tana yin shuru.
Da wani irin kallo Abidah ta bi bayan Uncle,wanda kuma a zahiri ba ita ce ɗin ba ruhin DEBORAH ne ke juya gangar jikinta.Ta so ace ya tafi da ita can ɗakin don hana shi ƙara kusantar Nafisa,amma babu yadda ta iya dole ta haƙura ta bi Mama.
Ina nan yadda ya bar ni ya shigo,jikinsa har rawa yake kamar kullum muddin dai yana da buƙatar kasancewa da ni to duk wani control rasa shi yake.
Fruits ya soma ciyar da mu,sai ya saka a bakinsa yana ɗura min kamar wasu tantabaru ko kuma ya saka a bakina sai ya dinga sha yana gamawa da sumbata ta a haka muka ƙara shiga wani shauƙin soyayyar muka samawa juna nutsuwa a karo na biyu.Duk yadda na so kuma na kwanta bacci Uncle bai bari na zauna da najasa ba sai da muka tsabtace jikinmu,a shagwaɓe nake yi masa mita sai ya ce “Baby babu kyau fa kwana da janaba,in mutum bai iya yin wanka to Manzon rahama ya ce ko alwala ce ka yi kafin ka kwanta don nisanta kanka daga sheɗanu”
Ambatar sheɗanu da yayi shi ya dawo min da tashin hankalin ɗazu na gamdakatar da na yi da FATALWAR DEBORAH,cike da tsoro na ƙanƙame shi ina shigewa ƙirjinsa haɗi da ɓoye fuskata shi kuwa karatu na ji ya soma yi min yana min wata irin shafa wacce ta mayar da tsikar jikina da ta tashi.
A hankali na soma lumshe ido saboda karatun da yake yi min yana kashe min jiki ne ruhina na yin wani sanyi liƙis,ko gama ida rufe ido ban yi ba na ga Deborah a tsaye a cikin mafarkina ta yi kicin-cikin da fuska,ba ta kuma ɗauki dogon lokaci ba ta shaƙe min wuya....
[27/02 15:49] MRS SADAUKI: *FATALWAR DEBORAH*🐲
MAKARANTAR MATSAFA 2 ☠️
```LoVe aNd HoRrOr story```👽
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}
*SADAUKARWA :* Ga malaman makaranta
*FCWA*☀️
________________________
07
Ko a cikin miyagu ita Deborah ƙarshe ce wurin iya mugunta,na sha jin labaranta a cikin littafin sirrin Kakata Ayodele na MUTUWARE.Wannan yasa ban ma ɓata wa kaina lokaci ba wurin ƙwatar kaina ta ƙarfi ba,sai dai furucin baki wanda nake feso ayoyin Alkur'ani duk wacce ta zo min wata ma ko ƙarshen ayar ban kai wa nake kamo wata.Amma tsabar taurin rai na fatalwa haka ta daure azabar da nake yi mata domin kuwa karatun Alkur'ani na ƙona ruhinta ne kamar yadda yake ƙona jinnu.
Cikin ikon Allah dai na samu na ci galaba a kanta ta bari na tashi daga baƙin baccin nan.Kan fuskar Uncle na sauke idona wanda ke sharar bacci,a hankali na sauka daga bed ɗin na nufi farantin da ya shigo mana shi don ɗaukar ruwa na sha sai dai ina taɓa gorar da hannuna nan take ruwan suka ƙwafe ki ɗigo ɗaya babu alhalin da idona na gansu.
Ƙishi nake ji sosai,maƙoshina ya bushe kamar wacce ba ta taɓa shan ruwa ba.Don dole na zura hijabi tare da fitowa,wani abin mamaki ne ya faru da ni,a daidai lokacin da na sauke ƙafata daga step ɗin ƙarshe sai duk ƙwayaƙwayin lantarki suka fara disashewa suna wani lummm kamar rana za ta faɗi,ko kafin ƙyaftawar ido kuma suka dinga tarwatsewa ji kake tatatseeee ! Rasss! Duk sun mutu ɗakin ya dawo baƙi ƙirin ko tafin hannuna ban iya gani,iska ne ya soma kaɗawa a hankali-a hankali kafin kuma ƙofae fita falo ta yi wani ƙiiii ta buɗe kanta daidai nan wata murya irin kamar ta wanda ya ɓata ta soma kiran sunana.
“Naf? Naf zo gare ni! Naf zo mana za su tafi da ni” muryar da na ajiye hankali sai na ji ta Uncle ce,kamar wacce ake yi wa jagora haka na soma bin wani hasken jar wutar kyandir har na fita daga gidan baki ɗaya.Tafiyar ƙasa na soma yi a cikin duhun sararin samaniya wanda ya ɗauki wani yanayi kamar lokacin damina,duk taurari sun ɓata sai giza-gizai ke faman gudu.
Ba zan iya cewa ga iya adadin lokacin da na ɗauka ina tafiya ba,ni dai kawai na gan ni a bakin ƙofar shiga wani jeji ina dab da saka ƙafata ciki na ji an jawo ni ta baya.Sai a lokacin kawai tunanina ya dawo jikina,a tsorace na juyo ina kallon shi.Farin dattijo ne wanda a ƙalla zai kai shekara ɗari da wasu ƴan kai.
“Me ya kawo ki wannan wuri?” ya jefo min tambaya cikin wani yare wanda ba nawa ba amma tabbas na fahimci me ya ce.
Samun bakina na yi da irin nasa Yaren na ce “ina ne nan?”
“Mama kar ki manta Inna A'i ko can ba ƴar aiki ba ce,kuma Nafisa yarinya ce ba za ta iya yin ayyukan gidan nan ba ita ɗaya a bar ko mutum ɗaya ne sai ya dinga kama mata”
“Ba dai a cikin bayin Victoria Falls ba,ka sallame su ni nan da kaina zan nemo ma ƴar aiki ka tashi ka tafi Allah yi ma albarka”
Ya miƙe yana mai cewa “amen” kafin ya fice....
[27/02 02:52] MRS SADAUKI: *FATALWAR DEBORAH*🐲
MAKARANTAR MATSAFA 2 ☠️
```LoVe aNd HoRrOr story```👽
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}
*SADAUKARWA :* Ga malaman makaranta
*FCWA*☀️
________________________
06
Ina nan zaune tare da yara Uncle Salem ya fito,a yanayin fuskarsa kawai na fahimci ba abu mai daɗi ne Mama ta sanar da shi ba amma na basar na ci gaba da fitar da chocolat da ke cikin ledar da ya bani ina nunawa Abdallah shi kuma yana karanta sunayensu.
Bai ce komai ba yayi sama,ni ma na ƙi tanka shi na yi zamana dukkan sallolina ma a ɗakin Inna A'i na yi su har isha'i.Abinci kuwa kasa ci na yi sai su Abdallah da na saka gaba suka ci na kuma umarce su da su wuce can ɗakin kakarsu tun da a can suke kwana,na yi Inna A'i sallama na fito.
Tun da na soma taka step nake jin tamkar ana take min baya har wata guguwa-guguwa nake ji haɗi da wani numfashi kamar na kumurci,amma a haka na daure na haura sama direct kuma ɗakin Uncle na shiga.
Kiciɓis muka yi da shi ya fito daga bedroom ɗinsa ƙugunsa ɗaure da towel yana goge kuma sumar kansa da ɗan ƙarami.
Na ɗan ja ajiyar zuciya kafin na je na karɓi towel ɗin na zauna da shi ina goge masa ruwan.
“Naf!” ya faɗa can ƙasan maƙoshi,na ce “uhum!”
“Mu je ki yi wanka” ya faɗa tare da tashi tsaye ya ja ni muka shiga can uwar ɗaka,sai da yayi mana addu'a sannan muka shiga toilet ɗin.Ruwan ɗumi ya cika min bahon wankan da su na shige,sai a lokacin ya fita ya bar ni na soma wanka ina ayyana abubuwa da yawa a raina har na gama na fito ɗaure da towel ɗinsa.
Bayan na shafa lotion da turare na saka kayan baccin da ya fitar min,sai a lokacin ya rufe laptop ɗinsa yana tsokana ta.“A zo a sama wa Mohamed ƙanwa”
Murmushi kawai na yi , ya rungumo ni tare da ja na muka yi baya muka zube kan bed.“Wai kin san da ina mahaukacin son ki?” yayi min tambayar da bai bani damar basa amsa ba saboda bakinmu da haɗe wuri guda yana kissing a hankali kuma yake shafar cikina zuwa ƙasa.Dakyar na aro jarumtar fitar da duk damuwata na ajiye hankali muka faranta ran juna,a yau ma Uncle ya ƙara dasa min wani sonsa na musamman a zuciya .A ɗan kunyace na yunƙura zan tashi amma ya mayar da ni tare da yi min raɗa a kunne,a shagwaɓe na daki ƙirjinsa na ce “uncle kana ƙara girma amma kana abubuwan yara” wata shu'umar dariya yayi ya ce “au kar dai a ce kallon tsoho kike yi min? Baby duka nawa nake da ba zan kasance da ke sau biyu ba?”
“Ni dai a bar ni na huta bacci nake ji” na faɗa ina ƙara ƙoƙarin tashi amma ya ɗora hannunsa kan cikina yana mai cewa “ki jira na haɗo miki lafiyayen abinci dai baby sai ki ji ƙarfin kula da mijinki”
Yana gama faɗar haka ya tashi ya kimtsa tare da fita,ni kuwa na lafe cikin blanket ina murmushi.
Uncle Salem kuwa shi kansa yunwar yake ji don kalaman Mama kasa barinsa sukuni suka yi ballantana har yayi tunanin cin abinci.
Ƙasa ya sauka tare da shiga kitchen,tray ya samu ya soma ɗora duk abin da za su ci yana tsaka da yin aikin gabansa Mama ta shigo hannunta riƙe da na Abidah.
A ɗan kunyace ya ce “Mama fitowa kika yi?”
“Eh Abidah ce tace min yunwa take ji shi ne na zo kitchen don sama mata abin da za ta ci” ita ma Mamar ta faɗa tana mai kallon trayn da ya zuba fruits kamar yadda Abidah ke kallo.
Shi kuwa ƙaramin plate ya samu ya soma yayanka mata yana mai farawa da Bismillah kamar yadda abin ya zame masa jiki babu abin da zai yi ba tare da ya ambaci sunan Allah ba.
Yana miƙawa Abidah amma ta ƙi karɓa a ƙarshe ma dai cewa ta yi ba ta jin yunwar,da Mama ta kama hannunta don su koma sai ta tsira kuka tana mai cewa “ni wurin Abba zan tafi”
Uncle kuwa sanin halin da ya baro Nafisa ,sannan da wanda shi kansa yake ciki na larurarsa sai ya kuwa ya murje ido ya ce “Mama ki tafi da ita ki rarrashe ta za ta bari,Abidar Mama ki bar kuka kin ji ko ? Gobe zan saya miki zuma” ya faɗi haka ne saboda duk rigimar da take in ambaci zuma tana yin shuru.
Da wani irin kallo Abidah ta bi bayan Uncle,wanda kuma a zahiri ba ita ce ɗin ba ruhin DEBORAH ne ke juya gangar jikinta.Ta so ace ya tafi da ita can ɗakin don hana shi ƙara kusantar Nafisa,amma babu yadda ta iya dole ta haƙura ta bi Mama.
Ina nan yadda ya bar ni ya shigo,jikinsa har rawa yake kamar kullum muddin dai yana da buƙatar kasancewa da ni to duk wani control rasa shi yake.
Fruits ya soma ciyar da mu,sai ya saka a bakinsa yana ɗura min kamar wasu tantabaru ko kuma ya saka a bakina sai ya dinga sha yana gamawa da sumbata ta a haka muka ƙara shiga wani shauƙin soyayyar muka samawa juna nutsuwa a karo na biyu.Duk yadda na so kuma na kwanta bacci Uncle bai bari na zauna da najasa ba sai da muka tsabtace jikinmu,a shagwaɓe nake yi masa mita sai ya ce “Baby babu kyau fa kwana da janaba,in mutum bai iya yin wanka to Manzon rahama ya ce ko alwala ce ka yi kafin ka kwanta don nisanta kanka daga sheɗanu”
Ambatar sheɗanu da yayi shi ya dawo min da tashin hankalin ɗazu na gamdakatar da na yi da FATALWAR DEBORAH,cike da tsoro na ƙanƙame shi ina shigewa ƙirjinsa haɗi da ɓoye fuskata shi kuwa karatu na ji ya soma yi min yana min wata irin shafa wacce ta mayar da tsikar jikina da ta tashi.
A hankali na soma lumshe ido saboda karatun da yake yi min yana kashe min jiki ne ruhina na yin wani sanyi liƙis,ko gama ida rufe ido ban yi ba na ga Deborah a tsaye a cikin mafarkina ta yi kicin-cikin da fuska,ba ta kuma ɗauki dogon lokaci ba ta shaƙe min wuya....
[27/02 15:49] MRS SADAUKI: *FATALWAR DEBORAH*🐲
MAKARANTAR MATSAFA 2 ☠️
```LoVe aNd HoRrOr story```👽
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}
*SADAUKARWA :* Ga malaman makaranta
*FCWA*☀️
________________________
07
Ko a cikin miyagu ita Deborah ƙarshe ce wurin iya mugunta,na sha jin labaranta a cikin littafin sirrin Kakata Ayodele na MUTUWARE.Wannan yasa ban ma ɓata wa kaina lokaci ba wurin ƙwatar kaina ta ƙarfi ba,sai dai furucin baki wanda nake feso ayoyin Alkur'ani duk wacce ta zo min wata ma ko ƙarshen ayar ban kai wa nake kamo wata.Amma tsabar taurin rai na fatalwa haka ta daure azabar da nake yi mata domin kuwa karatun Alkur'ani na ƙona ruhinta ne kamar yadda yake ƙona jinnu.
Cikin ikon Allah dai na samu na ci galaba a kanta ta bari na tashi daga baƙin baccin nan.Kan fuskar Uncle na sauke idona wanda ke sharar bacci,a hankali na sauka daga bed ɗin na nufi farantin da ya shigo mana shi don ɗaukar ruwa na sha sai dai ina taɓa gorar da hannuna nan take ruwan suka ƙwafe ki ɗigo ɗaya babu alhalin da idona na gansu.
Ƙishi nake ji sosai,maƙoshina ya bushe kamar wacce ba ta taɓa shan ruwa ba.Don dole na zura hijabi tare da fitowa,wani abin mamaki ne ya faru da ni,a daidai lokacin da na sauke ƙafata daga step ɗin ƙarshe sai duk ƙwayaƙwayin lantarki suka fara disashewa suna wani lummm kamar rana za ta faɗi,ko kafin ƙyaftawar ido kuma suka dinga tarwatsewa ji kake tatatseeee ! Rasss! Duk sun mutu ɗakin ya dawo baƙi ƙirin ko tafin hannuna ban iya gani,iska ne ya soma kaɗawa a hankali-a hankali kafin kuma ƙofae fita falo ta yi wani ƙiiii ta buɗe kanta daidai nan wata murya irin kamar ta wanda ya ɓata ta soma kiran sunana.
“Naf? Naf zo gare ni! Naf zo mana za su tafi da ni” muryar da na ajiye hankali sai na ji ta Uncle ce,kamar wacce ake yi wa jagora haka na soma bin wani hasken jar wutar kyandir har na fita daga gidan baki ɗaya.Tafiyar ƙasa na soma yi a cikin duhun sararin samaniya wanda ya ɗauki wani yanayi kamar lokacin damina,duk taurari sun ɓata sai giza-gizai ke faman gudu.
Ba zan iya cewa ga iya adadin lokacin da na ɗauka ina tafiya ba,ni dai kawai na gan ni a bakin ƙofar shiga wani jeji ina dab da saka ƙafata ciki na ji an jawo ni ta baya.Sai a lokacin kawai tunanina ya dawo jikina,a tsorace na juyo ina kallon shi.Farin dattijo ne wanda a ƙalla zai kai shekara ɗari da wasu ƴan kai.
“Me ya kawo ki wannan wuri?” ya jefo min tambaya cikin wani yare wanda ba nawa ba amma tabbas na fahimci me ya ce.
Samun bakina na yi da irin nasa Yaren na ce “ina ne nan?”