Sashe 6
Ba Kai Nake So Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suma suka mara mata baya.
“ Bobo me ya kawo ka nan da daddaren nan?.”
Numfashi ya sauƙe yana cewa. “ Guyinta fa nazo shi ne take mun yanga.”
“ Me zaka yi a gurinta din?.”
“ Dama…. Wait me ɗinka ce ita? A iya sanina da kai Man baka da ƙanwa bayan Yasmeen, to su kuma waɗan nan fa?.”
“ Uhmm sisters from another Mama.”
Gira ya ɗaga masa alamun yana son ƙarin bayani, amma sai ya mantar dashi yana cewa. “ Mu shiga ciki mana.”
“ No zan tafi.” Ya yi maganar yana zagayawa ya shiga motansa tare da tayarwa ya bar unguwan.
Mansoor ya daɗe a gurin kafin ya shiga ciki yana wucewa ɗakinsa.
“ Wai Meerah yaushe kika koma mara kunya ce? Yaushe kika fara magana? Kinsan waye wanda kika yiwa wannan rashin kunyar kuwa? Kinsan shi din waye ne a garin nan?.” Meemah ce ke mata masifa cikin ɗaga murya.
Ɗago da manya idanunta ta yi tana watsa mata tare da jan kuntun tsaki tana cewa. “ Ke kika san ko shi waye, da sanin shi da rashin sanin shi duk daya ne a gurina; sannan ya zama first and last da za ki ɗagamun murya idan kina min magana.”
“ Ni kike fadawa haka Meerah?.” Ko kallon arziki bata mata ba.
Cigaba da magana Meemah ta yi tana jijjiga kai. “ Shikenan bazan sake shiga rayuwar ki ba, kiyi duk abunda kika ga dama amma kina sanin cewa mu din marayu ne bamu da wani gata bayan Allah, sannan wulaƙanta mutum sam ba abu me kyau bane.”
“ Ni babu wanda na wulakanta Malama kuma ki dena ɗaga mun murya.”
Cikin haushi Meemah ke magana. “ An ɗaga din Meerah har ke waye da baza’a faɗa miki gaskiya ba.”
“ Bana so ki dena ɗaga mun murya, bana son jin gaskiyar.”
“ Kowa kin mai dashi sa’anki da zarar an miki magana sai yiwa mutum tsaki ko ki harare shi saboda rashin kunya, to Wallahi tallahi idan baki daina ba babu ni babu ke.”
“ Sai me idan babu ni babu ke din? Ce miki akayi mutuwa zanyi? Tun muna shekara tara iyayen mu suka rasu babu wanda ya taimaka mana har muka girma, shin na mutu? kuɗin Makarantarmu da wahala muka biya dan kawai mu samu ilili, wanke wanke da bauta babu wanda bamu yi ba saboda mu tsira da mutuncin mu, an kira mu da karuwai mun toshe kunne, an ce mana muna bin maza mun toshe kunne, an mana sharrin sata ko wani iri shima mun toshe kunne, dan yau an taimaka mana shine kike cewa za ki rabu dani Meemah? To dan Allah idan kin ki rabuwa dani baki cika mace ba.”
“ Wai dan Allah ku bar cacan bakin nan mana, sai kace ba ciki daya kuka fito ba.” A cewar Yasmeen wacce tun ɗazu take kallon su.
“ Uhm Meerah ke nan Allah ya shirye ki to, bazan tsaya yin cacan baki da ke ba.” Da haka ta hau kan gado tana jan bargo ta rufe har fuskarta.
Shuru Meerah tayi tana samun guri ta zauna, tunani ta fara yi tun suna yara ko hararan junan su basu taɓa yi ba, amma sai gashi yau akan wani chan daban suna cacan baki har da furtawa juna ɗaci.
Tuƙi ya ke yi hankalinsa gaba daya baya jikinsa, duk ya rasa mai yake damun shi, duk da ya kunna AC din motan hakan bai hana shi haɗa zufa ba; in banda taimakon Allah da bazai isa gida lafiya ba.
Yana parking direct part nashi ya wuce, yana shiga ya saka key ya koma ya zauna yana tunani, wayan shi ya ciro ya danna wani number bugu daya aka ɗauka.
“ Zan tuya maka wani photo da address din gidan da komai, nan da gobe inaso na kwana da ita.”
“ Ok Sir.”
Da haka ya datsai kiran yana sauke numfashi tare da furzar da iska mai haɗe da bacin rai, tashi yayi ya wuce toilet ya watsa ruwa ya dawo ya shirya cikin wani jallabiya blue wanda ya amshi fatar jikinsa.
Laptop ya ɗauka ya fara aiki dan yanaso ya sauƙe sabon waƙa kwanan nan, amma yana yi ne hankalinsa duk baya jikinsa, ganin hakan ne yasa ya ajiye kawai ya hau kan gado da zummar bacci, amma bacci bai ɗauke shi ba.
A daren ranar kusan mutane hudu basu yi bacci ba, Meerah da duk tunanin duniya ya isheta sai Meemah dake tunanin sauyawan ƴar uwarta ta, Mansoor kuma yana tunanin me ke tsakanin abokinsa da ita, shi kuma Alyan yana tunanin rashin mutuncin da zai aikata gobe.
Washe gari da safe, dama Mama ta rabawa kowa girki kuma yau ranar girkin Meemah ce hakan yasa ta tashi da sauri ta yi breakfast, a daining table ta kai ta jera tabi kowa ta tada shi har Mansoor.
Bayan kowa ya hallara ne aka fara cin abinci, amma kallo daya zakawa gurin ka gane ba kwanciyar hankali a wajen.
Duban kowa Mama tayi kafin ta ce. “ Ya naga kowa sai juya chokali yake? Ko akwai abunda ya faru ne ban sani ba?.”
Shuru kowa ya yi sai ma tsayawar da sukayi da juya chokalin, sake tambayan su ta yi. “ Akwai abunda ya faru ne Mansoor?.”
Da sauri ya ce. “ No Mama babu abunda ya faru.” Duba agogon hannunsa yayi gani har 8 tayi yasa ya tashi yana cewa. “ Mama bari naje ina da patients dayawa.” Da haka ya zame, Mama tana binshi da Allah ya tsare.
Mai da kallonta tayi izuwa ga su, da sauri Meemah ta miƙe tana cewa. “ Mama nima bari naje nayi late.” Da haka ta fice da sauri, gurin ya rage Yasmeen da Meerah sai Mama.
“ Meerah me ya faru ne?.” A cewar Mama.
Kanta a sunkuye ta ce. “ Bakomai Mamma.”
“ Me sa yau ba za kije aiki ba?.”
“ Zan nema a wani guri ne, na gaji da nan din.”
“ An miki wani abu ne?.”
“ A’a.” Ta faɗa a hankali.
“ Amma kin tabbata babu abunda yake damunki?.” Mama ta kuma tambayar ta cike da nuna kulawa.
“ Babu Mamma.”
“ Shikenan Allah ya sa hakane yafi Alkhairi.”
“ Amin.” Da haka kowa ya watse.
*COMPANY*
Meemah tana bud’e office Jameel ya tashi da sauri ya fice, da kallo ta bishi tana isa gurin zamanta ta zauna tare da fito dasu kayan aikinta ta soma aiki; tana cikin yin aikin ne ya dawo fuska ba annuri yana kallon ta.
Ita ma shi ta kallo tana gaishe da shi.
“ Bar gaisuwar a gefe, ina ƴar uwarki ne?.”
“ Ta ajiye aikin.”
Tsabar furgici sai da zuciyarsa ta tsinke wanda ya bayyana akan fuskansa, har sauri yake gurin cewa. “ Laifi aka mata ne? Ko ni ne na mata bansani ba?.”
“ Ni ma bansan dalili ba haka kawai ta ce ta daina zuwa.”
“ Ya Subhanallah, na shiga uku.”
Kallon tausayi kawai Meemah ta masa dan tasan indai Meerah ce yanzu ya fara.
Tun safe daya dawo daga sallan asuba bai sauƙo ƙasa ba, 𝐀𝐦𝐦𝐲 ta tura Laylerh amma ƙofar a datsai, da ta ƙwanƙwaso ya daka mata uban tsawa wanda yasa ta gudu, da 𝐀𝐦𝐦𝐲 taje bai buɗe ba sai ma cewa da yayi tayi hakuri zuwa anjima zai sauƙo.
Yana kwance akan gado yayi rub da ciki daga shi sai boxer, kuraren karfe biyu da mintuna talatin da uku wayansa ta buga ƙara,,, dama tun dazu kiran yake jira hakan yasa ba shiri ya ɗaga ya manna a kunne.
“ Sir done.” Wani kafurin murmushi ya sake yana kashe wayan ya tashi, sauri sauri ya shirya cikin shadda dark brown, ya taje gashin kansa wanda yake ta yalki ya ɗauki takalmi black ya saka, yana ɗaura agogo ya fashe jikinsa da turaruka masu kamshi, kafin ya buɗe ƙofan ɗakin ya fice da sauri babu wanda ya ganshi.
Bodyguard na hango shi suka tashi, hannu kawai ya ɗaga musu daya daga cikinsu ya miƙa masa key din mota, buɗe motan yayi ya shiga fuskansa ɗauke da murmushi, da haka aka buɗe masa get one ya fice, get two ma aka wangale masa ya fice a 360 yana murmushi yana shafa sajansa.
Sanye take cikin abaya brown wanda yasha adon stones, tayi rolling din kanta da mayafin abayar saboda babba ne ba ƙarami ba, dan har ya rufe bayanta.
Bayan ta fito daga shogon ne ta tsaya a bakin titi tana jiran machine, ga zafin rana ga wajen shuru babu mutane, da badan tana buk’atar taci biscuit ba, da yau baza ta fito ba.
Jin kamar an tsaya a bayanta ne, yasa ta juya dan ganin waye ne, watsa mata abu akayi a fuska ana sakata a mota, da sauri suka bar gurin.
*2 hours later*
A hankali ta soma buɗe idanunta waɗan da suka mata nauyi sosai, kafin daga bisani ta buɗe su duka tana bin gurin da kallo, ba shiri ta diro daga kan gadon da take tana bin ɗakin da kallon mamaki.
Jin ana k’ok’arin buɗe ƙofa ne yasa ta juyo da sauri tana jiran taga waye zai fito, a razane taja baya da sauri tana kare masa kallo mai cike da tuhuma….
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
7- *💅BA KAI NAKE SO BA💅*
_The story is all about love, romantic, sacrifice, heartbreak and destiny_
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*FATIMA ISA MANU💐*
*( DR TEEMAH)🦋🕊*
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
________________________________
Masu neman littafin *BA KAI NAKE SO BA* daga farko tare da sauran littafina zaku iya following channel ɗi na dan samu👇https://whatsapp.com/channel/0029Vaf6CpQDuMRYD1FMD92T
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IKUcfCN5rPQ9o0CaBtB2qP
___________________________________
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️*
____________________________________
*DIAMOND 💎 STAR ⭐*
*LADIES🧝♀️🧝♀️🧝♀️*
*(We stand together)*
🤝🤝🤝
___________________________________
*GARGADI*
Wannan littafin ƙagaggen labari ne, ban yarda wani ko wata ya sauya min shi ba ta kowace siga, sannan kuma ban amince a dauramin shi a youtube ba tare da izini na ba.
*BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫*
*P.7*
“ Bobo me ya kawo ka nan da daddaren nan?.”
Numfashi ya sauƙe yana cewa. “ Guyinta fa nazo shi ne take mun yanga.”
“ Me zaka yi a gurinta din?.”
“ Dama…. Wait me ɗinka ce ita? A iya sanina da kai Man baka da ƙanwa bayan Yasmeen, to su kuma waɗan nan fa?.”
“ Uhmm sisters from another Mama.”
Gira ya ɗaga masa alamun yana son ƙarin bayani, amma sai ya mantar dashi yana cewa. “ Mu shiga ciki mana.”
“ No zan tafi.” Ya yi maganar yana zagayawa ya shiga motansa tare da tayarwa ya bar unguwan.
Mansoor ya daɗe a gurin kafin ya shiga ciki yana wucewa ɗakinsa.
“ Wai Meerah yaushe kika koma mara kunya ce? Yaushe kika fara magana? Kinsan waye wanda kika yiwa wannan rashin kunyar kuwa? Kinsan shi din waye ne a garin nan?.” Meemah ce ke mata masifa cikin ɗaga murya.
Ɗago da manya idanunta ta yi tana watsa mata tare da jan kuntun tsaki tana cewa. “ Ke kika san ko shi waye, da sanin shi da rashin sanin shi duk daya ne a gurina; sannan ya zama first and last da za ki ɗagamun murya idan kina min magana.”
“ Ni kike fadawa haka Meerah?.” Ko kallon arziki bata mata ba.
Cigaba da magana Meemah ta yi tana jijjiga kai. “ Shikenan bazan sake shiga rayuwar ki ba, kiyi duk abunda kika ga dama amma kina sanin cewa mu din marayu ne bamu da wani gata bayan Allah, sannan wulaƙanta mutum sam ba abu me kyau bane.”
“ Ni babu wanda na wulakanta Malama kuma ki dena ɗaga mun murya.”
Cikin haushi Meemah ke magana. “ An ɗaga din Meerah har ke waye da baza’a faɗa miki gaskiya ba.”
“ Bana so ki dena ɗaga mun murya, bana son jin gaskiyar.”
“ Kowa kin mai dashi sa’anki da zarar an miki magana sai yiwa mutum tsaki ko ki harare shi saboda rashin kunya, to Wallahi tallahi idan baki daina ba babu ni babu ke.”
“ Sai me idan babu ni babu ke din? Ce miki akayi mutuwa zanyi? Tun muna shekara tara iyayen mu suka rasu babu wanda ya taimaka mana har muka girma, shin na mutu? kuɗin Makarantarmu da wahala muka biya dan kawai mu samu ilili, wanke wanke da bauta babu wanda bamu yi ba saboda mu tsira da mutuncin mu, an kira mu da karuwai mun toshe kunne, an ce mana muna bin maza mun toshe kunne, an mana sharrin sata ko wani iri shima mun toshe kunne, dan yau an taimaka mana shine kike cewa za ki rabu dani Meemah? To dan Allah idan kin ki rabuwa dani baki cika mace ba.”
“ Wai dan Allah ku bar cacan bakin nan mana, sai kace ba ciki daya kuka fito ba.” A cewar Yasmeen wacce tun ɗazu take kallon su.
“ Uhm Meerah ke nan Allah ya shirye ki to, bazan tsaya yin cacan baki da ke ba.” Da haka ta hau kan gado tana jan bargo ta rufe har fuskarta.
Shuru Meerah tayi tana samun guri ta zauna, tunani ta fara yi tun suna yara ko hararan junan su basu taɓa yi ba, amma sai gashi yau akan wani chan daban suna cacan baki har da furtawa juna ɗaci.
Tuƙi ya ke yi hankalinsa gaba daya baya jikinsa, duk ya rasa mai yake damun shi, duk da ya kunna AC din motan hakan bai hana shi haɗa zufa ba; in banda taimakon Allah da bazai isa gida lafiya ba.
Yana parking direct part nashi ya wuce, yana shiga ya saka key ya koma ya zauna yana tunani, wayan shi ya ciro ya danna wani number bugu daya aka ɗauka.
“ Zan tuya maka wani photo da address din gidan da komai, nan da gobe inaso na kwana da ita.”
“ Ok Sir.”
Da haka ya datsai kiran yana sauke numfashi tare da furzar da iska mai haɗe da bacin rai, tashi yayi ya wuce toilet ya watsa ruwa ya dawo ya shirya cikin wani jallabiya blue wanda ya amshi fatar jikinsa.
Laptop ya ɗauka ya fara aiki dan yanaso ya sauƙe sabon waƙa kwanan nan, amma yana yi ne hankalinsa duk baya jikinsa, ganin hakan ne yasa ya ajiye kawai ya hau kan gado da zummar bacci, amma bacci bai ɗauke shi ba.
A daren ranar kusan mutane hudu basu yi bacci ba, Meerah da duk tunanin duniya ya isheta sai Meemah dake tunanin sauyawan ƴar uwarta ta, Mansoor kuma yana tunanin me ke tsakanin abokinsa da ita, shi kuma Alyan yana tunanin rashin mutuncin da zai aikata gobe.
Washe gari da safe, dama Mama ta rabawa kowa girki kuma yau ranar girkin Meemah ce hakan yasa ta tashi da sauri ta yi breakfast, a daining table ta kai ta jera tabi kowa ta tada shi har Mansoor.
Bayan kowa ya hallara ne aka fara cin abinci, amma kallo daya zakawa gurin ka gane ba kwanciyar hankali a wajen.
Duban kowa Mama tayi kafin ta ce. “ Ya naga kowa sai juya chokali yake? Ko akwai abunda ya faru ne ban sani ba?.”
Shuru kowa ya yi sai ma tsayawar da sukayi da juya chokalin, sake tambayan su ta yi. “ Akwai abunda ya faru ne Mansoor?.”
Da sauri ya ce. “ No Mama babu abunda ya faru.” Duba agogon hannunsa yayi gani har 8 tayi yasa ya tashi yana cewa. “ Mama bari naje ina da patients dayawa.” Da haka ya zame, Mama tana binshi da Allah ya tsare.
Mai da kallonta tayi izuwa ga su, da sauri Meemah ta miƙe tana cewa. “ Mama nima bari naje nayi late.” Da haka ta fice da sauri, gurin ya rage Yasmeen da Meerah sai Mama.
“ Meerah me ya faru ne?.” A cewar Mama.
Kanta a sunkuye ta ce. “ Bakomai Mamma.”
“ Me sa yau ba za kije aiki ba?.”
“ Zan nema a wani guri ne, na gaji da nan din.”
“ An miki wani abu ne?.”
“ A’a.” Ta faɗa a hankali.
“ Amma kin tabbata babu abunda yake damunki?.” Mama ta kuma tambayar ta cike da nuna kulawa.
“ Babu Mamma.”
“ Shikenan Allah ya sa hakane yafi Alkhairi.”
“ Amin.” Da haka kowa ya watse.
*COMPANY*
Meemah tana bud’e office Jameel ya tashi da sauri ya fice, da kallo ta bishi tana isa gurin zamanta ta zauna tare da fito dasu kayan aikinta ta soma aiki; tana cikin yin aikin ne ya dawo fuska ba annuri yana kallon ta.
Ita ma shi ta kallo tana gaishe da shi.
“ Bar gaisuwar a gefe, ina ƴar uwarki ne?.”
“ Ta ajiye aikin.”
Tsabar furgici sai da zuciyarsa ta tsinke wanda ya bayyana akan fuskansa, har sauri yake gurin cewa. “ Laifi aka mata ne? Ko ni ne na mata bansani ba?.”
“ Ni ma bansan dalili ba haka kawai ta ce ta daina zuwa.”
“ Ya Subhanallah, na shiga uku.”
Kallon tausayi kawai Meemah ta masa dan tasan indai Meerah ce yanzu ya fara.
Tun safe daya dawo daga sallan asuba bai sauƙo ƙasa ba, 𝐀𝐦𝐦𝐲 ta tura Laylerh amma ƙofar a datsai, da ta ƙwanƙwaso ya daka mata uban tsawa wanda yasa ta gudu, da 𝐀𝐦𝐦𝐲 taje bai buɗe ba sai ma cewa da yayi tayi hakuri zuwa anjima zai sauƙo.
Yana kwance akan gado yayi rub da ciki daga shi sai boxer, kuraren karfe biyu da mintuna talatin da uku wayansa ta buga ƙara,,, dama tun dazu kiran yake jira hakan yasa ba shiri ya ɗaga ya manna a kunne.
“ Sir done.” Wani kafurin murmushi ya sake yana kashe wayan ya tashi, sauri sauri ya shirya cikin shadda dark brown, ya taje gashin kansa wanda yake ta yalki ya ɗauki takalmi black ya saka, yana ɗaura agogo ya fashe jikinsa da turaruka masu kamshi, kafin ya buɗe ƙofan ɗakin ya fice da sauri babu wanda ya ganshi.
Bodyguard na hango shi suka tashi, hannu kawai ya ɗaga musu daya daga cikinsu ya miƙa masa key din mota, buɗe motan yayi ya shiga fuskansa ɗauke da murmushi, da haka aka buɗe masa get one ya fice, get two ma aka wangale masa ya fice a 360 yana murmushi yana shafa sajansa.
Sanye take cikin abaya brown wanda yasha adon stones, tayi rolling din kanta da mayafin abayar saboda babba ne ba ƙarami ba, dan har ya rufe bayanta.
Bayan ta fito daga shogon ne ta tsaya a bakin titi tana jiran machine, ga zafin rana ga wajen shuru babu mutane, da badan tana buk’atar taci biscuit ba, da yau baza ta fito ba.
Jin kamar an tsaya a bayanta ne, yasa ta juya dan ganin waye ne, watsa mata abu akayi a fuska ana sakata a mota, da sauri suka bar gurin.
*2 hours later*
A hankali ta soma buɗe idanunta waɗan da suka mata nauyi sosai, kafin daga bisani ta buɗe su duka tana bin gurin da kallo, ba shiri ta diro daga kan gadon da take tana bin ɗakin da kallon mamaki.
Jin ana k’ok’arin buɗe ƙofa ne yasa ta juyo da sauri tana jiran taga waye zai fito, a razane taja baya da sauri tana kare masa kallo mai cike da tuhuma….
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
7- *💅BA KAI NAKE SO BA💅*
_The story is all about love, romantic, sacrifice, heartbreak and destiny_
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*FATIMA ISA MANU💐*
*( DR TEEMAH)🦋🕊*
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
________________________________
Masu neman littafin *BA KAI NAKE SO BA* daga farko tare da sauran littafina zaku iya following channel ɗi na dan samu👇https://whatsapp.com/channel/0029Vaf6CpQDuMRYD1FMD92T
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IKUcfCN5rPQ9o0CaBtB2qP
___________________________________
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️*
____________________________________
*DIAMOND 💎 STAR ⭐*
*LADIES🧝♀️🧝♀️🧝♀️*
*(We stand together)*
🤝🤝🤝
___________________________________
*GARGADI*
Wannan littafin ƙagaggen labari ne, ban yarda wani ko wata ya sauya min shi ba ta kowace siga, sannan kuma ban amince a dauramin shi a youtube ba tare da izini na ba.
*BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫*
*P.7*