Sashe 11
Ba Kai Nake So Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“ To me na maka?.” Durkushewa ta yi a gurin tana haɗa hannayen ta biyu tare da cewa. “ Na haɗa ka da Allah ka mayar dani gida.”
Zuba mata ido kawai yayi ba tare da ya ce komai ba.
“ Dan kaunar da kake yiwa Mahaifiyarka ka mayar dani.”
“ Bazan iya ba.” Ya faɗa a takaice.
Da mamaki ta tashi tsaye tana kallon shi, a hankali ta tako izuwa wajen da yake tana facing nashi, ɗaga ido ta yi tana kallon cikin nashi take cewa. “ Dalili?.”
“ Idan na mayay da ke da wa zan rin ga rage zafi?.” Ya faɗa yana sunkuyo da fuskar shi dai-dai nata.
“ Me ka ɗauke ni wai?.”
“ Kayuwata.”
“ Ko kunya baka ji kana kirana da karuwarka? Hmm shikenan kar ka mayar dani amma ka tsorace ranar kin dillanci, dan Allah ba azzalumin bawansa bane, kuma yanda kakeso na koma bazan taba komawa ba.”
Dariya yayi yana kama hannunta tare da cewa. “ Zo kici abinci dan na samu nawa lunch din anjima, babyn baby.” Ya faɗa yana kashe mata ido daya.
Damtsen hannunsa ta kama tana gantsarawa cizo, da sauri ya sake ta, da gudu ta fice daga ɗakin….
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
11 - 12 *💅BA KAI NAKE SO BA💅*
_The story is all about love, romantic, sacrifice, heartbreak and destiny_
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*FATIMA ISA MANU💐*
*( DR TEEMAH)🦋🕊*
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
Masu neman littafin *BA KAI NAKE SO BA* daga farko tare da sauran littafina zaku iya following channel ɗi na dan samu👇https://whatsapp.com/channel/0029Vaf6CpQDuMRYD1FMD92T
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IKUcfCN5rPQ9o0CaBtB2qP
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️*
*DIAMOND 💎 STAR ⭐*
*LADIES🧝♀️🧝♀️🧝♀️*
*(We stand together)*
🤝🤝🤝🤝
*GARGADI*
Wannan littafin ƙagaggen labari ne, ban yarda wani ko wata ya sauya min shi ba ta kowace siga, sannan kuma ban amince a dauramin shi a youtube ba tare da izini na ba.
*BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫*
*P.11 & 12*
Damtsen hannunsa ta kama tana gantsarawa cizo, da sauri ya sake ta, da gudu ta fice daga ɗakin tana dingishi, abun ka da wacce bata san yanda tsarin gidan ya ke ba, tana fita daga ɗakin ta kalla matakalan da zai kai ka down stairs, juya bayanta ta yi ta ga bai fito ba da sauri take taka stairs bibbiyu har ta sauƙo parlon.
Ƙofan parlon ta nufa da gudu zata buɗe, a rufe taji hakan yasa ta shiga bubbugawa tana kuka tana faɗin. “ Dan Allah wani ya taimake ni.”
Muryansa taji a bayanta yana cewa. “ Babu wanda zai iya taimakon ki.”
A tsorace ta juyo tana kallon shi, takowa yayi izuwa inda take yana cewa. “ Duk inda zaki shiga a faɗin duniyay nan sai na nemo ki, so no need ki nemi hanyay guduwa dan ba samu zakiyi ba, gida kuma zan kai ki amma ba yanzu ba.”
Gaban rigar shi ta cikume tana magana cikin ɗaga murya. “ Wai dan Allah me na maka ne? Me sa kakeso ka deɗanta rayuwata ne.”
Cire hannunta yayi daga gaban rigarsa yana cewa. “ Kay ki soma sabawa da cikume mijinki ba, ba dabi’a me kyau bane.”
“ Nabi dabi’a da gudu dan uban shi, mugu azzalumi kawai Allah ya isa tsakanina da kai, haduwa na da kai bai min komai ba, nayi dana sanin zuwa company ka da neman aiki, da ana komawa baya da na koma na goge wannan babin da duk haka bazata faru ba, mazina…”
“ Ya isa!!!.” Ya daka mata tsawa, da sauri ta ja baya tana kallon yanda idanunsa suka yi ja, har jijiyoyin kansa sai da suka tashi.
Murya a dake cikin tsawa yake cewa. “ Kay ki kuma sake aibanta ni da mugayen kalamai iyin wannan, ni ba tsayanki bane sannan ke ƙanwata ce ta kusan uku, kay ki ga ina miki wasa ki ɗauka ni bani da hankali, ni dabba ne da zan ɗauko mace in yinga kwanciya da ita ba taye da ta zama muhayyama ta ba, ko dan ina kiyan ki da kayuwata sai ki ɗauka hakan ne? ki sake zama kiyi tunani Idiot kawai.” Ya ƙarashe maganar yana nufan upstairs da sauri.
Da ido ta bishi tana zamewa ta zauna a gurin, kamar mutum mutumi haka ta koma, take jikinta yayi wani mugun sanyi taji kunyar da ta rasa gane kanshi yana sauƙar mata.
Ta dade zaune a gurin tana tunanin da ba kai, kafin ta tashi sulum-sulum tana nufan upstairs din, ɗakin farko ta murɗa taji a rufe, ɗaki na biyu taje ta murda taji a buɗe.
Shiga ta yi kanta a sunkuye, yana zaune a kan gujera yana danna laptop amma kallo daya zaka masa ka gane hankalin shi baya kan laptop din kawai dannawa yake.
A bakin ƙofar ta tsaya ta yi shuru, ba tare da ya ganta ba ya ce. “ Ga abinci idan za ki ci.”
Kallon inda basket din yake ta yi, kafin ta dube shi ganin baya kallon ta ne yasa ta nufa gurin tana ɗaukar basket din ta ajiye a ƙasa, ita ma zama ta yi tana ciro food flakes din, spaghetti ne da miyan vegetables yasha nama ga kamshin dake tashi.
Taɓe baki ta yi tana rufewa kana ta miƙe tsaye, duk abunda take yi yana kallonta ta witsiyar ido hakan yasa ya ce. “ Ba za ki ci bane?.”
“ Bana cin alaiyaho.”
Sakin baki yayi yana kallon ta da mamaki, wai bata cin alaiyaho ikon Allah kafin ya ce. “ Miƙo min ni zanci ai.”
Ɗauka ta yi ta kai mishi tana juyawa ta koma kan gado, hawa tayi tana jan bargo ta rufe har kanta.
“ To me zaki ci?.” Ya tambaye ta.
Mantar da shi ta yi tana sake rufe kan ta me kyau, yasan taji amma sai ya kuma maimaitawa, nan ma mantar dashi ta yi, hakan yasa ya tashi ya ɗauki laptop nashi da basket din ya fice daga ɗakin, tana ji ya saka key.
Buɗe fuskarta ta yi tana kallon ƙofar, tashi ta yi ta nufa gurin window tana kallon tsuntsayen.
*Bayan kwana hudu*
Meemah ce ta shigo part din Mansoor da waya a hannunta tana cewa. “ Yaya Mama tana maka magana.” Ta miƙa masa yana zaune akan three seater.
Waya suka yi da Mama kafin suka yi sallama yana miƙa mata wayanta tare da cewa. “ Ku de idan baku bawa mutum wahala ba, bakwa jin dadi.”
“ Hhh ai haka zaka ɗaure Yaya.”
Hararan wasa ya mata yana cewa. “ Bari na shirya sai muje.”
Waro ido waje ta yi tana cewa. “ Yaya Mama fa bata ce kaje da ni ba.”
“ To sai karki bi umarni na tunda ni nace muje.”
“ Hhh na isa wa zai na siyamin ice cream to.”
“ Oho fa.” Ya faɗa yana shigewa dakinsa, tashi ita kuma tayi tana fita ta koma bangaren su, murmushi ta yi lokacin da ta tuna da Meerah a fili ta ce. “ Allah ya bayyanar dake Love, Allah yasa kina hannu na gari.”
Da Ameen Yasmeen ta amsa mata, murmushi ta mata tana cewa. “ Kin ji wai Yaya ne yace na rakasa unguwa.”
“ Chabb ki ce yau anaji da ke, nifa ranar nan da yayi kyau nace zan rakasa ko a matsayin mai riƙe masa jaka ne amma ya ce wai budurwarsa zata ji haushi, kuma fa bayi da budurwar amma haka inaji ina gani ya hanani zuwa.”
Dariya Meemah ta mata tana cewa. “ Bari na saka abaya akan wannan rigar kawai.” Ta fada tana ciro brown din abaya irin na Meerah sak ta saka.
Yasmeen ce ta ce. “ Sai kika tunamin da Meerah, da irin kayan nan aka ɗauke ta.”
Murmushi ta yi tana kallon abayar tana cewa. “ Har faɗa muka tabayi akan abayar nan, wai nata na saka nace mata nawa fa na saka, sai da ta duba cikin kayanta ta gani kafin ta yarda ba nata na saka ba, kinsan yanda take son abayan nan kuwa.”
“ Allah sarki, Allah ya kubutar da ita.”
“ Ameen.”
Muryan Mansoor suka ji daga waje yana cewa shi fa zai tafi, da sauri Meemah ta fito tana yiwa Yasmeen sallama.
“ Ce miki akayi wai shan ice cream zamu je yi ne?.” Murmushi kawai ta masa, da haka ta shiga ya bude get yana fita da motan.
Suna tafiya suna hira har suka iso wani super market, parking ya yi yana fitowa ita ma ta fito, kallon motan dake wajen yayi yana cewa. “ Mutumin yana nan kenan.”
Ita dai bata ce komai ba, da haka suka jera kwanin burgewa suka nufa cikin super market din.
Gurin kayan sawa na mata suka nufa, kallon ta yayi yana cewa. “ Ki dibi abun da zai miki.” Gyaɗa masa kai ta yi zata juya, karaf suka haɗa ido da shi.
Zuciyansa ne ya tsinke, da sauri ya iso gurin da take zai yi magana ta riga sa cewa. “ Sir ina wuni.”
Muryan ne yaji ba nata ba hakan yasa ya gane cewa yar biyun ta ne, murmushi ya ƙwaƙulo yana daurawa akan fuskan sa tare da cewa. “ Lafiya, ya aikin?.”
Jin tana magana da wani ne yasa Mansoor juyowa, murmushi yayi yana cewa. “ Ai naga motan ka Bobo, nasan kana ciki.”
“ Wato samin ido kake yi?.” Ya faɗa yana bashi hannu suka gaisa.
“ Na isa na sawa Mama’s Boy ido, ai sai a ɗaure ni.”
“ Tsaf ma kuwa.” Ya faɗa yana dariya, wanda yasa dimple nashi duka biyu lotsewa.
“ Me ya kawo ka nan.”
“ Uhm wata nazowa siyayya fa.”
Kallon bangane ba Mansoor ya masa, gira ya ɗaga masa yana cewa. “ Abun da kaji shi na ce.”
Dariya yayi yana cewa. “ Ai ina son ƙarin bayani ne.”
“ Babu abunda zaka ji kuwa.”
Meemah ce tayi murmushi tana cewa. “ Yaya bari naje na fara.”
Gyaɗa mata kai yayi yana kama hannun Alyan.
“ Please duk abunda kika ɗauka ya zama bibbiyu kuma iyi daya.”
Mansoor ne ya ce. “ Komai fa Bobo, komai fa.”
Zuba mata ido kawai yayi ba tare da ya ce komai ba.
“ Dan kaunar da kake yiwa Mahaifiyarka ka mayar dani.”
“ Bazan iya ba.” Ya faɗa a takaice.
Da mamaki ta tashi tsaye tana kallon shi, a hankali ta tako izuwa wajen da yake tana facing nashi, ɗaga ido ta yi tana kallon cikin nashi take cewa. “ Dalili?.”
“ Idan na mayay da ke da wa zan rin ga rage zafi?.” Ya faɗa yana sunkuyo da fuskar shi dai-dai nata.
“ Me ka ɗauke ni wai?.”
“ Kayuwata.”
“ Ko kunya baka ji kana kirana da karuwarka? Hmm shikenan kar ka mayar dani amma ka tsorace ranar kin dillanci, dan Allah ba azzalumin bawansa bane, kuma yanda kakeso na koma bazan taba komawa ba.”
Dariya yayi yana kama hannunta tare da cewa. “ Zo kici abinci dan na samu nawa lunch din anjima, babyn baby.” Ya faɗa yana kashe mata ido daya.
Damtsen hannunsa ta kama tana gantsarawa cizo, da sauri ya sake ta, da gudu ta fice daga ɗakin….
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
11 - 12 *💅BA KAI NAKE SO BA💅*
_The story is all about love, romantic, sacrifice, heartbreak and destiny_
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*FATIMA ISA MANU💐*
*( DR TEEMAH)🦋🕊*
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
Masu neman littafin *BA KAI NAKE SO BA* daga farko tare da sauran littafina zaku iya following channel ɗi na dan samu👇https://whatsapp.com/channel/0029Vaf6CpQDuMRYD1FMD92T
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IKUcfCN5rPQ9o0CaBtB2qP
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️*
*DIAMOND 💎 STAR ⭐*
*LADIES🧝♀️🧝♀️🧝♀️*
*(We stand together)*
🤝🤝🤝🤝
*GARGADI*
Wannan littafin ƙagaggen labari ne, ban yarda wani ko wata ya sauya min shi ba ta kowace siga, sannan kuma ban amince a dauramin shi a youtube ba tare da izini na ba.
*BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫*
*P.11 & 12*
Damtsen hannunsa ta kama tana gantsarawa cizo, da sauri ya sake ta, da gudu ta fice daga ɗakin tana dingishi, abun ka da wacce bata san yanda tsarin gidan ya ke ba, tana fita daga ɗakin ta kalla matakalan da zai kai ka down stairs, juya bayanta ta yi ta ga bai fito ba da sauri take taka stairs bibbiyu har ta sauƙo parlon.
Ƙofan parlon ta nufa da gudu zata buɗe, a rufe taji hakan yasa ta shiga bubbugawa tana kuka tana faɗin. “ Dan Allah wani ya taimake ni.”
Muryansa taji a bayanta yana cewa. “ Babu wanda zai iya taimakon ki.”
A tsorace ta juyo tana kallon shi, takowa yayi izuwa inda take yana cewa. “ Duk inda zaki shiga a faɗin duniyay nan sai na nemo ki, so no need ki nemi hanyay guduwa dan ba samu zakiyi ba, gida kuma zan kai ki amma ba yanzu ba.”
Gaban rigar shi ta cikume tana magana cikin ɗaga murya. “ Wai dan Allah me na maka ne? Me sa kakeso ka deɗanta rayuwata ne.”
Cire hannunta yayi daga gaban rigarsa yana cewa. “ Kay ki soma sabawa da cikume mijinki ba, ba dabi’a me kyau bane.”
“ Nabi dabi’a da gudu dan uban shi, mugu azzalumi kawai Allah ya isa tsakanina da kai, haduwa na da kai bai min komai ba, nayi dana sanin zuwa company ka da neman aiki, da ana komawa baya da na koma na goge wannan babin da duk haka bazata faru ba, mazina…”
“ Ya isa!!!.” Ya daka mata tsawa, da sauri ta ja baya tana kallon yanda idanunsa suka yi ja, har jijiyoyin kansa sai da suka tashi.
Murya a dake cikin tsawa yake cewa. “ Kay ki kuma sake aibanta ni da mugayen kalamai iyin wannan, ni ba tsayanki bane sannan ke ƙanwata ce ta kusan uku, kay ki ga ina miki wasa ki ɗauka ni bani da hankali, ni dabba ne da zan ɗauko mace in yinga kwanciya da ita ba taye da ta zama muhayyama ta ba, ko dan ina kiyan ki da kayuwata sai ki ɗauka hakan ne? ki sake zama kiyi tunani Idiot kawai.” Ya ƙarashe maganar yana nufan upstairs da sauri.
Da ido ta bishi tana zamewa ta zauna a gurin, kamar mutum mutumi haka ta koma, take jikinta yayi wani mugun sanyi taji kunyar da ta rasa gane kanshi yana sauƙar mata.
Ta dade zaune a gurin tana tunanin da ba kai, kafin ta tashi sulum-sulum tana nufan upstairs din, ɗakin farko ta murɗa taji a rufe, ɗaki na biyu taje ta murda taji a buɗe.
Shiga ta yi kanta a sunkuye, yana zaune a kan gujera yana danna laptop amma kallo daya zaka masa ka gane hankalin shi baya kan laptop din kawai dannawa yake.
A bakin ƙofar ta tsaya ta yi shuru, ba tare da ya ganta ba ya ce. “ Ga abinci idan za ki ci.”
Kallon inda basket din yake ta yi, kafin ta dube shi ganin baya kallon ta ne yasa ta nufa gurin tana ɗaukar basket din ta ajiye a ƙasa, ita ma zama ta yi tana ciro food flakes din, spaghetti ne da miyan vegetables yasha nama ga kamshin dake tashi.
Taɓe baki ta yi tana rufewa kana ta miƙe tsaye, duk abunda take yi yana kallonta ta witsiyar ido hakan yasa ya ce. “ Ba za ki ci bane?.”
“ Bana cin alaiyaho.”
Sakin baki yayi yana kallon ta da mamaki, wai bata cin alaiyaho ikon Allah kafin ya ce. “ Miƙo min ni zanci ai.”
Ɗauka ta yi ta kai mishi tana juyawa ta koma kan gado, hawa tayi tana jan bargo ta rufe har kanta.
“ To me zaki ci?.” Ya tambaye ta.
Mantar da shi ta yi tana sake rufe kan ta me kyau, yasan taji amma sai ya kuma maimaitawa, nan ma mantar dashi ta yi, hakan yasa ya tashi ya ɗauki laptop nashi da basket din ya fice daga ɗakin, tana ji ya saka key.
Buɗe fuskarta ta yi tana kallon ƙofar, tashi ta yi ta nufa gurin window tana kallon tsuntsayen.
*Bayan kwana hudu*
Meemah ce ta shigo part din Mansoor da waya a hannunta tana cewa. “ Yaya Mama tana maka magana.” Ta miƙa masa yana zaune akan three seater.
Waya suka yi da Mama kafin suka yi sallama yana miƙa mata wayanta tare da cewa. “ Ku de idan baku bawa mutum wahala ba, bakwa jin dadi.”
“ Hhh ai haka zaka ɗaure Yaya.”
Hararan wasa ya mata yana cewa. “ Bari na shirya sai muje.”
Waro ido waje ta yi tana cewa. “ Yaya Mama fa bata ce kaje da ni ba.”
“ To sai karki bi umarni na tunda ni nace muje.”
“ Hhh na isa wa zai na siyamin ice cream to.”
“ Oho fa.” Ya faɗa yana shigewa dakinsa, tashi ita kuma tayi tana fita ta koma bangaren su, murmushi ta yi lokacin da ta tuna da Meerah a fili ta ce. “ Allah ya bayyanar dake Love, Allah yasa kina hannu na gari.”
Da Ameen Yasmeen ta amsa mata, murmushi ta mata tana cewa. “ Kin ji wai Yaya ne yace na rakasa unguwa.”
“ Chabb ki ce yau anaji da ke, nifa ranar nan da yayi kyau nace zan rakasa ko a matsayin mai riƙe masa jaka ne amma ya ce wai budurwarsa zata ji haushi, kuma fa bayi da budurwar amma haka inaji ina gani ya hanani zuwa.”
Dariya Meemah ta mata tana cewa. “ Bari na saka abaya akan wannan rigar kawai.” Ta fada tana ciro brown din abaya irin na Meerah sak ta saka.
Yasmeen ce ta ce. “ Sai kika tunamin da Meerah, da irin kayan nan aka ɗauke ta.”
Murmushi ta yi tana kallon abayar tana cewa. “ Har faɗa muka tabayi akan abayar nan, wai nata na saka nace mata nawa fa na saka, sai da ta duba cikin kayanta ta gani kafin ta yarda ba nata na saka ba, kinsan yanda take son abayan nan kuwa.”
“ Allah sarki, Allah ya kubutar da ita.”
“ Ameen.”
Muryan Mansoor suka ji daga waje yana cewa shi fa zai tafi, da sauri Meemah ta fito tana yiwa Yasmeen sallama.
“ Ce miki akayi wai shan ice cream zamu je yi ne?.” Murmushi kawai ta masa, da haka ta shiga ya bude get yana fita da motan.
Suna tafiya suna hira har suka iso wani super market, parking ya yi yana fitowa ita ma ta fito, kallon motan dake wajen yayi yana cewa. “ Mutumin yana nan kenan.”
Ita dai bata ce komai ba, da haka suka jera kwanin burgewa suka nufa cikin super market din.
Gurin kayan sawa na mata suka nufa, kallon ta yayi yana cewa. “ Ki dibi abun da zai miki.” Gyaɗa masa kai ta yi zata juya, karaf suka haɗa ido da shi.
Zuciyansa ne ya tsinke, da sauri ya iso gurin da take zai yi magana ta riga sa cewa. “ Sir ina wuni.”
Muryan ne yaji ba nata ba hakan yasa ya gane cewa yar biyun ta ne, murmushi ya ƙwaƙulo yana daurawa akan fuskan sa tare da cewa. “ Lafiya, ya aikin?.”
Jin tana magana da wani ne yasa Mansoor juyowa, murmushi yayi yana cewa. “ Ai naga motan ka Bobo, nasan kana ciki.”
“ Wato samin ido kake yi?.” Ya faɗa yana bashi hannu suka gaisa.
“ Na isa na sawa Mama’s Boy ido, ai sai a ɗaure ni.”
“ Tsaf ma kuwa.” Ya faɗa yana dariya, wanda yasa dimple nashi duka biyu lotsewa.
“ Me ya kawo ka nan.”
“ Uhm wata nazowa siyayya fa.”
Kallon bangane ba Mansoor ya masa, gira ya ɗaga masa yana cewa. “ Abun da kaji shi na ce.”
Dariya yayi yana cewa. “ Ai ina son ƙarin bayani ne.”
“ Babu abunda zaka ji kuwa.”
Meemah ce tayi murmushi tana cewa. “ Yaya bari naje na fara.”
Gyaɗa mata kai yayi yana kama hannun Alyan.
“ Please duk abunda kika ɗauka ya zama bibbiyu kuma iyi daya.”
Mansoor ne ya ce. “ Komai fa Bobo, komai fa.”