Sashe 10
Ba Kai Nake So Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi kawai ta yi cikin ranta kuwa kamar wuta ake hurara mata tsabar zafi, da kyar ta samu ta tsabtace jikinta kafin ta yi wanka ta ɗauro alwala saboda kiran sallan da ake a masallacin unguwan, fitowa ta yi tana tafiya tana ware ƙafa.
Ƙarewa ɗakin kallo me kyau ta yi, babban ɗaki ne wanda yasha kayan more rayuwa irin na ɗaki a ciki, royal bed ne da wardrobe ɗinsa purple, sai labulaye fari, ga gujera guda biyu a gefe mai launin purple.
Taɓe baki ta yi tana nufan wardrobe din da ta gani, hannu tasa tana buɗewa, kayan sawan shi ne a ciki, su jallabiya gefe daban sleeping dress ma gefe guda ga boxers da su shadda jamfa kenan.
Wani pink sleeping dress din shi ta gani, jawowa ta yi riga da wandon tana warwarewa, wandon gajere ne rigar kuma mara hannu ne wato mai siririn hannu.
Kunce towel din ta yi ya faɗi ƙasa tana saka wandon, amma kunkumin ya mata yawa sosai, turo baki gaba ta yi tana sake duba wani, jallabiya fari ta gani a naɗe, zaro shi ta yi tana warwarewa sai dai ya mata yawo sosai.
“ Ai Wallahi haka zan saka.” Ta faɗa tana zura jallabiyar, duk da ya mata yawa amma ya amshi jikinta sosai sai ta zama kamar wani tsinke a cikin buhu, gurin madubi ta nufa tana ɗaga ƙafa a hankali, tsayawa ta yi tana ƙarewa kanta kallo, dariya ta yi tana cewa. “ Wa yaga Boss kenan.” Ta kuma ƙwashewa da dariya, tunawa da ta yi yanzu ita ba budurwa bace kuma ba matar aure bace sannan ba bazawara ba.
Nan da nan hawaye suka cika idanunta, saurin sharewa ta yi tana ɗaukar sallayar dake kan bedside ta shimfiɗa, hijabin daya barga ta ɗauka ta rufe jikinta da shi tana mai tada kambara.
Ko da ya fita daga ɗakin direct ɗakin dake facing din wannan ya shiga, sai da yayi wanka kafin ya ɗauro alwala lokacin har an idar da sallah, hakan ya sa yayi nashi a gida.
Yana idarwa ya ɗauki key din mota ya fita daga ɗakin, down stairs ya sauƙo yana buɗe parlon ya fice bayan ya saka key.
Parking lot ya nufa amintaccen bodyguard nasa ne ya taso mai suna Alex yana nufo shi da sauri, buɗe masa baya yayi ya shiga shi kuma ya shiga wajen driver yana tada motan, da sauri aka wangale musu get suka fice.
“ Sir…” Tun kafin ya ƙarasar Alyan ya ce masa. “ Ammy.”
“ Owk.” A cewar Alex yana nufan unguwar.
*MILLIONAIRE CITY.*
A bakin get one suka tsaya akayi scanning, duk da kuwa ansan shi din ne amma dole ne ayi, get two suka nufa shi kuma security’s ne sosai a wajen, motan yana tsaye get din ya buɗe suka nufa ciki.
A bakin parlon Alex ya tsaya yana fitowa ya buɗe masa, idanunsa a lumshe fuskansa ɗauke da murmushi ya zuro fararen ƙafarsa, kafin ya buɗe ido ya fito baki daya, cike da isa ya fara takun sa ya nufa ƙofar parlon yana shiga.
Babu kowa a parlon hakan yasa ya haura sama yana nufan ɗakin Laylerh, a bakin ɗakin ya tsaya kafin ya buɗe ƙofan yana shiga.
Tana ƙwance ta rufu da bargo, da alama tana idar da sallah ta sake kwanciya, tamke fuska yayi ya nufa gurin gadon, bargon ya yaye yana zuba mata duka a bayanta.
A razane ta tashi tana sakin kuka, saurin haɗiye kukan ta yi tana kallon shi.
“ Je ki dafamin abinci.” Ya faɗa a tsare yana kallon ta.
“ Amma Yaya dan Allah shi ne zaka dake ni babu abunda na maka fa.”
“ Zo ki yama to.”
Turo baki gaba ta yi tana sauƙa akan gado, tana cewa. “ Yaya naga kayi kyau yau kayi wani fresh haka.”
“ Samin ido kika faya?.” Ya faɗa a fili, cikin ransa kuwa cewa ya yi ‘ Ba dole ba tunda na samu na yage zafi ‘ Katsai masa zancen zucin ta yi ta hanyar cewa. “ Me zan dafa maka da safen nan.”
“ Abun da maya lafiya zai iya ci.” Da sauri ta ce. “ Bro waye ba lafiya.” Da sauri ya gyara zancen. “ Ina nufin maya nauyi kaman wanda zan iya ci.”
“ Kai kuma, ai kai ko tuwon dawa ne zaka iya ci, ko dai Yaya ma wata zaka kaiwa.”
Ji kake Dumm zuciyarsa ya tsinke, amma dake namijin duniya ne sai ya nufo ta yana cewa. “ Bayi na isoki to.” Da sauri ta fice tana dariya.
Ɗakin Ammy ya nufo wacce take kusa da na Laylerh, ƙwanƙwasawa ya yi ta ciki Ammy na cewa. “ Bismillah a shigo.”
Da sallama a bakinsa ya shigo, tana zaune a bakin gado hannunta riƙe da charbi daga ganin alama tasbaha take, murmushi yayi yana ƙarasowa ya ɗurƙusa har ƙasa yana cewa. “ Ammyna good morning.”
“ Morning Babana, an tashi lafiya?.”
“ Lafiya Ammyna.”
Shuru ne ya biyo baya kafin Ammy ta dube shi me kyau tana cewa. “ A ina ka kwana jiya?.”
Kamar sauƙar aradu haka maganar Ammy ya sauƙar masa, cikin dakewa da nuna kamar ba shi ba ya ɗago yana cewa. “ Ammy a studio na kwana.”
“ Baka saba min karya ba kuma banaso ka soma, saboda haka a ina ka kwana jiya?.”
Shuru yayi yana tunanin me zai ce, kafin ya ce. “ Ammy a gidana na Unguwan Yimi na kwana.”
“ Kai da su wa?.” Da sauri ya dago yana kallon ta kafin ya ce. “ Ammy kina zaygina ne?.”
“ Dama kai kana zargin kan ka ne?.”
“ Ah ah.”
“ Na duba location naka ne jiya ya nunamin ba’a studio ka kwana ba, A unguwan Rimi ka kwana, then me ya sa kamin karya?.”
“ Ammy kiyi hakuyi.”
“ Babana yaushe ka fara min karya to?.”
“ Kiyi hakuyi Ammy.”
Shuru ta yi tana karantarsa me kyau, taga sauyi sosai a tattare dashi ga wani kiban da ya danyi amma sai bata ce komai ba.
Ganin babu abunda yake son cewa ne yasa ta ce. “ Muje muyi breakfast.” Ta faɗa tana tashi ta nufa hanyar fita, biyo bayanta yayi sumu-sumu kamar munafuki.
Daining table suka isa ya ja mata gujera tana zama shima ya zauna, da sauri masu aikin suka iso suna fara saving nasu.
“ Kira min Laylerh a ɗakin ta.” Ammy ta fada tana kallon ɗaya me aikin me sunan Laure.
“ To Hajiya.”
“ Ke dawo.” Alyan ya faɗa a kausashe, kana ya dubi Ammy yana cewa. “ Ammyna tana kitchen na sata giyki.”
“ Girki ma wa?.”
Dan sosa keya yayi yana cewa. “ Ma wata Mayainiya ce.”
Cigaba da cin abincin suka yi suna dan taba hira, cikin hiran ne Ammy take cewa. “ To Babana ka kawo Marainiyar nan mana kasan banaso suna shan wahala.”
Wani ƙwarewa yayi, da sauri Ammy ta miƙa masa ruwa tana masa sannu, lokacin ne kuma Laylerh ta fito da basket a hannunta da alama ta kammala girkin har ta jera a basket din.
Da sauri ya tashi yana cewa. “ Ammy na tafi sai na dawo.” Ya karbi basket din hannun Laylerh yana cewa. “ Thanks Lovely sai na dawo zan chanza miki waya.”
Ihu ta saka tana cewa. “ Allah ƙara arziki Babban yaya ya baka mace me hankali mai irin halinka.”
Bai ce komai ba ya fita, Ammy na rakasa da kallo mai cike da tambayoyi.
*UNGUWAR DOSA*
“ Meemah ki sakata cikin addu’a In Sha Allah zata dawo, amma wannan kukan naki ba shine mafita ba.” A cewar Mansoor yana mata magana cikin sigar lallashi.
Mama ce ta ce. “ Ta ƙi cin abinci ma tun shekaran jiyan, watakila idan ka mata magana zata ci.”
“ Me ya hanaki cin abinci?.”
“ Bana jin yunwa ne.” Muryanta na rawa ta faɗa.
“ Tun last three days bakya jin yunwa? Sannu robot.” Dariya ta fashe da shi Yasmeen na cewa. “ Robot kuma Yaya.”
“ Ah to Robot mana, wani mutum ne zai ƙi cin abinci har na kwana uku kuma still yana da lafiya.”
“ Mansoor ina ga ɗure zamu mata kawai.” Mama ta faɗa.
Dariya Meemah ke musu kawai, ta gefe guda kuma kewar ƴar biyunta take tana mata addu’a a duk inda take Allah yasa tana cikin ƙoshin lafiya.
A gurin da ta yi sallah a nan bacci ya ɗauke ta, sai guraren ƙarfe tara ta farka yunwa duk ya ishe ta, da kyar ta miƙe tana isa gurin window, kallon harabar gidan take da yanda security’s suke kai kawo, ga masu gyaran fulawa sai aiki suke.
Idonta ne ya sauƙa akan wasu tsuntsaye biyu suna caccakar abinci, murmushi ne ya subuce daga kan fuskarta ganin yanda tsuntsun yake bawa daya abinci a baki da halama uwa ne da ƴa.
Tana tsaye a bakin window ya shigo da basket a hannun shi, kafe ta da ido yayi yana ƙarewa surar jikinta kallo, ba laifi tana daya daga cikin matan da yake so, saboda tana da tsayi dai-dai misali ga ta slim kuma fara ga gashi, kuma akwai body ba laifi na dai-dai yanda yake so, amma mai sa yake mata abubbuwan da yake yi? Me ta masa har haka? Ta cancanci a mata haka?.
Ya daɗe a tsaye a gurin yana tambayar kan shi, kafin yayi gyaran murya wanda yasa ta juyo tana kallon shi.
Kallon kayan jikinta yayi yana tsayar da idanunsa akan bobs dinta wanda kana iya kallon yanda nipples nata yake kamar zai fito.
Kallon inda idanunsa suke kallo ta yi tana saka hannu ta rufe, mayar da kallon shi yayi izuwa fuskarta yana cewa. “ Wa ya baki damay saka min kaya?.”
“ Saboda bani da wanda zan saka.” Tayi maganar tana tura baki gaba.
“ Ban ce kina yawo haka ba? Ai kayuwai basa saka kaya.”
Da sauri ta dube shi, cike da tsana take cewa. “ Wai me na maka ne da kakeson sakamin ciwon zuciya? Akwai abunkan da na taɓa bata maka ne? Ko na taɓa zagin maka dangi ne ko Uwa da kake jifana da sunan karuwa?.”
“ Ko daya.”
Ƙarewa ɗakin kallo me kyau ta yi, babban ɗaki ne wanda yasha kayan more rayuwa irin na ɗaki a ciki, royal bed ne da wardrobe ɗinsa purple, sai labulaye fari, ga gujera guda biyu a gefe mai launin purple.
Taɓe baki ta yi tana nufan wardrobe din da ta gani, hannu tasa tana buɗewa, kayan sawan shi ne a ciki, su jallabiya gefe daban sleeping dress ma gefe guda ga boxers da su shadda jamfa kenan.
Wani pink sleeping dress din shi ta gani, jawowa ta yi riga da wandon tana warwarewa, wandon gajere ne rigar kuma mara hannu ne wato mai siririn hannu.
Kunce towel din ta yi ya faɗi ƙasa tana saka wandon, amma kunkumin ya mata yawa sosai, turo baki gaba ta yi tana sake duba wani, jallabiya fari ta gani a naɗe, zaro shi ta yi tana warwarewa sai dai ya mata yawo sosai.
“ Ai Wallahi haka zan saka.” Ta faɗa tana zura jallabiyar, duk da ya mata yawa amma ya amshi jikinta sosai sai ta zama kamar wani tsinke a cikin buhu, gurin madubi ta nufa tana ɗaga ƙafa a hankali, tsayawa ta yi tana ƙarewa kanta kallo, dariya ta yi tana cewa. “ Wa yaga Boss kenan.” Ta kuma ƙwashewa da dariya, tunawa da ta yi yanzu ita ba budurwa bace kuma ba matar aure bace sannan ba bazawara ba.
Nan da nan hawaye suka cika idanunta, saurin sharewa ta yi tana ɗaukar sallayar dake kan bedside ta shimfiɗa, hijabin daya barga ta ɗauka ta rufe jikinta da shi tana mai tada kambara.
Ko da ya fita daga ɗakin direct ɗakin dake facing din wannan ya shiga, sai da yayi wanka kafin ya ɗauro alwala lokacin har an idar da sallah, hakan ya sa yayi nashi a gida.
Yana idarwa ya ɗauki key din mota ya fita daga ɗakin, down stairs ya sauƙo yana buɗe parlon ya fice bayan ya saka key.
Parking lot ya nufa amintaccen bodyguard nasa ne ya taso mai suna Alex yana nufo shi da sauri, buɗe masa baya yayi ya shiga shi kuma ya shiga wajen driver yana tada motan, da sauri aka wangale musu get suka fice.
“ Sir…” Tun kafin ya ƙarasar Alyan ya ce masa. “ Ammy.”
“ Owk.” A cewar Alex yana nufan unguwar.
*MILLIONAIRE CITY.*
A bakin get one suka tsaya akayi scanning, duk da kuwa ansan shi din ne amma dole ne ayi, get two suka nufa shi kuma security’s ne sosai a wajen, motan yana tsaye get din ya buɗe suka nufa ciki.
A bakin parlon Alex ya tsaya yana fitowa ya buɗe masa, idanunsa a lumshe fuskansa ɗauke da murmushi ya zuro fararen ƙafarsa, kafin ya buɗe ido ya fito baki daya, cike da isa ya fara takun sa ya nufa ƙofar parlon yana shiga.
Babu kowa a parlon hakan yasa ya haura sama yana nufan ɗakin Laylerh, a bakin ɗakin ya tsaya kafin ya buɗe ƙofan yana shiga.
Tana ƙwance ta rufu da bargo, da alama tana idar da sallah ta sake kwanciya, tamke fuska yayi ya nufa gurin gadon, bargon ya yaye yana zuba mata duka a bayanta.
A razane ta tashi tana sakin kuka, saurin haɗiye kukan ta yi tana kallon shi.
“ Je ki dafamin abinci.” Ya faɗa a tsare yana kallon ta.
“ Amma Yaya dan Allah shi ne zaka dake ni babu abunda na maka fa.”
“ Zo ki yama to.”
Turo baki gaba ta yi tana sauƙa akan gado, tana cewa. “ Yaya naga kayi kyau yau kayi wani fresh haka.”
“ Samin ido kika faya?.” Ya faɗa a fili, cikin ransa kuwa cewa ya yi ‘ Ba dole ba tunda na samu na yage zafi ‘ Katsai masa zancen zucin ta yi ta hanyar cewa. “ Me zan dafa maka da safen nan.”
“ Abun da maya lafiya zai iya ci.” Da sauri ta ce. “ Bro waye ba lafiya.” Da sauri ya gyara zancen. “ Ina nufin maya nauyi kaman wanda zan iya ci.”
“ Kai kuma, ai kai ko tuwon dawa ne zaka iya ci, ko dai Yaya ma wata zaka kaiwa.”
Ji kake Dumm zuciyarsa ya tsinke, amma dake namijin duniya ne sai ya nufo ta yana cewa. “ Bayi na isoki to.” Da sauri ta fice tana dariya.
Ɗakin Ammy ya nufo wacce take kusa da na Laylerh, ƙwanƙwasawa ya yi ta ciki Ammy na cewa. “ Bismillah a shigo.”
Da sallama a bakinsa ya shigo, tana zaune a bakin gado hannunta riƙe da charbi daga ganin alama tasbaha take, murmushi yayi yana ƙarasowa ya ɗurƙusa har ƙasa yana cewa. “ Ammyna good morning.”
“ Morning Babana, an tashi lafiya?.”
“ Lafiya Ammyna.”
Shuru ne ya biyo baya kafin Ammy ta dube shi me kyau tana cewa. “ A ina ka kwana jiya?.”
Kamar sauƙar aradu haka maganar Ammy ya sauƙar masa, cikin dakewa da nuna kamar ba shi ba ya ɗago yana cewa. “ Ammy a studio na kwana.”
“ Baka saba min karya ba kuma banaso ka soma, saboda haka a ina ka kwana jiya?.”
Shuru yayi yana tunanin me zai ce, kafin ya ce. “ Ammy a gidana na Unguwan Yimi na kwana.”
“ Kai da su wa?.” Da sauri ya dago yana kallon ta kafin ya ce. “ Ammy kina zaygina ne?.”
“ Dama kai kana zargin kan ka ne?.”
“ Ah ah.”
“ Na duba location naka ne jiya ya nunamin ba’a studio ka kwana ba, A unguwan Rimi ka kwana, then me ya sa kamin karya?.”
“ Ammy kiyi hakuyi.”
“ Babana yaushe ka fara min karya to?.”
“ Kiyi hakuyi Ammy.”
Shuru ta yi tana karantarsa me kyau, taga sauyi sosai a tattare dashi ga wani kiban da ya danyi amma sai bata ce komai ba.
Ganin babu abunda yake son cewa ne yasa ta ce. “ Muje muyi breakfast.” Ta faɗa tana tashi ta nufa hanyar fita, biyo bayanta yayi sumu-sumu kamar munafuki.
Daining table suka isa ya ja mata gujera tana zama shima ya zauna, da sauri masu aikin suka iso suna fara saving nasu.
“ Kira min Laylerh a ɗakin ta.” Ammy ta fada tana kallon ɗaya me aikin me sunan Laure.
“ To Hajiya.”
“ Ke dawo.” Alyan ya faɗa a kausashe, kana ya dubi Ammy yana cewa. “ Ammyna tana kitchen na sata giyki.”
“ Girki ma wa?.”
Dan sosa keya yayi yana cewa. “ Ma wata Mayainiya ce.”
Cigaba da cin abincin suka yi suna dan taba hira, cikin hiran ne Ammy take cewa. “ To Babana ka kawo Marainiyar nan mana kasan banaso suna shan wahala.”
Wani ƙwarewa yayi, da sauri Ammy ta miƙa masa ruwa tana masa sannu, lokacin ne kuma Laylerh ta fito da basket a hannunta da alama ta kammala girkin har ta jera a basket din.
Da sauri ya tashi yana cewa. “ Ammy na tafi sai na dawo.” Ya karbi basket din hannun Laylerh yana cewa. “ Thanks Lovely sai na dawo zan chanza miki waya.”
Ihu ta saka tana cewa. “ Allah ƙara arziki Babban yaya ya baka mace me hankali mai irin halinka.”
Bai ce komai ba ya fita, Ammy na rakasa da kallo mai cike da tambayoyi.
*UNGUWAR DOSA*
“ Meemah ki sakata cikin addu’a In Sha Allah zata dawo, amma wannan kukan naki ba shine mafita ba.” A cewar Mansoor yana mata magana cikin sigar lallashi.
Mama ce ta ce. “ Ta ƙi cin abinci ma tun shekaran jiyan, watakila idan ka mata magana zata ci.”
“ Me ya hanaki cin abinci?.”
“ Bana jin yunwa ne.” Muryanta na rawa ta faɗa.
“ Tun last three days bakya jin yunwa? Sannu robot.” Dariya ta fashe da shi Yasmeen na cewa. “ Robot kuma Yaya.”
“ Ah to Robot mana, wani mutum ne zai ƙi cin abinci har na kwana uku kuma still yana da lafiya.”
“ Mansoor ina ga ɗure zamu mata kawai.” Mama ta faɗa.
Dariya Meemah ke musu kawai, ta gefe guda kuma kewar ƴar biyunta take tana mata addu’a a duk inda take Allah yasa tana cikin ƙoshin lafiya.
A gurin da ta yi sallah a nan bacci ya ɗauke ta, sai guraren ƙarfe tara ta farka yunwa duk ya ishe ta, da kyar ta miƙe tana isa gurin window, kallon harabar gidan take da yanda security’s suke kai kawo, ga masu gyaran fulawa sai aiki suke.
Idonta ne ya sauƙa akan wasu tsuntsaye biyu suna caccakar abinci, murmushi ne ya subuce daga kan fuskarta ganin yanda tsuntsun yake bawa daya abinci a baki da halama uwa ne da ƴa.
Tana tsaye a bakin window ya shigo da basket a hannun shi, kafe ta da ido yayi yana ƙarewa surar jikinta kallo, ba laifi tana daya daga cikin matan da yake so, saboda tana da tsayi dai-dai misali ga ta slim kuma fara ga gashi, kuma akwai body ba laifi na dai-dai yanda yake so, amma mai sa yake mata abubbuwan da yake yi? Me ta masa har haka? Ta cancanci a mata haka?.
Ya daɗe a tsaye a gurin yana tambayar kan shi, kafin yayi gyaran murya wanda yasa ta juyo tana kallon shi.
Kallon kayan jikinta yayi yana tsayar da idanunsa akan bobs dinta wanda kana iya kallon yanda nipples nata yake kamar zai fito.
Kallon inda idanunsa suke kallo ta yi tana saka hannu ta rufe, mayar da kallon shi yayi izuwa fuskarta yana cewa. “ Wa ya baki damay saka min kaya?.”
“ Saboda bani da wanda zan saka.” Tayi maganar tana tura baki gaba.
“ Ban ce kina yawo haka ba? Ai kayuwai basa saka kaya.”
Da sauri ta dube shi, cike da tsana take cewa. “ Wai me na maka ne da kakeson sakamin ciwon zuciya? Akwai abunkan da na taɓa bata maka ne? Ko na taɓa zagin maka dangi ne ko Uwa da kake jifana da sunan karuwa?.”
“ Ko daya.”