Sashe 17
Ba Kai Nake So Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sosai hankalin Meerah ya koma ga Makaranta, dan hutun da aka basu an dawo, taje ta cire kudin tayi registration ita da Meemah ta hada har da Yasmeen, da Mansoor yazo yi musu registration yaga sun biya, yayi mamaki sosai dan kusan duba dari hudu ne, amma wai sun biya kuma bai tambaye su ba dan ba gaskiya zasu fada ba sai dai ya bisu da addu’a.
Tun ranar da sukayi waya dashi ta cire sim din ta ajiye ta cigaba da harkan ta, sosai tayi kyau tayi haske abun har mamaki yake bawa su Meemah da Yasmeen, dan shi Mansoor sai dai ya bita da ido kawai yana ganin yanda take kara kyau, duk da kuwa kullum cikin hijabi take.
Yau ya kama Wednesday kuma suna da lecture daga karfe goma zuwa sha biyu, sauri sauri suka gama aikinsu suka fice daga gidan dukan su uku.
Meemah da Yasmeen gyale suka saka ita kuma ta saka hijab blue wanda ya haska farin fatarta da ya kara haske sosai, hira suke suna tafiya ita dai Meerah sai dai tayi murmushi idan na yi ne, idan kuma na shuru ne tayi, da haka suka isa bakin titi, mai adaidaita sahu suka tara suka fada masa inda zai kai su, da haka suka shiga yaja suka nufi bus stop.
Suna isa bus stop Meerah ta bashi kudinsa, Napep suka shiga su uku ya jasu suka tafi.
Kowa hanyar department nashi ya nufa, ita Meemah ta nufa Physiology department, Yasmeen kuma Computer science , Meerah kuma Law.
Sauri take dan baifi saura minti biyar a shiga ba, buguwa tayi da wata budurwa har ta watsar mata da takaddu.
“ Yi hakuri dan Allah sauri nake ban ganki ba.” Ta fada tana durkusawa ta fara tattare mata takardun ta mika mata.
Karba tayi tana mata murmushi tare da cewa. “ Bakomai Nagode.”
Murmushi Meerah ta mata tana k’ok’arin wucewa.
Budurwar ce ta dafa ta tana cewa. “ A wani department kike ne.”
“ Law.”
“ Ok ni kuma ina Computer science, sunana Laylerh.”
“ Ayya ni kuma Meerah.”
“ Wow suna mai dadi, sorry fa na cika ki da surutu ki tafi kar lecture ya wuce ki idan kika fito zamu hadu.”
Murmushi Meerah ta mata tana mai wucewa, ita kuma Laylerh ta tafi wajen zama ta zauna.
Tana shiga lecturer ya shigo, nan aka fara lecture bai barsu ba sai da suka yi kusan awa biyu da mintuna kafin ya fita.
Duk ta bi ta gaji ga yunwar dake dawainiya da ita, tashi tayi zata fita. “ Meerah Abdulrazak Alhassan.” Da sauri ta juyo dan ganin wani isheshen ne.
Kyakyawan saurayi ne wanda akalla bazai wuce ashirin da tara ba, dogo ne sai dai kuma ba fari bane, murmushi ya sakar mata yana isowa inda take tare da cewa. “ Ina ta miki magana tun last week shine kike min yanga ko, irin mun kusa gamawa din nan.”
Murmushi ta masa kafin ta ce. “ Ai kasan ana tests ne duk hankalina ya koma kan karatu, amma kayi hakuri.”
Kafada ya daga tare da cewa. “ Ya na iya, dole nayi hakuri dake ai muje ko.”
Fita sukayi daga hall din suna hira, cikin hiran ne yake ce mata. “ Meerah wai ina Meemah ne bana ganin ta 2days fa.”
“ Kuma yau tare muka shigo da ita ba.”
“ Haba dan Allah.”
“ Da gaske, kila tana ta wajen department na su.”
“ Meemah gidan surutu ba, nikam yaushe zan turo ne?.”
“ Waye zaka turo?.”
“ Magabata na mana, so nake ayi maganar gemu da gemu in yaso kina gaba Makarantar sai muyi bikin.”
Cak ta tsaya tana kare masa kallo, nan da nan ta hade rai tana cewa. “ Ko zanyi aure ba yanzu ba Alwan, sai na cika muradai na kafin nan.”
Kasa yayi da kansa yanda zai kalli cikin idanunta, kafin ya furta. “ Tare zamu cika muradin naki, idan ban aure ki ba Meerah to har abada bazan yi aure ba.”
Sauri kallon shi tayi, kai ya daga mata alamun eh abunda kika ji shi na fada. “ Banaso mutum ya cutu ta dalili na ne Alwan.”
“ Nasan bazan taba cutuwa ba inde ke ne.” Ya fada yana kallon hararan da Laylerh take masa, murmushi ya sakar mata zai yi magana ta karaso gurin da suke tana cewa. “ Kai kam ka boni, sai ace ai baya kula mata yanzu namiji kake kulawa ko.”
Sosa keya yayi yana cewa. “ Laylerh me ya kawo ki nan kuma?.”
Tabe baki tayi tana kallon inda Meerah take tana cewa. “ Gurin In-law nazo, dan kaima kasan idan kai ne bazan taba zuwa ba.”
Murmushi Meerah ta mata kawai, shi kuma ya ce. “ Waye ne In-law naki?.”
“ Mu nawa ka gani a nan da kake min tambayar iskanci?.”
“ Idan Meerah ce to na kai sadaki tun tuni.”
“ Allah tsinewa mai karya, kuma idan ban fadawa Big bro ba cewa ka zage shi.”
Saurin cewa ya yi. “ Laylerh kina yi kina tsoron Allah.”
“ Kama ce bana tsoron Allah kawai.”
“ Ban fada ba ni.”
Murguda masa baki tayi tana jan hannun Meerah da ta zama yar kallo suka bar gurin tana cewa. “ Kar ki biyewa yaran nan, dan ke matar Big bro ne.”
“ Ikon Allah.” Ta furta lokacin da suka zauna a karkashen bishiya.
“ Ni sunana Amina Junaid ya ga Marigayi Alhaji Junaid dala, sannan kanwa ga Most richest Man ina Kaduna Alyan Junaid Dala.”
Saurin kallon ta Meerah tayi zuciyarta na harba tara tara, nan taga kamannin su sak a fuskarta, muryanta har rawa ya fara gurin furta. “ Wani Alyan din?.”
“ Naga yana yin ki ya chanja da damuwa ne ko akwai wani abu ne?.”
Girgiza mata kai tayi tana kallon ta.
“ Alyan dai daya, dan nasan shine most popular a garin kaduna.”
Gyara natsuwar ta tayi tana cewa. “ Amma ya akayi bansan shi ba.”
Kallon kin raina min hankali Laylerh ta mata tana hade rai. “ Ni zaki cewa baki san Alyan ba, yanda sunan shi yayi tsaura a garin nan shine baki san shi ba.”
Tabe baki Meerah ta yi tana furta. “ Ban san shi ba nikam.”
Wayanta ta ciro daga cikin handbag din ta ta kunna ta shiga photos, photon da sukayi tare ta nuna mata tana cewa. “ Baki san shi ba?.”
Kallon kurilla take yiwa photon dan ko a mafarki ta tashi zata gane shi, saurin dauke idanunta tayi daga kan wayan tana tabe baki, murmushi Laylerh ta mata tana ta fara waka neman magana. “ Ta kamu na gane ta kamu, taga kyakyawa ta kamu sosai.”
“ Waye wai ya kamun ne?.”
“ Ni fa ban kira suna ba madam waka kawai nake.”
“ Ok.”
Hango Meemah tayi da Yasmeen da alama ita suke dubawa, hannu ta daga musu kafin duka karaso gurin nasu, kallon Laylerh Meemah tayi tana cewa. “ Kamar nasan fuskar nan?.”
Murmushi ta mata tare da cewa. “ Maybe za ki sani ko ta dalilin Yayana.”
“ Ayya ya school to?.”
“ Alhamdulillah.” Ta furta tana kallon Yasmeen. “ Yasmeen har an gama lecture din?.”
“ An gama ai kin ki shiga.”
“ Lecturer din ne kwata-kwata bai iya ba, yana yi yana face majina ina zan iya.”
Dariya suka yi dukan su. “ Allah fa haushi yake bani kawai.”
“ Lallai ai kuwa gwara ki dage dan ba haka ba kina cikin masu CO wannan karan.” Cewar Yasmeen.
“ Allah ma ya kiyaye.”
Suka hada baki gurin furta. “ Ameen.”
“ Zamu iya tafiya ai ko?.” Cewar Meerah tana tashi.
“ In-law wani unguwa za kuje?.”
“ Dukan mu ai gidan mu daya.” Cewar Yasmeen.
“ Haba, ai dama nace zan zowa Yasmeen tun da Oga baya kasar.”
Da sauri Meerah ta ce. “ Kina da aure ne?.”
Dariya ta mata tana cewa. “ Wanda na nuna miki shine ai mijin ko kina kishi ne?.” Ta fada tana daga mata gira.
“ Kai haba dai kishi kuma shi a suwa, wannan ne zanyi kishi akai.” Ta fada tana yin gaba, biyo bayanta suka yi Laylerh sai neman tsokana take wai jini yaja ta kaysa da yayanta, ita dai ko magana bata kuma yi mata ba.
Tafiya sosai suka yi kafin suka iso bakin get din Makarantar suna dan taba hira, Yasmeen ce ta ce. “ Yau babu mota ne Laylerh?.”
“ Yaya yace wai idan baza’a kai ni ba to bazan yi tuki ba, shiyasa naga gwara na rin ga hawa Napep kawai.”
Ita dai Meerah bin ta da ido kawai take, tana jin yanda take yaba yayan nata da kuma yanda take tsoron shi, tabe baki tayi tana jin haushin kowa.
Napep suka tara Laylerh ta hau suma suka tara wani suka tafi gida.
“ Kin ga yanda yake shishige mata kuwa, idan ban kashe yarinyar nan ba Luby bazan ji dadi ba sam.” Cewar wata budurwa da take tsaye taci uwar bleaching ita da kawayen ta biyu.
Dayar ce me suna Zuby ta yi dariya. “ Kee ai nemo gardi zamuyi ya mata kaca-kaca ta yanda bazata ganu ba, ko kuma a watsa mata acid.”
Tafawa suka yi Sumy na cewa. “ Shiyasa nake ji daku kawayen arziki, amma nifa nafi so a mata fyade ko ya kuka gani?.”
Luby ce tayi murmushi tana cewa. “ Amma kar garin nemo kiba a samo rama fa.”
“ Ke babu ramar da za’a samo ku shiga mota muje.” Cewar Sumy tana tada mota, Zuby ce ta zauna a gurin me zaman banza ita kuma Luby ta zauna a baya, kida ta kunna musu suna tashewa.
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
23 - 24 *💅BA KAI NAKE SO BA💅*
_The story is all about love, romantic, sacrifice, heartbreak and destiny_
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*FATIMA ISA MANU💐*
*( DR TEEMAH)🦋🕊*
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
Masu neman littafin *BA KAI NAKE SO BA* daga farko tare da sauran littafina zaku iya following channel ɗi na dan samu👇https://whatsapp.com/channel/0029Vaf6CpQDuMRYD1FMD92T
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IKUcfCN5rPQ9o0CaBtB2qP
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️*
Tun ranar da sukayi waya dashi ta cire sim din ta ajiye ta cigaba da harkan ta, sosai tayi kyau tayi haske abun har mamaki yake bawa su Meemah da Yasmeen, dan shi Mansoor sai dai ya bita da ido kawai yana ganin yanda take kara kyau, duk da kuwa kullum cikin hijabi take.
Yau ya kama Wednesday kuma suna da lecture daga karfe goma zuwa sha biyu, sauri sauri suka gama aikinsu suka fice daga gidan dukan su uku.
Meemah da Yasmeen gyale suka saka ita kuma ta saka hijab blue wanda ya haska farin fatarta da ya kara haske sosai, hira suke suna tafiya ita dai Meerah sai dai tayi murmushi idan na yi ne, idan kuma na shuru ne tayi, da haka suka isa bakin titi, mai adaidaita sahu suka tara suka fada masa inda zai kai su, da haka suka shiga yaja suka nufi bus stop.
Suna isa bus stop Meerah ta bashi kudinsa, Napep suka shiga su uku ya jasu suka tafi.
Kowa hanyar department nashi ya nufa, ita Meemah ta nufa Physiology department, Yasmeen kuma Computer science , Meerah kuma Law.
Sauri take dan baifi saura minti biyar a shiga ba, buguwa tayi da wata budurwa har ta watsar mata da takaddu.
“ Yi hakuri dan Allah sauri nake ban ganki ba.” Ta fada tana durkusawa ta fara tattare mata takardun ta mika mata.
Karba tayi tana mata murmushi tare da cewa. “ Bakomai Nagode.”
Murmushi Meerah ta mata tana k’ok’arin wucewa.
Budurwar ce ta dafa ta tana cewa. “ A wani department kike ne.”
“ Law.”
“ Ok ni kuma ina Computer science, sunana Laylerh.”
“ Ayya ni kuma Meerah.”
“ Wow suna mai dadi, sorry fa na cika ki da surutu ki tafi kar lecture ya wuce ki idan kika fito zamu hadu.”
Murmushi Meerah ta mata tana mai wucewa, ita kuma Laylerh ta tafi wajen zama ta zauna.
Tana shiga lecturer ya shigo, nan aka fara lecture bai barsu ba sai da suka yi kusan awa biyu da mintuna kafin ya fita.
Duk ta bi ta gaji ga yunwar dake dawainiya da ita, tashi tayi zata fita. “ Meerah Abdulrazak Alhassan.” Da sauri ta juyo dan ganin wani isheshen ne.
Kyakyawan saurayi ne wanda akalla bazai wuce ashirin da tara ba, dogo ne sai dai kuma ba fari bane, murmushi ya sakar mata yana isowa inda take tare da cewa. “ Ina ta miki magana tun last week shine kike min yanga ko, irin mun kusa gamawa din nan.”
Murmushi ta masa kafin ta ce. “ Ai kasan ana tests ne duk hankalina ya koma kan karatu, amma kayi hakuri.”
Kafada ya daga tare da cewa. “ Ya na iya, dole nayi hakuri dake ai muje ko.”
Fita sukayi daga hall din suna hira, cikin hiran ne yake ce mata. “ Meerah wai ina Meemah ne bana ganin ta 2days fa.”
“ Kuma yau tare muka shigo da ita ba.”
“ Haba dan Allah.”
“ Da gaske, kila tana ta wajen department na su.”
“ Meemah gidan surutu ba, nikam yaushe zan turo ne?.”
“ Waye zaka turo?.”
“ Magabata na mana, so nake ayi maganar gemu da gemu in yaso kina gaba Makarantar sai muyi bikin.”
Cak ta tsaya tana kare masa kallo, nan da nan ta hade rai tana cewa. “ Ko zanyi aure ba yanzu ba Alwan, sai na cika muradai na kafin nan.”
Kasa yayi da kansa yanda zai kalli cikin idanunta, kafin ya furta. “ Tare zamu cika muradin naki, idan ban aure ki ba Meerah to har abada bazan yi aure ba.”
Sauri kallon shi tayi, kai ya daga mata alamun eh abunda kika ji shi na fada. “ Banaso mutum ya cutu ta dalili na ne Alwan.”
“ Nasan bazan taba cutuwa ba inde ke ne.” Ya fada yana kallon hararan da Laylerh take masa, murmushi ya sakar mata zai yi magana ta karaso gurin da suke tana cewa. “ Kai kam ka boni, sai ace ai baya kula mata yanzu namiji kake kulawa ko.”
Sosa keya yayi yana cewa. “ Laylerh me ya kawo ki nan kuma?.”
Tabe baki tayi tana kallon inda Meerah take tana cewa. “ Gurin In-law nazo, dan kaima kasan idan kai ne bazan taba zuwa ba.”
Murmushi Meerah ta mata kawai, shi kuma ya ce. “ Waye ne In-law naki?.”
“ Mu nawa ka gani a nan da kake min tambayar iskanci?.”
“ Idan Meerah ce to na kai sadaki tun tuni.”
“ Allah tsinewa mai karya, kuma idan ban fadawa Big bro ba cewa ka zage shi.”
Saurin cewa ya yi. “ Laylerh kina yi kina tsoron Allah.”
“ Kama ce bana tsoron Allah kawai.”
“ Ban fada ba ni.”
Murguda masa baki tayi tana jan hannun Meerah da ta zama yar kallo suka bar gurin tana cewa. “ Kar ki biyewa yaran nan, dan ke matar Big bro ne.”
“ Ikon Allah.” Ta furta lokacin da suka zauna a karkashen bishiya.
“ Ni sunana Amina Junaid ya ga Marigayi Alhaji Junaid dala, sannan kanwa ga Most richest Man ina Kaduna Alyan Junaid Dala.”
Saurin kallon ta Meerah tayi zuciyarta na harba tara tara, nan taga kamannin su sak a fuskarta, muryanta har rawa ya fara gurin furta. “ Wani Alyan din?.”
“ Naga yana yin ki ya chanja da damuwa ne ko akwai wani abu ne?.”
Girgiza mata kai tayi tana kallon ta.
“ Alyan dai daya, dan nasan shine most popular a garin kaduna.”
Gyara natsuwar ta tayi tana cewa. “ Amma ya akayi bansan shi ba.”
Kallon kin raina min hankali Laylerh ta mata tana hade rai. “ Ni zaki cewa baki san Alyan ba, yanda sunan shi yayi tsaura a garin nan shine baki san shi ba.”
Tabe baki Meerah ta yi tana furta. “ Ban san shi ba nikam.”
Wayanta ta ciro daga cikin handbag din ta ta kunna ta shiga photos, photon da sukayi tare ta nuna mata tana cewa. “ Baki san shi ba?.”
Kallon kurilla take yiwa photon dan ko a mafarki ta tashi zata gane shi, saurin dauke idanunta tayi daga kan wayan tana tabe baki, murmushi Laylerh ta mata tana ta fara waka neman magana. “ Ta kamu na gane ta kamu, taga kyakyawa ta kamu sosai.”
“ Waye wai ya kamun ne?.”
“ Ni fa ban kira suna ba madam waka kawai nake.”
“ Ok.”
Hango Meemah tayi da Yasmeen da alama ita suke dubawa, hannu ta daga musu kafin duka karaso gurin nasu, kallon Laylerh Meemah tayi tana cewa. “ Kamar nasan fuskar nan?.”
Murmushi ta mata tare da cewa. “ Maybe za ki sani ko ta dalilin Yayana.”
“ Ayya ya school to?.”
“ Alhamdulillah.” Ta furta tana kallon Yasmeen. “ Yasmeen har an gama lecture din?.”
“ An gama ai kin ki shiga.”
“ Lecturer din ne kwata-kwata bai iya ba, yana yi yana face majina ina zan iya.”
Dariya suka yi dukan su. “ Allah fa haushi yake bani kawai.”
“ Lallai ai kuwa gwara ki dage dan ba haka ba kina cikin masu CO wannan karan.” Cewar Yasmeen.
“ Allah ma ya kiyaye.”
Suka hada baki gurin furta. “ Ameen.”
“ Zamu iya tafiya ai ko?.” Cewar Meerah tana tashi.
“ In-law wani unguwa za kuje?.”
“ Dukan mu ai gidan mu daya.” Cewar Yasmeen.
“ Haba, ai dama nace zan zowa Yasmeen tun da Oga baya kasar.”
Da sauri Meerah ta ce. “ Kina da aure ne?.”
Dariya ta mata tana cewa. “ Wanda na nuna miki shine ai mijin ko kina kishi ne?.” Ta fada tana daga mata gira.
“ Kai haba dai kishi kuma shi a suwa, wannan ne zanyi kishi akai.” Ta fada tana yin gaba, biyo bayanta suka yi Laylerh sai neman tsokana take wai jini yaja ta kaysa da yayanta, ita dai ko magana bata kuma yi mata ba.
Tafiya sosai suka yi kafin suka iso bakin get din Makarantar suna dan taba hira, Yasmeen ce ta ce. “ Yau babu mota ne Laylerh?.”
“ Yaya yace wai idan baza’a kai ni ba to bazan yi tuki ba, shiyasa naga gwara na rin ga hawa Napep kawai.”
Ita dai Meerah bin ta da ido kawai take, tana jin yanda take yaba yayan nata da kuma yanda take tsoron shi, tabe baki tayi tana jin haushin kowa.
Napep suka tara Laylerh ta hau suma suka tara wani suka tafi gida.
“ Kin ga yanda yake shishige mata kuwa, idan ban kashe yarinyar nan ba Luby bazan ji dadi ba sam.” Cewar wata budurwa da take tsaye taci uwar bleaching ita da kawayen ta biyu.
Dayar ce me suna Zuby ta yi dariya. “ Kee ai nemo gardi zamuyi ya mata kaca-kaca ta yanda bazata ganu ba, ko kuma a watsa mata acid.”
Tafawa suka yi Sumy na cewa. “ Shiyasa nake ji daku kawayen arziki, amma nifa nafi so a mata fyade ko ya kuka gani?.”
Luby ce tayi murmushi tana cewa. “ Amma kar garin nemo kiba a samo rama fa.”
“ Ke babu ramar da za’a samo ku shiga mota muje.” Cewar Sumy tana tada mota, Zuby ce ta zauna a gurin me zaman banza ita kuma Luby ta zauna a baya, kida ta kunna musu suna tashewa.
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
23 - 24 *💅BA KAI NAKE SO BA💅*
_The story is all about love, romantic, sacrifice, heartbreak and destiny_
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*FATIMA ISA MANU💐*
*( DR TEEMAH)🦋🕊*
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
Masu neman littafin *BA KAI NAKE SO BA* daga farko tare da sauran littafina zaku iya following channel ɗi na dan samu👇https://whatsapp.com/channel/0029Vaf6CpQDuMRYD1FMD92T
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IKUcfCN5rPQ9o0CaBtB2qP
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️*