Sashe 32
Aziza da Azima Macizai Ne Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Da sallama suka shiga Sultana ce a gaba sai Aziza dake binta a baya kanta a duƙe cikin hijabi gabanta na faduwa, yana kwance a dogon kujera yana sanye da jallabiyya, amsa sallamar tasu ya yi yana tashi zaune, da sauri Sultana ta ajiye tray din hannunta ta zauna kusa da shi tana masa sannu da zuwa,kanta ya shafa cikin kulawa yana amsawa, duƙawa kasa Aziza ta yi bakinta na rawa ta ce
"Ina wuni *HAMMA NAWAZ* ya hanya?" rassrassras! gaban Nawaz ya faɗi ya ƙura mata ido amma ta gefen ido yana kallon yadda take rirriƙe yatsun hannunta jikinta na rawa daga nesa yake karantar yanayinta duk da ta boye fuskarta cikin hijabi sai saitin ƙaramin bakinta da yake iya hangowa wanda shi ma ke b'ari,
"HAMMA NAWAZ!" yake ta nanatawa a ransa, Aziza kuwa jin bai amsa mata gaisuwarta ba alhali ya amsa na kanwarsa yasa ta tashi a hankali jiki a sanyaye zata fita, watakila baya amsa gaisuwar masu aiki, har ta kai bakin kofa sai taji Sultana na faɗin Aziza ina kuma zakije?"
"Amm dama Anty Sultana dama akwai kayan da ban....kwa. She...ba...ina...so..ne...naje....na kwashe" ta karasa maganar da in-ina tana fita da sauri, cikin fuskar tausayi Sultana ta juyo ta kalli Yayanta ta ce
"Bro,wlh Aziza bata ji dadi ba, ta gaisheka baka amsa ba fa,kuma kamar ma naga tsoronka takeji"
"Za ki yi serving ɗina ne ko zaki cika min ciki da magana?" ya faɗa ba tare da ya kalleta ba, kasancewar tasan halinsa yasa ta zuba masa abincin ta ajiye masa komai sannan ta fice itama,tana fita ya dauki spoon zai kai abincin bakinsa sai ya tsinci kansa cikin rashin jin dadin amsa gaisuwarta da bai yi ba, HAMMA NAWAZ! ya faɗa a fili ya saki murmushi jin yadda ta kira cike da harshen fullaci kuma sai sunan ya yi daɗi a bakinta, da kyar ya lallaba ya ci abinci dan kuwa yaji dadin abincin sosai yaci yasha zobon da suka haɗa ya yi hamdala, nan ya zauna suna waya da amininsa yana gaya masa ranar thursday In sha Allahu yana hanya zai bi jirgi amma sai ya ƙara komawa ta abuja, Allah ya kawo shi lafiya ya yi masa,yana kan waya har aka kira sallar magriba dan haka yace masa za shi masallaci suka yi sallama akan cewa sai sunyi waya anjima, alwala Nawaz ya yi ya tafi masallaci bai dawo ba sai da ya haɗa da isha'i, ko da ya shigo gida babban parlourn gidansu ya wuce da sallama ya shiga a lokacin Aziza na riƙe da kaskon turaren wuta ita kadai ce ma a parlourn, jin sallamarsa yasa jikinta ya dauki rawa wanda bata san dalilin hakan ba, cikin rawar murya ta amsa sallamar ta shi ta ajiye kaskon hannunta tana shirin shigewa daki da gudu taji muryarsa kamar daga sama
"Ya kike? ya jikin naki? Yanzu babu inda yake miki ciwo ko?" ya faɗa lokaci daya,cak Aziza taja ta tsaya,a iya saninta Sultana da Mom suna sama,to kenan da ita yake yi? take tambayar kanta, bata amsa ba bata juyo ba sai da taji ya sake fadin
"AZIZA baki ji ina miki magana ne?" sai a sannan ta juyo murya na rawa ta ce
"Alhamdulillah na warke" tana gama fadi ta shige daki, shuru ya ɗan yi yana nazartan yarinyar daga baya kuma ya yi tsaki ya hau sama,dakin Mom ya je ya kwanta a gadonta suna hira, Mom ta ce
"Bana ma kenan a kasar waje zaku sake yin Azumi ga Azumi ya ƙarato, meyasa ba zaka sa amininka ya dawo nigeria kuyi azumi a gida ba? Bana dai ace kunyi sallah a kasarku tare damu"
"Mom kema kin san ba zai dawo ba ko da na faɗa masa, azumi kuma In sha Allahu mai zuwa idan rai ya kaimu ai muna nan a gida In sha Allah" Mom ta sauke ajiyar zuciya ta ce
"Ai ya kamata,ni na ƙagu ku dawo dan ku nemo matar aure ku aura,barin ma Son yana da bukatar mata wacce zata kula da shi"
"Ai ya samu Mom"
Mom ta ce
"A'a gwara dai fa ya samo mai tarbiyya da natsuwa da hankali" Nawaz ya tabe baki ya ce
"Humm wanda yake fadin zai aura ni kwata-kwata bata min ba,bamu shiri da ita ko kadan amma shi yace zai aureta,kuma abun takaicin fa Mom shima ba sonta yakeyi ba"
"To ina ruwanka? kai fa matsalarka Nawaz zafin zuciya" Mom ta fada tana kallonsa
"Mom ai ba zan can ina ruwana bane ko zafin zuciya,magana ce ta gaskiya,kuma ai abunda ya shafesa ya shafeni"
"To kawai ka tayasa da addua shine babban soyayyar da zaka ci gaba da nuna masa"
"In sha Allah Mom" daga haka suka ci gaba da hirarsu,bai baro dakin Mom ba kuwa sai sha biyu na dare yana fitowa ya shiga dakin Sultana bata nan,tana can dakin Aziza tana koya mata karatu,cikin ikon Allah Aziza ke ganewa, da bai ganta a dakin ba ya yi tunanin ko tana toilet ne dan haka ya wuce part dinsa ya kwanta, sai sha biyu da rabi Sultana ta miƙe tana fadin
"To Aziza bari mu dakata da karatun haka sai Allah ya kaimu gobe kuma, yanzu akwai wani horror series film din da nake kalla, 12 ake farawa a gama 1:30 ga shi yanzu har sha biyu da rabi sai dai na kalli karashi,ko zaki zo muje ki kalla ne?" Aziza ta ce
"Me hakan ke nufi? shi horror din" sai da Sultana tayi dariya kafin ta ce
"Ina nufin fina-finan dodanni, kamar irinsu abun tsoro haka da film din macizai!" rassssss! gaban Aziza ya buga ta yi sauri dago fuskarta ta kalli Sultana ta tsakiyar gashinta da ya rufe mata fuska,Sultana ta kwashe da dariya ta ce
"Matsoraciya kawai,daga faɗa miki har kin firgita, wlh kuma fa Yaya ya hanani kalla har cewa yake min ranar da na fara ganinsu a zahiri zan sani, yanzun ma inada tabbacin ya tafi part dinsa,kinga sai da safe" tana fadi ta fice ta bar Aziza da zare ido tana tunanin ranar da Sultana zata ganta a macijiya mai zai faru? Saurin kau da tunanin ta yi tana fadin "taya ma hakan zata faru?" ajiye tunanin tayi a gefe ta shiga ta ɗauro alwala ta tada sallah,ta jima tana addua tana kuka tana neman taimakon mahaliccinta.
🍃🍃🍃🍃🍃
Kwana a tashi ba wuya a wajan Allah, Azima duk hankalinta ta karkata shi wajan sakawa su Maman Hanan da Maman Beenah ido ganin manaƙisan da suke kullawa wanda bai ji ba bai gani ba, ta sha jin haushin kanta a kan ƙutse da take yiwa wanda bai san da ita ba kamar yadda itama bata san da shi ba, ga shi duk sadda ta yi yunkurin barin gidan sai taji kamar an ɗaure mata kafafu,wannan gida ya zame mata karfen kafa.
🍃🍃🍃🍃
Ana gobe Nawaz sai tafi abuja jibi kuma zai wuce america ya yi wani mugun mafarkin da ya gigita duniyarsa, Aziza ce ya gani a jejin da yafi na kullum muni tana kuka tana miƙa masa hannu ya taimaketa, kar ya tafi ya taimaka mata,ƙiri-kiri ya ganta a macijiya.
🍃🍃🍃🍃
A Lallaba yau aiki yamin yawa🏃🏻♀️
MOMYN AHLAN✍🏻
[4/13, 10:12 AM] Mom Ahlan: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)
MALLAKAR.
*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*
SAHIBAR KAINUWA.
Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.
Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_
_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_
🍃🍃🍃🍃🍃
*PAID.*
🅿️=4️⃣1️⃣↪️4️⃣2️⃣
"Ina wuni *HAMMA NAWAZ* ya hanya?" rassrassras! gaban Nawaz ya faɗi ya ƙura mata ido amma ta gefen ido yana kallon yadda take rirriƙe yatsun hannunta jikinta na rawa daga nesa yake karantar yanayinta duk da ta boye fuskarta cikin hijabi sai saitin ƙaramin bakinta da yake iya hangowa wanda shi ma ke b'ari,
"HAMMA NAWAZ!" yake ta nanatawa a ransa, Aziza kuwa jin bai amsa mata gaisuwarta ba alhali ya amsa na kanwarsa yasa ta tashi a hankali jiki a sanyaye zata fita, watakila baya amsa gaisuwar masu aiki, har ta kai bakin kofa sai taji Sultana na faɗin Aziza ina kuma zakije?"
"Amm dama Anty Sultana dama akwai kayan da ban....kwa. She...ba...ina...so..ne...naje....na kwashe" ta karasa maganar da in-ina tana fita da sauri, cikin fuskar tausayi Sultana ta juyo ta kalli Yayanta ta ce
"Bro,wlh Aziza bata ji dadi ba, ta gaisheka baka amsa ba fa,kuma kamar ma naga tsoronka takeji"
"Za ki yi serving ɗina ne ko zaki cika min ciki da magana?" ya faɗa ba tare da ya kalleta ba, kasancewar tasan halinsa yasa ta zuba masa abincin ta ajiye masa komai sannan ta fice itama,tana fita ya dauki spoon zai kai abincin bakinsa sai ya tsinci kansa cikin rashin jin dadin amsa gaisuwarta da bai yi ba, HAMMA NAWAZ! ya faɗa a fili ya saki murmushi jin yadda ta kira cike da harshen fullaci kuma sai sunan ya yi daɗi a bakinta, da kyar ya lallaba ya ci abinci dan kuwa yaji dadin abincin sosai yaci yasha zobon da suka haɗa ya yi hamdala, nan ya zauna suna waya da amininsa yana gaya masa ranar thursday In sha Allahu yana hanya zai bi jirgi amma sai ya ƙara komawa ta abuja, Allah ya kawo shi lafiya ya yi masa,yana kan waya har aka kira sallar magriba dan haka yace masa za shi masallaci suka yi sallama akan cewa sai sunyi waya anjima, alwala Nawaz ya yi ya tafi masallaci bai dawo ba sai da ya haɗa da isha'i, ko da ya shigo gida babban parlourn gidansu ya wuce da sallama ya shiga a lokacin Aziza na riƙe da kaskon turaren wuta ita kadai ce ma a parlourn, jin sallamarsa yasa jikinta ya dauki rawa wanda bata san dalilin hakan ba, cikin rawar murya ta amsa sallamar ta shi ta ajiye kaskon hannunta tana shirin shigewa daki da gudu taji muryarsa kamar daga sama
"Ya kike? ya jikin naki? Yanzu babu inda yake miki ciwo ko?" ya faɗa lokaci daya,cak Aziza taja ta tsaya,a iya saninta Sultana da Mom suna sama,to kenan da ita yake yi? take tambayar kanta, bata amsa ba bata juyo ba sai da taji ya sake fadin
"AZIZA baki ji ina miki magana ne?" sai a sannan ta juyo murya na rawa ta ce
"Alhamdulillah na warke" tana gama fadi ta shige daki, shuru ya ɗan yi yana nazartan yarinyar daga baya kuma ya yi tsaki ya hau sama,dakin Mom ya je ya kwanta a gadonta suna hira, Mom ta ce
"Bana ma kenan a kasar waje zaku sake yin Azumi ga Azumi ya ƙarato, meyasa ba zaka sa amininka ya dawo nigeria kuyi azumi a gida ba? Bana dai ace kunyi sallah a kasarku tare damu"
"Mom kema kin san ba zai dawo ba ko da na faɗa masa, azumi kuma In sha Allahu mai zuwa idan rai ya kaimu ai muna nan a gida In sha Allah" Mom ta sauke ajiyar zuciya ta ce
"Ai ya kamata,ni na ƙagu ku dawo dan ku nemo matar aure ku aura,barin ma Son yana da bukatar mata wacce zata kula da shi"
"Ai ya samu Mom"
Mom ta ce
"A'a gwara dai fa ya samo mai tarbiyya da natsuwa da hankali" Nawaz ya tabe baki ya ce
"Humm wanda yake fadin zai aura ni kwata-kwata bata min ba,bamu shiri da ita ko kadan amma shi yace zai aureta,kuma abun takaicin fa Mom shima ba sonta yakeyi ba"
"To ina ruwanka? kai fa matsalarka Nawaz zafin zuciya" Mom ta fada tana kallonsa
"Mom ai ba zan can ina ruwana bane ko zafin zuciya,magana ce ta gaskiya,kuma ai abunda ya shafesa ya shafeni"
"To kawai ka tayasa da addua shine babban soyayyar da zaka ci gaba da nuna masa"
"In sha Allah Mom" daga haka suka ci gaba da hirarsu,bai baro dakin Mom ba kuwa sai sha biyu na dare yana fitowa ya shiga dakin Sultana bata nan,tana can dakin Aziza tana koya mata karatu,cikin ikon Allah Aziza ke ganewa, da bai ganta a dakin ba ya yi tunanin ko tana toilet ne dan haka ya wuce part dinsa ya kwanta, sai sha biyu da rabi Sultana ta miƙe tana fadin
"To Aziza bari mu dakata da karatun haka sai Allah ya kaimu gobe kuma, yanzu akwai wani horror series film din da nake kalla, 12 ake farawa a gama 1:30 ga shi yanzu har sha biyu da rabi sai dai na kalli karashi,ko zaki zo muje ki kalla ne?" Aziza ta ce
"Me hakan ke nufi? shi horror din" sai da Sultana tayi dariya kafin ta ce
"Ina nufin fina-finan dodanni, kamar irinsu abun tsoro haka da film din macizai!" rassssss! gaban Aziza ya buga ta yi sauri dago fuskarta ta kalli Sultana ta tsakiyar gashinta da ya rufe mata fuska,Sultana ta kwashe da dariya ta ce
"Matsoraciya kawai,daga faɗa miki har kin firgita, wlh kuma fa Yaya ya hanani kalla har cewa yake min ranar da na fara ganinsu a zahiri zan sani, yanzun ma inada tabbacin ya tafi part dinsa,kinga sai da safe" tana fadi ta fice ta bar Aziza da zare ido tana tunanin ranar da Sultana zata ganta a macijiya mai zai faru? Saurin kau da tunanin ta yi tana fadin "taya ma hakan zata faru?" ajiye tunanin tayi a gefe ta shiga ta ɗauro alwala ta tada sallah,ta jima tana addua tana kuka tana neman taimakon mahaliccinta.
🍃🍃🍃🍃🍃
Kwana a tashi ba wuya a wajan Allah, Azima duk hankalinta ta karkata shi wajan sakawa su Maman Hanan da Maman Beenah ido ganin manaƙisan da suke kullawa wanda bai ji ba bai gani ba, ta sha jin haushin kanta a kan ƙutse da take yiwa wanda bai san da ita ba kamar yadda itama bata san da shi ba, ga shi duk sadda ta yi yunkurin barin gidan sai taji kamar an ɗaure mata kafafu,wannan gida ya zame mata karfen kafa.
🍃🍃🍃🍃
Ana gobe Nawaz sai tafi abuja jibi kuma zai wuce america ya yi wani mugun mafarkin da ya gigita duniyarsa, Aziza ce ya gani a jejin da yafi na kullum muni tana kuka tana miƙa masa hannu ya taimaketa, kar ya tafi ya taimaka mata,ƙiri-kiri ya ganta a macijiya.
🍃🍃🍃🍃
A Lallaba yau aiki yamin yawa🏃🏻♀️
MOMYN AHLAN✍🏻
[4/13, 10:12 AM] Mom Ahlan: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)
MALLAKAR.
*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*
SAHIBAR KAINUWA.
Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.
Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_
_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_
🍃🍃🍃🍃🍃
*PAID.*
🅿️=4️⃣1️⃣↪️4️⃣2️⃣