Sashe 29
Aziza da Azima Macizai Ne Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana isa ko parking bai gama ba ya shiga ciki da sauri,yana shiga reception ya samu nurses ɗin suna bacci, a tsawance ya tayar dasu nan ya hau su da faɗa a kan basu san aikinsu ba, hakuri suka hau ba shi amma bai tsaya ya sauraresu ba illa dakin da Aziza ke kwance,kamar yadda ya barta jiya haka ya sameta tana bacci gashinta ya rufe mata fuska,yana ganin lafiyarta ya saki ajiyar zuciya wanda bai san dalilin hakan ba bai ma san lokacin da ya saki ba, dubata ya sake yi ya ga zata iya farkawa ko da wani lokaci, hannu yasa da niyyar kwashe gashin fuskarta a fili ya ce
"Wai meke damuna ne kam? Mtsww!" ya ɗan ja gajerar tsaki yana fita a dakin, gida ya koma dan kansa ke masa ciwo sosai,magani ya sha cikin ikon Allah bacci ya kwashesa bai farka ba sai daya saura,yana tashi ana kiran sallar azahar, bai tsaya bata lokaci ba ya yi alwala ya tafi masallaci bayan ya dawo babban parlour ya wuce ya samu Mom da Sultana suna zaune suna hira, gaishe da Mom ya sake yi ta amsa Sultana ta gaishesa ya amsa yana haɗe rai da fadin
"Keee me ya hanaki zuwa skull?"
"Brother yau bani da komai shiyasa ban je ba"
"Kin san dai bana son wasa da karatu ko?"
"E Brother bana wasa da karatu ko Mom?" ta fada a shagwabe tana kallon Mom,Mom ta yi murmushi ta ce
"Ai kai ma kasan yadda Sultana ke son karatu,ya gajiyar hanyan da kuma jikin?"
"Alhamdulillah Mom na warware"
"To Ma sha Allah haka ake so, dama mun gama shiryawa kai muke jira idan ka farka sai mu gaya maka zamu je asibitin duba yarinyar"
"Okay Mom bari nayi wanka sai na kai ku,nima akwai marasa lafiyan da nake son dubawa, gobe kuma zanje abuja akwai aikin da nake da shi"
"Kuma?" cewar Mom,ya ce
"E wlh Mom,ai idan har mun samu sauki sai dai idan mun dawo kasarmu gabadaya,tunda ko kaɗan zuwan nan wan can guy din dan ya raina min wayo ba zuwa yakeyi ba,ya maqale a kasar wasu" murmushi Mom tayi ta ce
"Ka kyalesa mana Nawaz,kasan fa ba jin dadin zama yakeyi dasu Hajiya Lawiza da Hajiya Luba ba, kai mutanan duniya sai Allah wlh,ace kuna zaune karkashin mutum kuna cin albarkacinsa kuna rayuwa da dukiyarsa amma kun tsanesa kuna cin dunduniyarsa,kai Allah shi kyauta" Nawaz ya amsa da amin yana fadin
"Ba ri na shirya nazo na kaiku nima na samu nayi aikin dake gabana a hospital din"
"To a fito lafiya" cewar Mom.
Mintuna sha biyar ya daukesa ya gama shirinsa ya shiga ya yiwa su Mom magana suka fito suka nufi asibiti,ko da sukaje kwatanta musu room din ya yi shi bai shiga ba ya tafi dan akwai cs din da zai yi, su Mom ne suka shiga suka zauna da ita,Sultana tasa hannu ta kwashe mata gashin fuskarta ta ce
"Woww! Allahu Akbar! Ma sha Allah!"
"Menene Sultana?"
"Wlh Mom kyakkyawa da ita, ki ga gashi, wayyo Allah na ni,wlh Mom kamar ba yar nigeria ba" Mom tayi murmushi ta ce
"Baki rabuwa da shiririta Sultana ba bafulatana ba ce"
"Ai wlh Mom ko a fulanin ba kowa ke da kyau ba"
"To anji ki rufe min baki, karki cika marar lafiya da surutu Yayanki ya shigo ya sameki kina zuba zaneki zaiyi kema kin sani" zare ido ta yi tana riƙe bakinta dan tasan sarai zai zanetan sai dai idan bata cika masa ciki ba dan akwai sa da saurin zuciya abu kaɗan ke tunzura shi ransa ya b'aci.
Su na zaune a asibitin sai wajan uku da rabi kafin Aziza ta fara farkawa, farkawartata yazo mata da mugun mafarki Azima ta biyo Baffa da wani zabgegen takwabi tana shirin kashe Baffa bayan sun gama dambatuwa In da Baffa karfinsa ya ƙare ya hau kwalawa Aziza kira ta kawo masa dauki Banju zai kashesa! Ga Hajja a sume a kasa, wani ihu Aziza ta yi dai-dai da lokacin da Nawaz ya sako kafarsa dakin ya zo dubasu ya iske ihunta tana fadin
"BAFFAAAANAAAAA!!! HAJJAAAAA!! KEEEEE!!! AZIMAAAAAA!! KARKI KASHE BAFFAAAA!!" sauri yin kanta suka yi Nawaz ya tallabota kirjinsa ya kalli Sultana yace "maza je ki kirawo min wasu nurses ko Dr duk wanda kika samu su zo yanzu" da gudu Sultana ta fice suka dawo da nurse mutum hudu, nan yace su ba shi allurai, bayan sun miƙa masa ne tana ta faman buge-buge, Mom tana tsaye daga saman kanta tana mata tofi, yana mata alluran ta koma ta yi lamo a kirjinsa tana kan ambatar sunan Baffanta da Hajjanta, kamar da minti biyar abun ya lafa,Mom ta ce
"Nawaz ya dai?"
"Ba komai Mom,nan da 30mins zata farka zata dawo dai-dai In sha Allah" Mom ta ce
"Ka gani ko Nawaz? Gwara da Allah yasa baka barta ba ka taho da ita, Allah ya bata lafiya ya tashi kafaɗunta" ya amsa da amin yana me leƙa fuskarta ya ga gashi ya rufe,kwantar da ita ya yi ya fice, Sultana ta zauna kusa da ita tana kamo hannunta.
Kamar yadda Nawaz ya fada haka kuwa ya kasance 30mins ta farka, tana buɗe ido ta hau bin inda take da kallo, ba dai har ta mutu bane yanzu haka tana lahira? Take tambayar kanta,kallon hannunta ta yi ta ga wata budurwa zaune kusa da ita, ga wata dattijuwar mata zaune hannunta dauke da carbi tana lazimi, budurwar kuma hannunta da waya tana dannawa,saurin janye hannunta Aziza ta yi ta matsa baya, tana dafe kanta da kafarta da ta ga an daure mata shi,nan abunda ya faru ya dawo mata kai, Sultana ta ce
"Sannu kinji! Ya jikin naki?"
"Sultana kira yayanki mana" cewar Mom
"To Mom" Sultana ta faɗa tana ficewa.
Tare suka dawo da shi, a lokacin Aziza na maqale can jikin gado tana wani irin kuka kanta a sunkuye tayi mayafi da gashin kanta, jin magana yasata dagowa kaɗan ganin mutum na matsota ya sakata fashewa da sabon kuka tana fadin
"Aradu karka matso kusa dani" a yadda take magana zaka san babu hausa a harshenta,banza da ita Nawaz ya yi yasa hannu zai tabata ta saki ihu tana kiran sunan Baffa, haushi ne ya kama Nawaz ya daka mata tsawa
"Keeeee!!! Bana son hauka!! Ki natsu!!" Mom tace
"Haba Nawaz!? Miye haka? Ka mata a hankali mana" wani tsoro ne ya kama Aziza,ganin haka yasa Mom matsowa kusa da ita ta ce
"Ɗana ne! Ba zai cutar dake ba, wancan kanwarsa ce, shi kuma likita ne, ya bugeki ne bisa tsautsayi sannan wannan asibitinsa ne yana kula dake,alhamdulillah kin farka, yanzu haka kina garin kaduna ne,munji kina ambatar sunan Baffanki, da kinji sauki zamu maidaki gida kinji ko? Karkiji tsoronsa zai duba ki ne uhum?" Mom ta faɗa tana bubbuga Aziza, dubata Nawaz ya yi ya fice cikin haushi.
🐍🐍🐍🐍🐍
Tun shigan Azima dakin munir da niyyar gyarawa ba a sake ganin mai kama da ita ba, har dare, kuma cikin wani ikon Allah babu wanda ya nemeta,dan sun manta da ita,tunda sun san mai aikinsu ta gudu sun manta sun dauki sabuwa, sai wajan karfe tara Munir ya dawo shi da Baby, bayan sun yi magana da Zuby da Hajiya Baby ta wuce dakinta,Munir ma ya wuce nasa,yana shiga ya yi turuss yana ganin ikon Rabba, Azima ta yi ɗaya-ɗaya a kan gado ta bararraje an samu gado mai laushi bana kara ba, sai kwasar baccinta take cikin salama hankali kwance, gashinta da ya sha wanki sai kyalli yake yi duk ya baje ya rufe mata fuska, wani yawu muqut Munir ya hadiye yana fadin
"Kai daga ina wannan balarabiyan?" ya fada yana yin kanta ba tare da yayi dogon tunani ba shin aljana ce ko mutum.
🍃🍃🍃🍃🍃
MOMYN AHLAN✍🏻
[4/13, 10:12 AM] Mom Ahlan: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)
MALLAKAR.
*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*
SAHIBAR KAINUWA.
Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.
Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_
_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_
🍃🍃🍃🍃🍃
*PAID.*
🅿️==3️⃣9️⃣↪️4️⃣0️⃣
Hannu yasa jikinsa na rawa yana lashe baki yana kwashe gashin da ya rufe mata fuska cikin bacci Azima ta ji mutum a kanta, bata gama tabbatarwa ba sai da taji saitin hannun mutum a wajan dukiyar fulaninta, nan da nan ta farga da abunda ke wakana a kanta, idonta ne ya sauya, da tafin hannunta ta tokari kirjin Munir kamar kiftawar ido da bismillah sai ga Munir ya yi sama ya bugu timm da kasa!! Saurin tashi Azima ta yi,ta dauki mayafinta ta yi lullubi sannan ta yi kan Munir,tana zuwa ta shaƙosa da hannu daya ta haɗasa da bango,nan idon Munir ya yi waje yana so ya yi ihu amma baya so kannansa suji su rainasa, lallai yau ba shakka ya yi gamo da aljana a garin ɗan banzan son matan tsiya tun bai tsaya ya ga wacece ba ya afka mata ga shi tana neman kashesa, lokuta da yawa Munir ya sha yiwa yaran aikinsu fyaɗe,da anyi kara kuwa uwarsu zata zuba kuɗi ta karbo ɗanta tace an masa sharri.
"Wai meke damuna ne kam? Mtsww!" ya ɗan ja gajerar tsaki yana fita a dakin, gida ya koma dan kansa ke masa ciwo sosai,magani ya sha cikin ikon Allah bacci ya kwashesa bai farka ba sai daya saura,yana tashi ana kiran sallar azahar, bai tsaya bata lokaci ba ya yi alwala ya tafi masallaci bayan ya dawo babban parlour ya wuce ya samu Mom da Sultana suna zaune suna hira, gaishe da Mom ya sake yi ta amsa Sultana ta gaishesa ya amsa yana haɗe rai da fadin
"Keee me ya hanaki zuwa skull?"
"Brother yau bani da komai shiyasa ban je ba"
"Kin san dai bana son wasa da karatu ko?"
"E Brother bana wasa da karatu ko Mom?" ta fada a shagwabe tana kallon Mom,Mom ta yi murmushi ta ce
"Ai kai ma kasan yadda Sultana ke son karatu,ya gajiyar hanyan da kuma jikin?"
"Alhamdulillah Mom na warware"
"To Ma sha Allah haka ake so, dama mun gama shiryawa kai muke jira idan ka farka sai mu gaya maka zamu je asibitin duba yarinyar"
"Okay Mom bari nayi wanka sai na kai ku,nima akwai marasa lafiyan da nake son dubawa, gobe kuma zanje abuja akwai aikin da nake da shi"
"Kuma?" cewar Mom,ya ce
"E wlh Mom,ai idan har mun samu sauki sai dai idan mun dawo kasarmu gabadaya,tunda ko kaɗan zuwan nan wan can guy din dan ya raina min wayo ba zuwa yakeyi ba,ya maqale a kasar wasu" murmushi Mom tayi ta ce
"Ka kyalesa mana Nawaz,kasan fa ba jin dadin zama yakeyi dasu Hajiya Lawiza da Hajiya Luba ba, kai mutanan duniya sai Allah wlh,ace kuna zaune karkashin mutum kuna cin albarkacinsa kuna rayuwa da dukiyarsa amma kun tsanesa kuna cin dunduniyarsa,kai Allah shi kyauta" Nawaz ya amsa da amin yana fadin
"Ba ri na shirya nazo na kaiku nima na samu nayi aikin dake gabana a hospital din"
"To a fito lafiya" cewar Mom.
Mintuna sha biyar ya daukesa ya gama shirinsa ya shiga ya yiwa su Mom magana suka fito suka nufi asibiti,ko da sukaje kwatanta musu room din ya yi shi bai shiga ba ya tafi dan akwai cs din da zai yi, su Mom ne suka shiga suka zauna da ita,Sultana tasa hannu ta kwashe mata gashin fuskarta ta ce
"Woww! Allahu Akbar! Ma sha Allah!"
"Menene Sultana?"
"Wlh Mom kyakkyawa da ita, ki ga gashi, wayyo Allah na ni,wlh Mom kamar ba yar nigeria ba" Mom tayi murmushi ta ce
"Baki rabuwa da shiririta Sultana ba bafulatana ba ce"
"Ai wlh Mom ko a fulanin ba kowa ke da kyau ba"
"To anji ki rufe min baki, karki cika marar lafiya da surutu Yayanki ya shigo ya sameki kina zuba zaneki zaiyi kema kin sani" zare ido ta yi tana riƙe bakinta dan tasan sarai zai zanetan sai dai idan bata cika masa ciki ba dan akwai sa da saurin zuciya abu kaɗan ke tunzura shi ransa ya b'aci.
Su na zaune a asibitin sai wajan uku da rabi kafin Aziza ta fara farkawa, farkawartata yazo mata da mugun mafarki Azima ta biyo Baffa da wani zabgegen takwabi tana shirin kashe Baffa bayan sun gama dambatuwa In da Baffa karfinsa ya ƙare ya hau kwalawa Aziza kira ta kawo masa dauki Banju zai kashesa! Ga Hajja a sume a kasa, wani ihu Aziza ta yi dai-dai da lokacin da Nawaz ya sako kafarsa dakin ya zo dubasu ya iske ihunta tana fadin
"BAFFAAAANAAAAA!!! HAJJAAAAA!! KEEEEE!!! AZIMAAAAAA!! KARKI KASHE BAFFAAAA!!" sauri yin kanta suka yi Nawaz ya tallabota kirjinsa ya kalli Sultana yace "maza je ki kirawo min wasu nurses ko Dr duk wanda kika samu su zo yanzu" da gudu Sultana ta fice suka dawo da nurse mutum hudu, nan yace su ba shi allurai, bayan sun miƙa masa ne tana ta faman buge-buge, Mom tana tsaye daga saman kanta tana mata tofi, yana mata alluran ta koma ta yi lamo a kirjinsa tana kan ambatar sunan Baffanta da Hajjanta, kamar da minti biyar abun ya lafa,Mom ta ce
"Nawaz ya dai?"
"Ba komai Mom,nan da 30mins zata farka zata dawo dai-dai In sha Allah" Mom ta ce
"Ka gani ko Nawaz? Gwara da Allah yasa baka barta ba ka taho da ita, Allah ya bata lafiya ya tashi kafaɗunta" ya amsa da amin yana me leƙa fuskarta ya ga gashi ya rufe,kwantar da ita ya yi ya fice, Sultana ta zauna kusa da ita tana kamo hannunta.
Kamar yadda Nawaz ya fada haka kuwa ya kasance 30mins ta farka, tana buɗe ido ta hau bin inda take da kallo, ba dai har ta mutu bane yanzu haka tana lahira? Take tambayar kanta,kallon hannunta ta yi ta ga wata budurwa zaune kusa da ita, ga wata dattijuwar mata zaune hannunta dauke da carbi tana lazimi, budurwar kuma hannunta da waya tana dannawa,saurin janye hannunta Aziza ta yi ta matsa baya, tana dafe kanta da kafarta da ta ga an daure mata shi,nan abunda ya faru ya dawo mata kai, Sultana ta ce
"Sannu kinji! Ya jikin naki?"
"Sultana kira yayanki mana" cewar Mom
"To Mom" Sultana ta faɗa tana ficewa.
Tare suka dawo da shi, a lokacin Aziza na maqale can jikin gado tana wani irin kuka kanta a sunkuye tayi mayafi da gashin kanta, jin magana yasata dagowa kaɗan ganin mutum na matsota ya sakata fashewa da sabon kuka tana fadin
"Aradu karka matso kusa dani" a yadda take magana zaka san babu hausa a harshenta,banza da ita Nawaz ya yi yasa hannu zai tabata ta saki ihu tana kiran sunan Baffa, haushi ne ya kama Nawaz ya daka mata tsawa
"Keeeee!!! Bana son hauka!! Ki natsu!!" Mom tace
"Haba Nawaz!? Miye haka? Ka mata a hankali mana" wani tsoro ne ya kama Aziza,ganin haka yasa Mom matsowa kusa da ita ta ce
"Ɗana ne! Ba zai cutar dake ba, wancan kanwarsa ce, shi kuma likita ne, ya bugeki ne bisa tsautsayi sannan wannan asibitinsa ne yana kula dake,alhamdulillah kin farka, yanzu haka kina garin kaduna ne,munji kina ambatar sunan Baffanki, da kinji sauki zamu maidaki gida kinji ko? Karkiji tsoronsa zai duba ki ne uhum?" Mom ta faɗa tana bubbuga Aziza, dubata Nawaz ya yi ya fice cikin haushi.
🐍🐍🐍🐍🐍
Tun shigan Azima dakin munir da niyyar gyarawa ba a sake ganin mai kama da ita ba, har dare, kuma cikin wani ikon Allah babu wanda ya nemeta,dan sun manta da ita,tunda sun san mai aikinsu ta gudu sun manta sun dauki sabuwa, sai wajan karfe tara Munir ya dawo shi da Baby, bayan sun yi magana da Zuby da Hajiya Baby ta wuce dakinta,Munir ma ya wuce nasa,yana shiga ya yi turuss yana ganin ikon Rabba, Azima ta yi ɗaya-ɗaya a kan gado ta bararraje an samu gado mai laushi bana kara ba, sai kwasar baccinta take cikin salama hankali kwance, gashinta da ya sha wanki sai kyalli yake yi duk ya baje ya rufe mata fuska, wani yawu muqut Munir ya hadiye yana fadin
"Kai daga ina wannan balarabiyan?" ya fada yana yin kanta ba tare da yayi dogon tunani ba shin aljana ce ko mutum.
🍃🍃🍃🍃🍃
MOMYN AHLAN✍🏻
[4/13, 10:12 AM] Mom Ahlan: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)
MALLAKAR.
*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*
SAHIBAR KAINUWA.
Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.
Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_
_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_
🍃🍃🍃🍃🍃
*PAID.*
🅿️==3️⃣9️⃣↪️4️⃣0️⃣
Hannu yasa jikinsa na rawa yana lashe baki yana kwashe gashin da ya rufe mata fuska cikin bacci Azima ta ji mutum a kanta, bata gama tabbatarwa ba sai da taji saitin hannun mutum a wajan dukiyar fulaninta, nan da nan ta farga da abunda ke wakana a kanta, idonta ne ya sauya, da tafin hannunta ta tokari kirjin Munir kamar kiftawar ido da bismillah sai ga Munir ya yi sama ya bugu timm da kasa!! Saurin tashi Azima ta yi,ta dauki mayafinta ta yi lullubi sannan ta yi kan Munir,tana zuwa ta shaƙosa da hannu daya ta haɗasa da bango,nan idon Munir ya yi waje yana so ya yi ihu amma baya so kannansa suji su rainasa, lallai yau ba shakka ya yi gamo da aljana a garin ɗan banzan son matan tsiya tun bai tsaya ya ga wacece ba ya afka mata ga shi tana neman kashesa, lokuta da yawa Munir ya sha yiwa yaran aikinsu fyaɗe,da anyi kara kuwa uwarsu zata zuba kuɗi ta karbo ɗanta tace an masa sharri.