← Book details Ameenatou Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 57 OF 59

Sashe 57

Ameenatou Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Fitowan su Jamaal yayi daidai da fitowan Dad Omar tareda Ahmed zasu shiga mota Dan haka Kai tsaye ya kofar harabar Daya hada gidajen suna nufa suka Isa gurinsa idanuwansa na kansu Yana kallansu a tare zuciyarsa na cika da farin ganin auren yarsa Dan haka Kai tsaye rungume Jamaal yayi kafin ya rungume Haroon da yau Shima yake cikawa kowa idanuwa da kwarjini Mai sanyi.

Cikin kulawa da kauna Dad Omar ya kallo Haroon yace su shiga motarsa suje daurin auren tare.

Cikin farin cikin Hakan Haroon ya juyo ya kallo Jamaal zaice da Dan uwansa yake son zuwa daurin aurensa sai Jamaal din Wanda ya kasa samun nutsuwa ya girgiza masa Kai Yana kallan fuskansa Yace yabi Dad din kawai.

Murmushi me sanyi Haroon yayi tareda gyada Kai kaman qaramin yaro yabi dad da Ahmed dukkaninsu suna murmushi suka shige mota.

Jamaal na kallo suka tada motar suka bar harabar gidan Shima ya juya yabar harabar gidan.

Dayake sun Dade da fita kafin ya fita Kai tsaye biyawa sukai suka dauki Babbah sbd Shi Daman da Omar zasu tafi daurin auren sai gashi Kuma sunzo da Haroon sai Hakan yayiwa Babbah dadi sbd zaiso ya sake bawa Haroon amanar Ameenatou
Babbah na shiga suka tada motar suka bar gurin.

Jamaal na kama hanyar zuwa gurin daurin auren siddeeq ya kirasa kaman bazai daukaba Saiya Isa sai kuma ya dauka
Abinda siddeeq din ke sanar masa yaji Yanzu daga bakin Lameenu da BB a Mansion shine ya sakashi juya kan motarsa ya kama hanyar gidansu Ameenatou sbd bazai taba barin wani abu ya samu matar Haroon ba aranar aurensu kaman yanda Shima ranar auren ya rasa tasa matar.

Wayar Dad Omar yake kira cikin gaggawa Amma Sam Bata shiga,
Ta Ahmed ya koma kira kwata kwata Bata shiga itama,
Ta Haroon ya kira ita Kuma Saiya jita a cikin motar dayake din Dan haka yayi wurgi da wayar seat din gefensa tareda qarawa motar tsananin gudu yana nufar gidan.

Yana Isa kofar gidan Hafiz da Abdul sun fito kenan cikin Shirin wucewa ko kashe motar baiyiba ya fito da sauri Yana kallan Abdul yace

"Yi sauri karbi bayansu Dad da Babbah ka sanar musu kada su bi ta Aneyam nzki road,
Ka tabbatarda Basu bi hanyar ba yi sauri, yi sauri...

Abdul na Jin Hakan da Kuma ganin yanda Jamaal din yake a zafafe ya sakashi fadawa motar Hafiz ma ya fada suka bi bayan su Haroon din da mugun gudun gaske.

Shikuwa Kai tsaye harabar gidan ya shiga daidai fitowan Ameenatou din zata bawa Hafiz agogonsa Daya manta gurin sauri cikin mahaukacin navy blue tsadaddiyar lace din Daya fidda kayanta da kuruciyarta akansa idanuwanta akansa suka sauka ta tsaya cak daga inda take tana masa kallan Daya Sakasa qin kallan fuskanta bare gane kamanninta.

Takowa tafara yi ahankali tana nufosa cikin sanyin da duka jikinta kawai taji yayi hakama kirjinta nauyi yayi mata take me tsananin.

Gap take da isowa gurinsa wayar hannunta tayi ringing daidai Nan tasa wayar Shima tayi ringing itace ta fara daukan tata tareda kaiwa kunnenta tareda tsayawa cak daga inda take.

Daga nasa Kiran yayi da siddeeq yayi masa sedai baima gama Jin Abinda yafara fada masa ba Ameenatou ta Yanke jiki ta zube a jikinsa kaman matacciya Shima Neman zubewan yakeyi siddeeq daya iso bakin gate din gidan a haukace sbd mummunan tashin hankalin da baa Saka masa Rana ba ya shigo da mugun gudu.ya taresu gaba dayansu.
##MAMUH#*_AMEENATOUH_*
_Mamuhgee_
#Arewabook@Mamuhgee
#ZafadaBiyar

56
A jikin Jamaal gaba Dayanta Ameenatou din ta zube Dan haka baida zabin Daya wuce riqeta da hannuwansa Shima nasa kafafun na gagararsa daukansa.

Siddeeq da idanuwansa ke rikice da wani mugun ja riqesa Shima yayi Yana Kasa kallan fuskarsa data fara gaba Daya.

Umman fadila ce tareda anti zulaihat cikin mutanen dadah da suka taho daga Nasarawa biki ne suka fito daukan kaya a harabar gidan suka tarar da wanna tashin hankalin da sauri siddeeq yace umman tazo ta dauke Ameenatou daga jikin Jamaal din.

Da sauri suka qaraso tare umman ta tattaro Ameenatou din daga jikinsa tana tambayar lafiya a rude Tana raba idanuwa a tsakanin Ameenatou din da Jamaal da Kuma siddeeq din.

Siddeeq Bai iya cewa komai bayan cewan suyi ciki da Ameenatou din shikuma ya kama Jamaal Wanda har lokacin kaman jiri yake Gani suka fito daga harabar gidan Kai tsaye motar da Jamaal din yazo da ita suka nufa shi siddeeq din yabar wadda yazo da ita a gurin.

Saida ya zaunar da Jamaal din a mota kafin ya zagaya da sauri ya shiga motar zai tayar Jamaal ya dago jajayen idanuwansa ya kallesa daqyar ya iya Bude Baki yace

"Bani key ni zanje na dubo Kai ka Jira anan din Sbd A,dole Ina buqatan barin wani anan din incase.

Siddeeq kallansa yayi da nasa jajayen idanuwan Shima Yana girgiza Kai sbd bazai iya barinsa yayi tuqi ba a lokacin da kansa.

Bude motar Jamaal yayi tareda fitowa ya zagayo ko gabansa Baya Gani dakyau wani irin wuta da radadin azabar nauyi yake ji a kirjinsa Babu abinda yakeso kaman ganinsa gurin da ake maganar.

Karban key din yayi Bai tsaya komaiba ya fada motar Yana rufewa ya tayar Kai tsaye yayi mata wani irin mugun ja yabar gurin siddeeq na bin bayan motar da kallo hankalinsa na mummunan sake tashi sbd kaman zata tashi sama tsaban mugun gudun da Jamaal din keyi.

Jamaal na barin gurin yayi cikin harabar gidan Yana fiddo wayarsa aljihu Yana rasa a cikin wainda suka tafin waye zai kira tinda Babu me lafiyan dauka Kila.

Jamaal kuwa tuqin yakeyi idanuwansa na Neman rufewa Amma karfin hali Dana zuciyarsa Basu bar hakanba Saida ya hau titin da zai Kaisa Aneyam nzki road Wanda yake kaman bypass Babu mutune sosai.

Yana Jin Nisa sosai a kan titin
Tin daga nesa yafara hango mutane da Jamaan tsaro sun rufe titin hakama hadda masu daukan hotuna da wata katuwar mota a gurin datake kokarin kamawa da wuta anata ihu da hayaniya.

Tin anan Kunnuwansa sukai masa wani irin dim suna kokarin dauke jinsu,
Idanuwansa kuwa wani dishi dishi suke son fara masa Amma ya rintse su da karfi tareda budewa Yana budewa motarsa da sauri ya fito batareda ya kasheta ba hakama wani parking din tsakiyar Titi yayi Yana qarasowa gurin da gudun gaske ganin motar Dad Omar data Abdul sun hade guri Daya kaman kayan wankin da aka hada aka matse cikin mafi muni da tashin hankalin kallo a kusan karkashin babbar motar wadda da alama itace tayi musu hawan tela.

Daukewa ganinsa yafara yi da gaske hakama kunnuwansa Dan haka take yafara Neman kasa karasawa sbd jiri da rashin Gani,
Daidai lokacin Mam ya iso gurin da drivernsa tareda Lameenu cikin matsanancin tashin hankalin da Bai taba Shiga ba Shima nasa ganin da Jin kusan daukewa yayi can sama sama yakejin maganganun mutane da iska suna kadawa hakama gabansa Baya Gani sosai Yana Sako Kai inda police din gurin janye masa shida Jamaal daidai lokacinda aka shimfide gawar Haroon da aka samu cirowa a gabansu cikin fararen kayansa da suka sauya take Babu ko dogon haskensu koina jininsa ne ya sauya kalar kayan gabaki dayanta.

Daga Jamaal har Dad lokaci Daya kafafuwansu suka sare a gaban gaban gawar suna zubewa Jamaal take ya qarasa zubewa qasa Yana rarrafowa gaban Haroon din Dan cetan ransa sbd Bai yadda da wani abin ya Riga ya faru ba da Haroon dinsa, Dad kuwa zubawa gawar idanuwansa yayi hannuwansa na wata irin rawar tashin hankali bakinsa na rawa yace

"Kuyi sauri ku kawo mota muje asibiti Dan uwansa likita ne kwararre gashinan zai taimaka masa kuyi sauri,
A kawo mota,
Me kuke Jira?
A kawo mota da sauri 'dana Yana buqatan taimakon gaggawa,
Yaro na Yana buqatan Isa asibiti,
Lameenuuuu a yi gaggawan kawo mota Dan Allah karku bari yarona ya mutu a Haka yanada raunin zuciyaa, HAROON,HAROON,
HAROON my boy,
Yarona 'dan Albarka Karka tafi ka barni Kai kadai nake dashi a cikin abinda nake tsananin so a duniyar Nan,
Haroon,Haroon...... innalillahi wainna ilaihirrajiun....

Dukkanin maganganun da Dad din keyi Baya hayyacinsa sbd Bai yadda da Babu Rai a jikin Haroon ba sbd jamaal ma kwata kwata ya kasa yadda da Babu Rai a jikin Dan uwansa Dan haka yaketa kokarin dawo da numfashi a jikinsa ya hanyar dubarunsu na likitoci hannuwansa na wani irin tsananin rawa hakama nasa fararen kayan tini sukai kaca kaca da jinin Yana rungumo Haroon din idanuwansa na qanqancewa Yana ihun su kawo ambulance Shima.

Lameenu rudewa yayi Shima yafara cewa a kawo ambulance Maza Maza daga SEELAHs hospital Yana Jin tsananin tashin hankali da tausayin halin da yaga Mam a ciki yau harma da tsoro da fargaba duk ya shiga sbd dukkaninsu Basu taba kawo tinanin Haroon zai shiga motar Omar ba,to mema ya shigar dashi,

Babban tsoro da tashin hankali da mugun firgicin dayake ciki shine bayan wucewansu Omar din tareda Haroon Saida ya Jira Jamaal ya gama wayoyinsa tukuna ya fice kafin ya fidda wayarsa ya kira Lameenu din Kuma daidai wannan lokacin ne siddeeq ya shigo mansion din Bai dauka su Jamaal din sun wuce ba sbd yanata Kiran wayarsa busy yake.

BB ya sanar da Lameenu cewan Haroon fa yabi motar Sir Omar a dakatar da aikin kokuwa a qaddamar dashi yanda aka tsara sbd Haroon na ciki,

Kai tsaye Lameenu Bada umarnin yayi ayi aikin kaman yanda aka tsara sbd Ameenatou bazata taba zama sirikar Mam ba ta yanda zai fisa Iko ko mallakar dukiyar gaba dayanta bayan wuyar da suka shawo akanta Dan haka gwara Bata zama sirikar tasaba tin farko suna gamawa da Omar itama su gama da ita shikenan sune magada tinda sune ake kallan uwa Daya Uba Daya dashi Kuma kada a kuskura duk tsanani bayan aiki a cewa Mam an sani su tsaya akan Basu San Haroon yabi motar ba.

Hakan da siddeeq yaji ne ya sakashi Kiran Jamaal Wanda ya gama wayarsa harya fara Nisa a hanya ya fada masa take shikuma ya sauya hanya yabi zuwa gidansu Ameenatou Dan cimma su Dad din da bawa Ameenatou kariya kafin ya samu a dauro auren a dawo yasan Dan uwansa ya samu mallakar macen zuciyarsa.
Chapter 57 · 0% Book details