Sashe 39
Ameenatou Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jini hancinsa da goshinsa suka fara fitarwa harma da bakinsa Yana wani irin fizga take hankalin Dad din yayi mummunan tashin da baitaba tinanin zaishiga ba ya dawo da sauri Yana Kiran sunan Haroon din da sauri sedai tini ya fice hayyacinsa dukkanin jikinsa na qara jijjiga sosai.
Siddeeq ma cikin matsanancin tashin hankali ya kamo Haroon din Yana janyo pillow na kujera ya Saka masa Akai tareda birkitasa Yana hanasa bubbuga kansa a tiles da jininsa ke fita sosai.
Rasa abinyi Dad yai Yana shiga sabon tashin hankali da mamakin Menene yake faruwa da rayuwar Haroon din,
Badai shi Kuma haukacewa zaiyiba akan mace ba,
Innalillahi wainna ilaihirrajiun"
Meke faruwa da yayansa?
Innalillahi wainna ilaihirrajiun.
Duk yanda Dad yake tsammanin lamarin ya wuce Nan sbd Haroon take ya koma tamkar me cikakkiyar tabin kwakwalwa duk tsananin zafi da bacin ran dayazo dashi jin yayi kansa Shima Yana daukan matsanancin zafi.
Siddeeq drawers ya nufa na gado da gaban mirror Yana yamutsa hankali tashe Yana Neman maganinsa Amma kwata kwata ya kasa Gani.
Cikin daga sauti da kidima Dad yake cewa
"Meyake faruwa dashi ne?
Menene Hakan nake Gani?
Ciwon hauka ya kamasa ne kokuwa?
Menene wannan din???
Duk a jere ciki daga murya da tashin hankali yake jero tambayoyi Yana kamo Haroon din Wanda yake jijjiga har lokacin.
A karkarshi pillow siddeeq ya sami maganin bayan ya haukata dakin cikin tashin hankali da mintinan da Basu Fi biyu ba ya iso da sauri yana Bude maganin ya kamo kan Haroon ya Saka masa
Tsaban rudewa Dad dinne da kansa ya dauko ruwa ya miqawa siddeeq ya basa rabi na shiga bakinsa Rabi na zubewa harya hadiye maganin.
Sakewa jikinsa yayi Dad yayi gaggawan Bada umarnin a fito dashi zuwa asibiti shi kansa siddeeq a daidai wannan lokacin yasan likitocin gaske Haroon yake buqata Dan haka ba Bata lokaci aka kwashi Haroon din sai asibiti.
Suna zuwa aka karbesa sbd duka jikinsa ya Dena rawa ko wani abin sai kawai aka miqasa da cewan faduwa yayi.
Dayake Mam yasan abinda zai iya faruwa na zuwan Yan jarida take ya Bada izinin securities kada su bar yan jarida zuwa ko sanin komai.
Har yamma sosai suna asibitin Haroon Bai farfado ba,
Dad magana yayi da siddeeq sosai yaji komai gameda ciwon Haroon da lokacinda ya fara take ya fahimci ba karamar illa maganinsu keyi masa ba Ashe Dan haka take ya sake shiga tashin hankali da damuwan kada Yan jarida ko kadan Susan dansa Barr Haroon seelah na fama da tabin kwakwalwa.
A Daren suka koma Abuja dashi sbd hankalin Dad Bai kwanta ba anan din.
Su Babbah da suka samu labarin anbar Nasarawan da Haroon hankalinsu tashi yayi Dan kuwa ciwonsa kenan yayi tsananin gaske haka suka ringa Kila mintina bayan mintina Dan Jin lafiyansa.
A cikin kwana da wunin Dad yayi sakawa da warwaran datafi dari da hamshin hakama Dad Lameenu ma hakanan ya lallabo ya taho sbd yasan Mam din na cikin damuwa da matsanancin hali Dan haka ya taho su fuskanci lamarin tare duk da Shima ya kasa warware sbd Bai dawo daidaiba idan ba Jin yayi sun samu mafitan warwara ba.
A cikin kwana da wuni Dad ya tabbatarda irin tsananin so da kwallafa Rai da Haroon yayi akan AMEENATOU sunan Daya riqe Kai tsaye sbd Tinanin dasuketa yawo akansa.
A karon farko da zai sauya raayinsa zuwa wani raayin Dan cimma burinsa cikin sauri da samun mafita biyu,tasa data rasa 'dansa.
Shi kansa Dad Lameenu yashiga firgicin tarihin dayake Neman maimaita kansa,
Idan sun rasa Jamaal sun tabarbare haka to Haroon dinma dasuke ganin baida amfani suna rasasa karasa tabarbarewa zasuyi komai yazo karshe shikenan.
Farfadowan Haroon Saida ya bawa dukkaninsu tausayi sbd yanajin jikin sosai Dan wanna Karan maganin ya Riga yayi masa illa sosai da Babu wani abinda zaa iya yi sai ikon Allah.
Su Dad kasa barin kowa yaji zancen sukai sbd a nasu tinanin maganinsu ne yayi masa wannan mummunan illar.
Duk tsananin halin dayake ciki kallan Dad dinsa yayi har lokacin yanajin raunin batawa su Dad din Rai dayayi da asarar da shi kansa baisan ta inda zai fara gyara ba.
Rokonsa gafara da sake basa Dama shine abi farko Daya furta Yana rintse idanuwansa.
numfashi Dad din ya sauke tareda Gyara zamansa Yana kallansa cikin nutsuwa yace
"Zan sake baka Daman karshen Amma ba iya akan aikin kadai ba,
Zan nema Maka auren Ameenatou Amma sai idan ka cika alkawarinka ka gyara mummunan Barna da Tsaka me wuyan daka Saka SEELAHs gaba Dayanta aciki idan ba Hakan ba ka manta da maganar aurenta Dan kuwa har abada bazaka auretaba idan ba Hakan ne ya faru ba"
Rintse idanuwansa yayi hawayen ciki masu dumi suna gangarowa ya gyada kansa cikin wani irin sanyin jikin da mutuwar jikin batareda ya iya cewa komaiba sai tsananin tsoro da shakkan Dayake mamayesa.
Dad Lameenu da Baice komaiba gyara zama yayi Yana kallan Haroon din cikin nutsuwa Shima ya Bude Baki yace
"Haroon nayi Maka alkawarin bazamu bar garin Nan ba ayau sai munje munyi gaisuwar iyaye da iyayenta sbd Neman Maka aurenta idan har zaka nutsuwa ka fuskanci nauyin dayake kanka sbd Kaine kaidai zaka iya gyara wannan Barnar data riskemu sbd kafi kowa sanin halinda muke Neman fadawa idan bamu farfado ba.
Tinda suke magana idanuwansa a rufe suka Hawaye masu zafi na gangarowa a acikinsu Saida Dad Lameenu yayi masa alkawarin nema masa auren ya Bude idanuwan ahankali ya kallesa Yana sauke Kai kasa.
Dad dinsa ma Jin yayi yayi Naam da Hakan Dan shine maslaharsu ayanzu kada su maimaita kuskuren Baya gwara su nema masa auren su juyasa akan abinda sukeso tinda zai iya komai akanta din.
Duk yanda wani zai samu Daman sanin matsalar ciwon Haroon Saida Dad ya tabbatarda Bata fita ba hatta siddeeq Bai bari likitocin sun bari yasan duk wani abinda aka bincika aka Gano ba har suka sake kwana biyu a garin Akai sallamarsa a ranar suka kwasa zuwa Nasarawa Dan Kai gaisuwan Neman auren.
#MAMUH#*_Arewabooks@Mamuhgee_*
39
****Su babbah da suka samu labarin zuwan da Dad din zasuyi gaisuwa tini aka gyara koina hatta kofar gidansa Saida aka share har kofar gidan makota aka shirya tsaf Dan tarbonsu da Aminansa guda biyu da zasu tayasa karban gaisuwan.
Dayake ranar su Dad din zasu koma da wuri suka iso guraren karfe daya na Rana Dan haka su Babbah suka tarbesu da girmamawa da mutuntawa sosai har cikin fara isowan gidan babban suka zauna a babbar dadduman da aka shimfida musu me kyau.
Dad Lameenu Dayake amsa gaisuwansu cikin girmamawa da kulawa sosai Shima tareda farin ciki me tsananin da tin anan aka fara farin cikin Samun Sirikai irinsu da duk kudi da matsayinsu sunsan mutuncin mutane da iya mu'amalantarsu.
Babbah Dad Lameenu yayi kallan tsaf Mintina Yana tantance kamannin nasa da son tabbatarda idan shine Wanda yake tinanin shi dinne.
Ganin irin kallan da Alh Lameenu kewa Babbah ya sakashi sai farin ciki yake sake shiga Yana sake musu barka da zuwa kafin ya tambaya jikin Haroon cikin kulawa sosai Yana dorawa da cewa sai anjima su Abdul su shiga dubasa Inshallah.
Abinda ya tarasu suka shiga gabatarwa Babu wani Bata lokaci suka gabatar da kansu da Neman auren Ameenatou da suka zo nemawa dansu Haroon Wanda su Babbah sun sanshi kuma sunsan aikinsa da halayensa daidai gwargwado.
Naam su Babbah sukai kafin suka suka sake gabatar da kansu da shi babban amatsayin mahaifin Ameenatou wadda shine ya haifa abarsa da cikinsa Kuma yayi na'am da Hakan ya Kuma bawa Haroon aurenta.
Farin ciki da hamdala suka ringa miqawa ana sake taya juna murna Dad Lameenu ya cire kudin Neman auren Naira dubu dari biyar ya bayar kafin suka sake miqa godiyarsu har lokacin zuciyar lameenu wani tsalle takeyi cikin rudewa da rikicewa Dan kuwa ya sake tabbatarda Babbah ne suka tana Gani asibiti gurin Omar a lokacinda aka taba Kai masa attack idan Bai mantaba Kuma ya sake dubawa ya tabbata Babbah ne ya Gani Wlh.
Abdul da shine babban yayan Ameenatou Kuma dashi Akai zaman Neman auren Alh Lameenu ya kalla cikin kulawa Yana tambayarsa Aikinsa da karatunsa.
Cikin nutsuwa da ladabi Abdul din ya amsa masa matsayin karatunsa da aikin dayake yi.
Take Alh Lameenun ya nuna raayinsa na Taimkawa yace Abdul din ya hada takardunsa zai Aiko a karba a aika masa Lagos.
Godiya Abdul din yayi su Babbah dasu Alh sabi'u makocin Babbah godiya sukai suna sake nuna Jin dadinsu kafin su Dad suka saki jiki sosai sukai fira da maganganu dasu babban anan ma sukai sallah azahar kafin suka Shirin tafiya su Babbah suka rakosu har waje inda motocinsu da securities dinsu suke suka shiga take aka bar gurin dasu.
Suna barin gurin Dad Lameenu zufan dayake hadawa tin acan yana shanye abinsa a jikinsa ya zari tissue ya goge kafin ya Ciro wayarsa.
Hotunan da BB ya turo musu nasu babban ya Nemo hannuwansa na Dan rawa ya Nemo na Babbah ya zuba masa idanuwansa.
Mam da zuciyarsa kwata kwata Bata cikin dadi Baida energy din tambayar abinda yake faruwa sbd bayajin zai taba barin ya hada zuria dasu Babbah
Ya nema auren ne sbd yana buqatan Haroon din sbd ya Jamaal ya dawo garesa Amma Badan Hakan ba bayajin zai tana yadda ya Kai kansa Neman auren.
Lameenu Daya sake goge zufansa miqewa Mam wayar yayi Yana cewa
"Wannan shine fitilar da zata kaimu ga sanin duk inda dangin matar Omar suke sbd samun Magajinsa"
Kallan wayar Mam yayi kansa na tsananin sarawa da nauyi Amma Jin Abinda Lameenu ya fada ya sakashi cire hannunsa daga goshinsa Daya dafe idanuwansa a lumshe.
Kallan Lameenu din yayi bayan ya Kalli Babbah a wayar Yana jiran bayaninsa.
Cikin nutsuwa lameenu ya tinatar dashi ganin da sukaiwa Babbah a asibiti tareda Omar shekarun Baya.
A saninsu wancan lokacin daga kauyensu Omar yace musu babban yake Amma basusan Menene alaqarsa dashi ba Dan haka dole babba yasan waye yayan matar Omar Kuma bazasu rasa sanin komai ta hanyar Saba Daman a bagiren Neman ko mutum Daya daga kauyen suke amma tsawon shekaru ankasa samu.
Siddeeq ma cikin matsanancin tashin hankali ya kamo Haroon din Yana janyo pillow na kujera ya Saka masa Akai tareda birkitasa Yana hanasa bubbuga kansa a tiles da jininsa ke fita sosai.
Rasa abinyi Dad yai Yana shiga sabon tashin hankali da mamakin Menene yake faruwa da rayuwar Haroon din,
Badai shi Kuma haukacewa zaiyiba akan mace ba,
Innalillahi wainna ilaihirrajiun"
Meke faruwa da yayansa?
Innalillahi wainna ilaihirrajiun.
Duk yanda Dad yake tsammanin lamarin ya wuce Nan sbd Haroon take ya koma tamkar me cikakkiyar tabin kwakwalwa duk tsananin zafi da bacin ran dayazo dashi jin yayi kansa Shima Yana daukan matsanancin zafi.
Siddeeq drawers ya nufa na gado da gaban mirror Yana yamutsa hankali tashe Yana Neman maganinsa Amma kwata kwata ya kasa Gani.
Cikin daga sauti da kidima Dad yake cewa
"Meyake faruwa dashi ne?
Menene Hakan nake Gani?
Ciwon hauka ya kamasa ne kokuwa?
Menene wannan din???
Duk a jere ciki daga murya da tashin hankali yake jero tambayoyi Yana kamo Haroon din Wanda yake jijjiga har lokacin.
A karkarshi pillow siddeeq ya sami maganin bayan ya haukata dakin cikin tashin hankali da mintinan da Basu Fi biyu ba ya iso da sauri yana Bude maganin ya kamo kan Haroon ya Saka masa
Tsaban rudewa Dad dinne da kansa ya dauko ruwa ya miqawa siddeeq ya basa rabi na shiga bakinsa Rabi na zubewa harya hadiye maganin.
Sakewa jikinsa yayi Dad yayi gaggawan Bada umarnin a fito dashi zuwa asibiti shi kansa siddeeq a daidai wannan lokacin yasan likitocin gaske Haroon yake buqata Dan haka ba Bata lokaci aka kwashi Haroon din sai asibiti.
Suna zuwa aka karbesa sbd duka jikinsa ya Dena rawa ko wani abin sai kawai aka miqasa da cewan faduwa yayi.
Dayake Mam yasan abinda zai iya faruwa na zuwan Yan jarida take ya Bada izinin securities kada su bar yan jarida zuwa ko sanin komai.
Har yamma sosai suna asibitin Haroon Bai farfado ba,
Dad magana yayi da siddeeq sosai yaji komai gameda ciwon Haroon da lokacinda ya fara take ya fahimci ba karamar illa maganinsu keyi masa ba Ashe Dan haka take ya sake shiga tashin hankali da damuwan kada Yan jarida ko kadan Susan dansa Barr Haroon seelah na fama da tabin kwakwalwa.
A Daren suka koma Abuja dashi sbd hankalin Dad Bai kwanta ba anan din.
Su Babbah da suka samu labarin anbar Nasarawan da Haroon hankalinsu tashi yayi Dan kuwa ciwonsa kenan yayi tsananin gaske haka suka ringa Kila mintina bayan mintina Dan Jin lafiyansa.
A cikin kwana da wunin Dad yayi sakawa da warwaran datafi dari da hamshin hakama Dad Lameenu ma hakanan ya lallabo ya taho sbd yasan Mam din na cikin damuwa da matsanancin hali Dan haka ya taho su fuskanci lamarin tare duk da Shima ya kasa warware sbd Bai dawo daidaiba idan ba Jin yayi sun samu mafitan warwara ba.
A cikin kwana da wuni Dad ya tabbatarda irin tsananin so da kwallafa Rai da Haroon yayi akan AMEENATOU sunan Daya riqe Kai tsaye sbd Tinanin dasuketa yawo akansa.
A karon farko da zai sauya raayinsa zuwa wani raayin Dan cimma burinsa cikin sauri da samun mafita biyu,tasa data rasa 'dansa.
Shi kansa Dad Lameenu yashiga firgicin tarihin dayake Neman maimaita kansa,
Idan sun rasa Jamaal sun tabarbare haka to Haroon dinma dasuke ganin baida amfani suna rasasa karasa tabarbarewa zasuyi komai yazo karshe shikenan.
Farfadowan Haroon Saida ya bawa dukkaninsu tausayi sbd yanajin jikin sosai Dan wanna Karan maganin ya Riga yayi masa illa sosai da Babu wani abinda zaa iya yi sai ikon Allah.
Su Dad kasa barin kowa yaji zancen sukai sbd a nasu tinanin maganinsu ne yayi masa wannan mummunan illar.
Duk tsananin halin dayake ciki kallan Dad dinsa yayi har lokacin yanajin raunin batawa su Dad din Rai dayayi da asarar da shi kansa baisan ta inda zai fara gyara ba.
Rokonsa gafara da sake basa Dama shine abi farko Daya furta Yana rintse idanuwansa.
numfashi Dad din ya sauke tareda Gyara zamansa Yana kallansa cikin nutsuwa yace
"Zan sake baka Daman karshen Amma ba iya akan aikin kadai ba,
Zan nema Maka auren Ameenatou Amma sai idan ka cika alkawarinka ka gyara mummunan Barna da Tsaka me wuyan daka Saka SEELAHs gaba Dayanta aciki idan ba Hakan ba ka manta da maganar aurenta Dan kuwa har abada bazaka auretaba idan ba Hakan ne ya faru ba"
Rintse idanuwansa yayi hawayen ciki masu dumi suna gangarowa ya gyada kansa cikin wani irin sanyin jikin da mutuwar jikin batareda ya iya cewa komaiba sai tsananin tsoro da shakkan Dayake mamayesa.
Dad Lameenu da Baice komaiba gyara zama yayi Yana kallan Haroon din cikin nutsuwa Shima ya Bude Baki yace
"Haroon nayi Maka alkawarin bazamu bar garin Nan ba ayau sai munje munyi gaisuwar iyaye da iyayenta sbd Neman Maka aurenta idan har zaka nutsuwa ka fuskanci nauyin dayake kanka sbd Kaine kaidai zaka iya gyara wannan Barnar data riskemu sbd kafi kowa sanin halinda muke Neman fadawa idan bamu farfado ba.
Tinda suke magana idanuwansa a rufe suka Hawaye masu zafi na gangarowa a acikinsu Saida Dad Lameenu yayi masa alkawarin nema masa auren ya Bude idanuwan ahankali ya kallesa Yana sauke Kai kasa.
Dad dinsa ma Jin yayi yayi Naam da Hakan Dan shine maslaharsu ayanzu kada su maimaita kuskuren Baya gwara su nema masa auren su juyasa akan abinda sukeso tinda zai iya komai akanta din.
Duk yanda wani zai samu Daman sanin matsalar ciwon Haroon Saida Dad ya tabbatarda Bata fita ba hatta siddeeq Bai bari likitocin sun bari yasan duk wani abinda aka bincika aka Gano ba har suka sake kwana biyu a garin Akai sallamarsa a ranar suka kwasa zuwa Nasarawa Dan Kai gaisuwan Neman auren.
#MAMUH#*_Arewabooks@Mamuhgee_*
39
****Su babbah da suka samu labarin zuwan da Dad din zasuyi gaisuwa tini aka gyara koina hatta kofar gidansa Saida aka share har kofar gidan makota aka shirya tsaf Dan tarbonsu da Aminansa guda biyu da zasu tayasa karban gaisuwan.
Dayake ranar su Dad din zasu koma da wuri suka iso guraren karfe daya na Rana Dan haka su Babbah suka tarbesu da girmamawa da mutuntawa sosai har cikin fara isowan gidan babban suka zauna a babbar dadduman da aka shimfida musu me kyau.
Dad Lameenu Dayake amsa gaisuwansu cikin girmamawa da kulawa sosai Shima tareda farin ciki me tsananin da tin anan aka fara farin cikin Samun Sirikai irinsu da duk kudi da matsayinsu sunsan mutuncin mutane da iya mu'amalantarsu.
Babbah Dad Lameenu yayi kallan tsaf Mintina Yana tantance kamannin nasa da son tabbatarda idan shine Wanda yake tinanin shi dinne.
Ganin irin kallan da Alh Lameenu kewa Babbah ya sakashi sai farin ciki yake sake shiga Yana sake musu barka da zuwa kafin ya tambaya jikin Haroon cikin kulawa sosai Yana dorawa da cewa sai anjima su Abdul su shiga dubasa Inshallah.
Abinda ya tarasu suka shiga gabatarwa Babu wani Bata lokaci suka gabatar da kansu da Neman auren Ameenatou da suka zo nemawa dansu Haroon Wanda su Babbah sun sanshi kuma sunsan aikinsa da halayensa daidai gwargwado.
Naam su Babbah sukai kafin suka suka sake gabatar da kansu da shi babban amatsayin mahaifin Ameenatou wadda shine ya haifa abarsa da cikinsa Kuma yayi na'am da Hakan ya Kuma bawa Haroon aurenta.
Farin ciki da hamdala suka ringa miqawa ana sake taya juna murna Dad Lameenu ya cire kudin Neman auren Naira dubu dari biyar ya bayar kafin suka sake miqa godiyarsu har lokacin zuciyar lameenu wani tsalle takeyi cikin rudewa da rikicewa Dan kuwa ya sake tabbatarda Babbah ne suka tana Gani asibiti gurin Omar a lokacinda aka taba Kai masa attack idan Bai mantaba Kuma ya sake dubawa ya tabbata Babbah ne ya Gani Wlh.
Abdul da shine babban yayan Ameenatou Kuma dashi Akai zaman Neman auren Alh Lameenu ya kalla cikin kulawa Yana tambayarsa Aikinsa da karatunsa.
Cikin nutsuwa da ladabi Abdul din ya amsa masa matsayin karatunsa da aikin dayake yi.
Take Alh Lameenun ya nuna raayinsa na Taimkawa yace Abdul din ya hada takardunsa zai Aiko a karba a aika masa Lagos.
Godiya Abdul din yayi su Babbah dasu Alh sabi'u makocin Babbah godiya sukai suna sake nuna Jin dadinsu kafin su Dad suka saki jiki sosai sukai fira da maganganu dasu babban anan ma sukai sallah azahar kafin suka Shirin tafiya su Babbah suka rakosu har waje inda motocinsu da securities dinsu suke suka shiga take aka bar gurin dasu.
Suna barin gurin Dad Lameenu zufan dayake hadawa tin acan yana shanye abinsa a jikinsa ya zari tissue ya goge kafin ya Ciro wayarsa.
Hotunan da BB ya turo musu nasu babban ya Nemo hannuwansa na Dan rawa ya Nemo na Babbah ya zuba masa idanuwansa.
Mam da zuciyarsa kwata kwata Bata cikin dadi Baida energy din tambayar abinda yake faruwa sbd bayajin zai taba barin ya hada zuria dasu Babbah
Ya nema auren ne sbd yana buqatan Haroon din sbd ya Jamaal ya dawo garesa Amma Badan Hakan ba bayajin zai tana yadda ya Kai kansa Neman auren.
Lameenu Daya sake goge zufansa miqewa Mam wayar yayi Yana cewa
"Wannan shine fitilar da zata kaimu ga sanin duk inda dangin matar Omar suke sbd samun Magajinsa"
Kallan wayar Mam yayi kansa na tsananin sarawa da nauyi Amma Jin Abinda Lameenu ya fada ya sakashi cire hannunsa daga goshinsa Daya dafe idanuwansa a lumshe.
Kallan Lameenu din yayi bayan ya Kalli Babbah a wayar Yana jiran bayaninsa.
Cikin nutsuwa lameenu ya tinatar dashi ganin da sukaiwa Babbah a asibiti tareda Omar shekarun Baya.
A saninsu wancan lokacin daga kauyensu Omar yace musu babban yake Amma basusan Menene alaqarsa dashi ba Dan haka dole babba yasan waye yayan matar Omar Kuma bazasu rasa sanin komai ta hanyar Saba Daman a bagiren Neman ko mutum Daya daga kauyen suke amma tsawon shekaru ankasa samu.