Sashe 18
Zumuntar Kenan Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read
THE ISSUE OF MOMIN ABU
Sha'ani na da Momin ABU kamar yadda Fa'izah bata fahimce shi ba ko ince bata sani ba. Babu kuma wanda ya taba tararta ya gaya mata, Momin ABU bata daga cikin Zuri'ar Abubakar Bamalli.
Kamar yadda ya faru tun muna kanana, an tura Baban ABU bautar kasa Jihar Taraba, kamar yadda Baban Kaduna yake bamu labari, yana (service) din ne a gidan marayu na Jihar Taraba (Taraba State Orphanage Home).
Maimunatu marainiya ce, da ta tashi ba uwa ba uba, ba dangi a gidan marayu. Kamar yadda Baban ABU ya baiwa su Baban Kaduna labari, ni kuma a lokacin bani da wayo da nayi wayo ne naji labarin a bakin Hajjah.
An tura Ahmadu A.B bautar kasa Jihar Taraba, acan yaga Maimunatu, inda yake (serving) wato Taraba State Orphanage Home. Tana daga cikin 'yan mata goma a gidan marayun da suka kai minzalin aure, sannan mafi nutsuwa da kamalar cikinsu.
Ya je ne a matsayin malamin (secondary school) dinsu, yana koyar dasu kimiyyar noma, wato (Agricultural Science).
Maimunatu hazikar yarinya ce wadda Allah Ya yiwa baiwar kwakwalwar fahimtar karatu.
Kamar yadda yake a cikin (psychological nature) na kowanne malamin makaranta. Wato kaunar hazikin dalibi da girmama shi hakan ce ta faru tsakanin Baban ABU da Momin ABU har kuma ya rikide zuwa soyayya mai tsafta da inganci. Wadda tausayi da kauna, shi ne tubali da ginshikinta.
Kamar yadda Hajjah ke bamu labari, ta ko'ina Ahmadu A.B ya hanga ya tauna baiga ta inda marigayi mahaifinsa A.B zai amince masa auren Maimuna ba.
Bar ta auren zumuncin gidansu da suka maida shi farillah, kuma shika-shikan rayuwarsu, rashin ASALI wani babban abu ne domin kashi tamanin cikin dari na yaran dake gidan marayu har abada ba'a sanin asalinsu ko ganin wani nasu. A haka suke zuwa duniya su koma, cikin kiyayewar Ubangiji.
Wannan yasa Ahmadu A.B cikin tsaka mai wuya da tunanin abin yi. Na farko ba zai iya barin Maimunatu ba, maganar ma ace ya hakura da ita bata taso ba, domin ba karamin sonta yake ba, kuma shakuwar dake tsakanin su ta wuce tunanin kowa.
Sai ya yi tunanin wadda yake ganin zata fisshe shi saboda KURUCIYA irin wadda ta faru dani akan Fa'izah!
Ahmadu yaje kotun Musulunci an daura musu aure da Maimuna ta yin amfani da malaman shi na Jami'ar Ahmad Bello. Ya dauko Maimunatu ta kawowa Hajjah, a lokacin da cikin Fa'izah wata bakwai.
Mafari kenan dana tashi cikin nunawa Momin Fa'izah wariya da kabilanci a tsakanin su Mama, Aunty Hauwa da tsararrakinta. Shi din ma na fatar baki ne, ko kallon banza ban taba yi mata ba, sannan a bayan idonta musamman idan Fa'izah ta bani haushi.
Hali ne na zuri'armu baki daya (kabilanci) da 'ethnocentrism' duk wanda ba daga zuri'ar A.B ya fito ba, to fa ba cikakken mutum bane.
Da Hajjah da marigayi suka ji kowacece Maimunatu hankalinsu ya tashi kwarai, sunyi fushi da Baban ABU fushi mai tsanani, sannan 'punishment' dinsa shi ne 'suspension' daga duk wani abu da ya shafi zuri'ar A.B zuwa wani lokaci da basu kayyade ba. Duk Ahmadu ya ce yaji ya gani, indai zasu barshi ya cigaba da rayuwa da ita.
A lokacin hatta zuwa daurin auren cikin gida an dakatar dashi, haka itama, zuwa wani sha'ani na mata kamar biki ko suna duk ba’a bukatar su.
Zance ko da Baban ABU ya damu to kadan ne tunda gogaggen dan boko ne wadanda (time matters a lot for them) wato lokaci abu ne mai matukar muhimmanci a garesu. Sai ya yi amfani da lokacin 'suspension' din nasu ya koma makaranta ya nemi (degree) na biyu. Ita kuma ya sanyaata a (school of Nursing and Midwifery).
Ba da bata lokaci ba yana kammalawa A.B.U suka dauke shi 'lecturing' ya kuma samu gida a cikin makaranta, domin ada a gidan haya suke domin gidansa na A.B Quaters an hana shi mukullin an rufe. A lokacin tuni an haifi fa’izah har tayi wayo.
Kafin A.B ya rasu ya yafewa dansa Ahmadu, ya kuma karbi Maimunatu a matsayin surukar kaddara, bayan haihuwar danta na biyu, wato Abdallah, saboda kyawawan halayenta da zuri'a da tazo musu da ita mai albarka mai kama da nasu 'ya'yan. Domin Abdallah sak mahaifinsa, Fa'izah kuma Aunty Rabi ta debo, sai dai ta dauko duhun Maimunatu. Dama kuma abinda basa so kenan na auren bare, domin zai haifar da sauyin kamanni a cikinsu. Amma tabbas da Maimunatu na da iyaye, da sun maida ta ga iyayenta ko Ahmadu zai mutu, sun karbeta ne saboda MARAICIN ta.
Nayi nadama, nadama mai yawa akan duk abinda na yiwa Fa'izah! Nadamar da bani da tabbacin akwai ranar da Fa'izah zata karbeta, tunda ba zata taba tsayawa ta saurari kalaman bakina ba. Fatana Allah Ya bani iko da damar nunawa Fa'izah kuskurena da karbarsa kafin na kwanta dama... Ya yaye min wannan ginshiran, domin ni kaina yana wahalar dani...".
Da na kawo nan kuka na rikice da shi sosai, na kasa ci gaba da karatun, na ya da littafin. A guje nayi daki na ina kuka wiwi, na fada tsakiyar gadona na ci gaba da rasgar kuka.
Nayi kuka-nayi kuka har naji babu dadi. Wannan shaukin ke kara mamayar zuciyata yana kara habaka. Wanda da nayi tsai da zuciyata na fahimci abinda bana so in fahimta da gangan. Wato SON FA'IZ ne yake mamayata cikin kowanne dakika na bayan da ya barni. Wani irin so mai cin rai, da tafarfasa zuciya.
Sha'ani na da Momin ABU kamar yadda Fa'izah bata fahimce shi ba ko ince bata sani ba. Babu kuma wanda ya taba tararta ya gaya mata, Momin ABU bata daga cikin Zuri'ar Abubakar Bamalli.
Kamar yadda ya faru tun muna kanana, an tura Baban ABU bautar kasa Jihar Taraba, kamar yadda Baban Kaduna yake bamu labari, yana (service) din ne a gidan marayu na Jihar Taraba (Taraba State Orphanage Home).
Maimunatu marainiya ce, da ta tashi ba uwa ba uba, ba dangi a gidan marayu. Kamar yadda Baban ABU ya baiwa su Baban Kaduna labari, ni kuma a lokacin bani da wayo da nayi wayo ne naji labarin a bakin Hajjah.
An tura Ahmadu A.B bautar kasa Jihar Taraba, acan yaga Maimunatu, inda yake (serving) wato Taraba State Orphanage Home. Tana daga cikin 'yan mata goma a gidan marayun da suka kai minzalin aure, sannan mafi nutsuwa da kamalar cikinsu.
Ya je ne a matsayin malamin (secondary school) dinsu, yana koyar dasu kimiyyar noma, wato (Agricultural Science).
Maimunatu hazikar yarinya ce wadda Allah Ya yiwa baiwar kwakwalwar fahimtar karatu.
Kamar yadda yake a cikin (psychological nature) na kowanne malamin makaranta. Wato kaunar hazikin dalibi da girmama shi hakan ce ta faru tsakanin Baban ABU da Momin ABU har kuma ya rikide zuwa soyayya mai tsafta da inganci. Wadda tausayi da kauna, shi ne tubali da ginshikinta.
Kamar yadda Hajjah ke bamu labari, ta ko'ina Ahmadu A.B ya hanga ya tauna baiga ta inda marigayi mahaifinsa A.B zai amince masa auren Maimuna ba.
Bar ta auren zumuncin gidansu da suka maida shi farillah, kuma shika-shikan rayuwarsu, rashin ASALI wani babban abu ne domin kashi tamanin cikin dari na yaran dake gidan marayu har abada ba'a sanin asalinsu ko ganin wani nasu. A haka suke zuwa duniya su koma, cikin kiyayewar Ubangiji.
Wannan yasa Ahmadu A.B cikin tsaka mai wuya da tunanin abin yi. Na farko ba zai iya barin Maimunatu ba, maganar ma ace ya hakura da ita bata taso ba, domin ba karamin sonta yake ba, kuma shakuwar dake tsakanin su ta wuce tunanin kowa.
Sai ya yi tunanin wadda yake ganin zata fisshe shi saboda KURUCIYA irin wadda ta faru dani akan Fa'izah!
Ahmadu yaje kotun Musulunci an daura musu aure da Maimuna ta yin amfani da malaman shi na Jami'ar Ahmad Bello. Ya dauko Maimunatu ta kawowa Hajjah, a lokacin da cikin Fa'izah wata bakwai.
Mafari kenan dana tashi cikin nunawa Momin Fa'izah wariya da kabilanci a tsakanin su Mama, Aunty Hauwa da tsararrakinta. Shi din ma na fatar baki ne, ko kallon banza ban taba yi mata ba, sannan a bayan idonta musamman idan Fa'izah ta bani haushi.
Hali ne na zuri'armu baki daya (kabilanci) da 'ethnocentrism' duk wanda ba daga zuri'ar A.B ya fito ba, to fa ba cikakken mutum bane.
Da Hajjah da marigayi suka ji kowacece Maimunatu hankalinsu ya tashi kwarai, sunyi fushi da Baban ABU fushi mai tsanani, sannan 'punishment' dinsa shi ne 'suspension' daga duk wani abu da ya shafi zuri'ar A.B zuwa wani lokaci da basu kayyade ba. Duk Ahmadu ya ce yaji ya gani, indai zasu barshi ya cigaba da rayuwa da ita.
A lokacin hatta zuwa daurin auren cikin gida an dakatar dashi, haka itama, zuwa wani sha'ani na mata kamar biki ko suna duk ba’a bukatar su.
Zance ko da Baban ABU ya damu to kadan ne tunda gogaggen dan boko ne wadanda (time matters a lot for them) wato lokaci abu ne mai matukar muhimmanci a garesu. Sai ya yi amfani da lokacin 'suspension' din nasu ya koma makaranta ya nemi (degree) na biyu. Ita kuma ya sanyaata a (school of Nursing and Midwifery).
Ba da bata lokaci ba yana kammalawa A.B.U suka dauke shi 'lecturing' ya kuma samu gida a cikin makaranta, domin ada a gidan haya suke domin gidansa na A.B Quaters an hana shi mukullin an rufe. A lokacin tuni an haifi fa’izah har tayi wayo.
Kafin A.B ya rasu ya yafewa dansa Ahmadu, ya kuma karbi Maimunatu a matsayin surukar kaddara, bayan haihuwar danta na biyu, wato Abdallah, saboda kyawawan halayenta da zuri'a da tazo musu da ita mai albarka mai kama da nasu 'ya'yan. Domin Abdallah sak mahaifinsa, Fa'izah kuma Aunty Rabi ta debo, sai dai ta dauko duhun Maimunatu. Dama kuma abinda basa so kenan na auren bare, domin zai haifar da sauyin kamanni a cikinsu. Amma tabbas da Maimunatu na da iyaye, da sun maida ta ga iyayenta ko Ahmadu zai mutu, sun karbeta ne saboda MARAICIN ta.
Nayi nadama, nadama mai yawa akan duk abinda na yiwa Fa'izah! Nadamar da bani da tabbacin akwai ranar da Fa'izah zata karbeta, tunda ba zata taba tsayawa ta saurari kalaman bakina ba. Fatana Allah Ya bani iko da damar nunawa Fa'izah kuskurena da karbarsa kafin na kwanta dama... Ya yaye min wannan ginshiran, domin ni kaina yana wahalar dani...".
Da na kawo nan kuka na rikice da shi sosai, na kasa ci gaba da karatun, na ya da littafin. A guje nayi daki na ina kuka wiwi, na fada tsakiyar gadona na ci gaba da rasgar kuka.
Nayi kuka-nayi kuka har naji babu dadi. Wannan shaukin ke kara mamayar zuciyata yana kara habaka. Wanda da nayi tsai da zuciyata na fahimci abinda bana so in fahimta da gangan. Wato SON FA'IZ ne yake mamayata cikin kowanne dakika na bayan da ya barni. Wani irin so mai cin rai, da tafarfasa zuciya.