Sashe 35
Yar Bariki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
(60)
Takai mintuna biyar kafin ta kammala saidai kuma jin yanda hayaniya da shewar murna ta cika dakin inna ya hana Tasleem fitowa yayin data kifa goshinta jikin kofar bandakin tana rusar kuka. Ta tabbata an daura aurenta da Haris akan sadaki dubu hamsin. Shikenan Haris ya samu damar wulakantata da cin zarafinta. Yan uwanta sun kasa fahimtar Haris ba kaunarta yakeyi ba. Ta bandakin tana jiyo muryar Baharu yana labarta musu cewar ai Haris ne ya nemi a daura auren a yanzu,Abba(alhaji Aliyu,mahaifinsa) yana fadan wane irin gaggawa ne haka? Liman yace hakan shine daidai tunda gashi an hadu domin har mijin Mamma,Dad yana wajen wanda shine ya zama wakilin tasleem aka daura auren kawai. Zahra ma an daura saidai an bar tarewar sai nan da wata daya bayan an kammala shirye shirye. Nan dakin ya dauki kabbara cike da sowar farin cikin jin wannan labari. Tana jin sadda d'iyar Dada(dada matar kanin Liman daya rasu take zaune gidan) wacce take zawarci sakamakon mijinta daya rasu da jimawa,wato Hafsa ta tahowa tana buga kofar tana fadin
"Fito kin kunshe kanki a bandaki,komin abunki fa sai mun murjeki da lalle." Aka kwashe da dariya kafin dai kowa ya tattara ya fice. Saida taji shiru sannan ta fito, ji tayi an rukunkumeta ana dariya
"Ja'ira,ai daman nace sai na ga fuskarki." Cewar Hafsat. Tasleem tana kuka tace
"Anti Hafsa kina kallo aka auramin wanda baya kaunata baya sona? Anya ba'a kwareni ba?"
Jikin Hafsa yayi sanyi,ta ja hannunta suka zauna bakin gado
"Haba Tasleem,kinga yanda yake rawar kafa da wasa da dariya kuwa? Anya zan amince baya sonki? Kodai kece bakya sonshi ne?"
Tasleem tayi shiru da kukan,toh tana da bakin cewa batason mutumin da tun zuwanta Kazaure dashi take kwana take tashi a zuciyarta? Tabbas tana son Haris. Banda Rilwan bata taba son wani d'a namiji ba da zuciya daya sai shi.
"Kinyi shiru?"
Inna dake jinsu tace
"Ki rabu da wannan sakaryar wacce batasan abunda ya dace gareta ba. Nikam takaicinta ma yana sanyani jin kamar na kwasheta da mari."
Hafsa taja hannun Tasleem sukayi hanyar fita zuwa dakinta tana fadin
"Ayi hakuri innarmu,kinsan sabon shiga."
Inna ta tabe baki suka nufi dakin Hafsat. Ita dinma rarrashi da ban baki gami da gwada mata hanyoyin kissosi da zata bi domin mallakar zuciyar Haris cikin sauki. Tasleem dai sauraronta kawai takeyi,wannan ba matsalarta bace,babu wani abu na fannin kissa da bata kware dashi ba saidai Hafsa ta gaza fahimtar matsalarta. Ita fa kalaman da Haris keyi mata ne yake daukar hankalinta.
"Nan zuwa sati biyu za'a kawo lefenku. Aurensa dake aka soma d'aurawa sannan kuma da Zahra. Kinga kenan matsayinki ta babba dole saikinyi hakuri kin rike girmanki koda dai Zahra bata da raini yarinyar akwai hankali da nutsuwa ba kamar su Atika ba. Duk da haka sai kin dage."
Haka dai sukayita hirarsu har Hafsat take bata labarin zaman hakurin da tayi da facalolinta wanda yasa Tasleem sakewa sosai. Sallamar Musty ta katsesu. Ya shigo suka hada ido da Tasleem yayi mata murmushi a sanyaye
"Babana ya akayi?" Cewar anti Hafsa kasancewar sunan kanin Liman yaci kuma mahaifi gareta. Hakanan mustapha jikan Dada ne mahaifiyarta sannan shi din maraya ne gaba da baya a hannun Dada ya girma har zuwa aurensa da Farida.
Ya zauna saman hannun kujera yana yamutsa fuska
"Ina fa lafiya kuna ji kuna gani an kwacemin matata." Duk suka dubeshi Tasleem kuwa saita dauki abun wasa ashe Antin ma wasa ta dauka jin tayi dariya tace
"Me zatayi dakai yarinya yar birni.?"
Ta fice daga dakin,Tasleem ta gaidashi yak'i amsawa
"Small ashe zaki iya auren wani ba ni ba?"
A mamakince ta yamutsa fuska kadan kamar bazatayi magana ba sai kuma tayita tamkar bataso
"Wai daman kana sona ne yaya?"
Musty ya ciji lebbansa cike da takaici
"Tun kina secondary nake dawainiya da sonki. Allah bai kaddaro ke zam fara aure ba sai Farida. Yanzu kuma gashi ina murnar dama tazo min sai kawai na tsinci labarin aurenki da wannan gayen."
Ya danyi shiru itama tausayinsa takeji,
"Haka Allah Ya kaddaromin. Allah Ya baki zaman lafiya da mijinki. Saidai ina fushi har yau gashi satinki daya cif a garin nan baki tako kinga matata ba shiyasa nima duk da dokin ganinki da takeyi domin ina yawan bata labarin sister dita mai sona amma na hanata zuwa."
Ya karashe a wasance,itama ta share wancan zancen watakila dai ya tuna a yanzun matar aure ce,
"Kayi hakuri dai yaya mustyna,zan shigo."
"Ai na mantaa yanzun saida iznin oganki ko?"
Gabanta ya fadi,ashe yanzu komai zatayi saida iznin Haris? Tab ai kuwa ta gwammace tayi ta zaman gidan gashi tana matukar son komawa wajen mahaifiyarta domin ta kara neman afuwarta.
"Bari na wuce."
Ya maidota daga kogin tunanin data shiga,ta dubeshi har yakai kofa
"Toh yaya saida safe." Itama ta mike ta koma dakin inna. Sallar isha'i kawai tayi kafin tayi zaman hira da inna. Sai ga Liman ya aiko kiranta. Ta iskeshi babu kowa a dakin sai shi. Nan yayi mata doguwar nasiha akan aure da nuna mata ita din yanzu fa karkashin ikon Haris take sannan ya gargadeta data dunga mutunta shigarta. A karshe ya damka mata sadakinta tace ita yanzu bata da abunda zatayi dashi,ya adana mata. Yace shikenan. Ta mike ta fita, zatayi ciki taji muryar Baharu a bayanta yana kiranta dole ta tsaya ta dubeshi ta lura dai d'asawa yakeyi da Haris sosai. Leda ya mik'omata yana dariya
"Gashi inji maigidanki."
Ita kam duk sadda aka dangantata da Haris sai gabanta ya fadi,tasa hannu ta karba babu ko godiya tayi ciki.
Waya ce da chajinta da komai,sai kwalinta da alama harda sim. Blackberry ce. Sai kayan ciye ciye, nan inna ta hau duddubasu tana fadin oh,abun dadi basu karewa a duniya. Wayar tayi k'arar shigowar sak'o. Ta bude ganin lamba.
"Ga waya nan,ban amince ki bawa kowane namiji damar mallakarta ba ke daidai da dan uwanki banda Abdullah banason ganin lambar kowaye!
"Harith"
Ta tabe baki ai shi d'inma bazaici darajar saving number nasa ba a wayar. Ta ajiye wayar ta mike domin watsawa kanta ruwa haka dai inna ta dauka tayita kalle kallenta tana fadin yanda wayar ta burgeta kwarai.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(59)
Cikin fushi inna ta ture tasleem daga jikinta
"Ke ni matsamin kibani wuri shashashar banza kawai! Aure hauka ne? Don za'ayi maki gata ke kuma kin kasa fahimta? Toh wallahi ba baki zanyi maki ba Tasleem,amma matukar kika bari batun auren nan naku ya rushe da yaron nan zaiyi wuya ki samu madadinsa. Ke kamar wata yarinya karama,a hakan ake cewa kinyi degree? Amma tabbas bakiyi kama da matan jami'a ba sam sam baki da wayewa. Mts. (Hhhh kuji fa! Baby ake fadawa duniya..cewar Rufaidarh)
Ta dago ta dubi inna dake faman zazzaga masifa
"Shi da bakinsa fa yace baya sona lik'a mi.."
"Kina nufin Liman k'arya yayi maki?"
Ita dai batace uffan ba,ai sai fadan inna ya k'aru karshe tace bazata iya ba saita had'ata da mamma. Sai kuma tayi shiru kafin ta kara cewa
"Allah Ya kyauta,namanta ashe ita dinma daren jiya tazo tana surutanta wai don me za'a yiwa Harisu haka? Saida na zageta tsaf na nuna mata kurenta sannan tace shikenan. Haka kawai kunbi kun tsani yaro na arziki ma."
Haka dai inna ta mike ta fice bayan ta dauki furar data kammala damunsa zata bayar a mik'awa bak'i.
Baby ringingine ta kwanta ta lumshe ido yayinda kwakwalwarta ke k'ara tunano mata bakaken maganganun Haris daya jefa mata. Zarginta ya tabbata kenan ba sonta yakeyi ba? Zahra,Zahra? Wacece ma hakan?
'Yar farar yarinyar nan dai siririya mai siririyar fuska. Kallo daya zakayi musu ita da Haris ka tabbatar da cewar jini d'aya suke saboda matukar d'ibar kamar da sukeyi da juna. Bata da mazauna sosai hakanan kirjinta baida cika sosai.
Tabbas ta tuno Zahra, itace dai wacce tayi mata rakiya gidansu KB. Murmushi kawai tasleem tayi tunawa da sanyin halinta. Babu ruwanta watakila shine dalilin da yasa Haris ke sonta. Kaico da rayuwarta,ita kam ba abun ta samu su Baffa ba tace bata kaunar auren nan.
"Taso kije Harisu ya aiko kiranki."
Ta bude idanuwanta sosai jin muryar inna. A sanyaye ta mike,ita fa batasan dalilin da yasa take shakkar Haris ba,kai bata taba kawowa bama zataji tsoron wani d'a namiji ba sai Haris.
"Don Allah ki mutuntashi babu kyau wulakanta mutum."
Murmushi tayi mai ciwo,ta mike ta dauki mayafinta ta fita bayan ta zura silifas. Ta nufi zauren saidai bayanan,ta karasa waje gabanta na dukan tara tara. Hon da taji ya tabbatar mata cikin motarsa yake, hakan yasa ta karasa kafin ta bude ta shiga. Bazata mance motar nan ba a tarihin rayuwarta,motar data fayyacewa Haris komai na sirrin rayuwarta?
"Baki iya gaisuwa bane ko kuwa dai rashin tarbiyya zaki gwadamin?"
Ta kalleshi
"Haris wai menayi maka hakane? Haris ka chanja ba haka...."
Kallon daya watsa mata shi ya sanyata yin shiru.
"Ba wannan na tambayeki malama."
"Barka da yamma."
Ya tabe baki kadan
"Rike abinki tunda rok'a nayi. Abunda nakeson sani shine,kinga period naki?"
Ta kauda kanta ga barin kallonsa
"Da asuba nayi wanka."
"Kina iya tafiya."
Shiru na mintuna,ganin bata da niyyar motsawa yasa shi saurin fita ya rabu da ita a motar. Tana kallonsa ya koma ciki,hawayenta suka kara kwaranyowa karo na ba adadi,toh zaman me takeyi kuma? Kawai saita bude ta fito itama.
*****
"Ayyiriri yiriri! Kai Alhamdulillah. Harda na Zahra?"
Batasan lokacin da cikinta ya murd'a ba,me kunnuwanta ke shirin ji mata ne? Innalillahi wa inna ilaihiraaji'un!
Da azama ta nufi bandaki domin rage cikinta......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar
(61)
Takai mintuna biyar kafin ta kammala saidai kuma jin yanda hayaniya da shewar murna ta cika dakin inna ya hana Tasleem fitowa yayin data kifa goshinta jikin kofar bandakin tana rusar kuka. Ta tabbata an daura aurenta da Haris akan sadaki dubu hamsin. Shikenan Haris ya samu damar wulakantata da cin zarafinta. Yan uwanta sun kasa fahimtar Haris ba kaunarta yakeyi ba. Ta bandakin tana jiyo muryar Baharu yana labarta musu cewar ai Haris ne ya nemi a daura auren a yanzu,Abba(alhaji Aliyu,mahaifinsa) yana fadan wane irin gaggawa ne haka? Liman yace hakan shine daidai tunda gashi an hadu domin har mijin Mamma,Dad yana wajen wanda shine ya zama wakilin tasleem aka daura auren kawai. Zahra ma an daura saidai an bar tarewar sai nan da wata daya bayan an kammala shirye shirye. Nan dakin ya dauki kabbara cike da sowar farin cikin jin wannan labari. Tana jin sadda d'iyar Dada(dada matar kanin Liman daya rasu take zaune gidan) wacce take zawarci sakamakon mijinta daya rasu da jimawa,wato Hafsa ta tahowa tana buga kofar tana fadin
"Fito kin kunshe kanki a bandaki,komin abunki fa sai mun murjeki da lalle." Aka kwashe da dariya kafin dai kowa ya tattara ya fice. Saida taji shiru sannan ta fito, ji tayi an rukunkumeta ana dariya
"Ja'ira,ai daman nace sai na ga fuskarki." Cewar Hafsat. Tasleem tana kuka tace
"Anti Hafsa kina kallo aka auramin wanda baya kaunata baya sona? Anya ba'a kwareni ba?"
Jikin Hafsa yayi sanyi,ta ja hannunta suka zauna bakin gado
"Haba Tasleem,kinga yanda yake rawar kafa da wasa da dariya kuwa? Anya zan amince baya sonki? Kodai kece bakya sonshi ne?"
Tasleem tayi shiru da kukan,toh tana da bakin cewa batason mutumin da tun zuwanta Kazaure dashi take kwana take tashi a zuciyarta? Tabbas tana son Haris. Banda Rilwan bata taba son wani d'a namiji ba da zuciya daya sai shi.
"Kinyi shiru?"
Inna dake jinsu tace
"Ki rabu da wannan sakaryar wacce batasan abunda ya dace gareta ba. Nikam takaicinta ma yana sanyani jin kamar na kwasheta da mari."
Hafsa taja hannun Tasleem sukayi hanyar fita zuwa dakinta tana fadin
"Ayi hakuri innarmu,kinsan sabon shiga."
Inna ta tabe baki suka nufi dakin Hafsat. Ita dinma rarrashi da ban baki gami da gwada mata hanyoyin kissosi da zata bi domin mallakar zuciyar Haris cikin sauki. Tasleem dai sauraronta kawai takeyi,wannan ba matsalarta bace,babu wani abu na fannin kissa da bata kware dashi ba saidai Hafsa ta gaza fahimtar matsalarta. Ita fa kalaman da Haris keyi mata ne yake daukar hankalinta.
"Nan zuwa sati biyu za'a kawo lefenku. Aurensa dake aka soma d'aurawa sannan kuma da Zahra. Kinga kenan matsayinki ta babba dole saikinyi hakuri kin rike girmanki koda dai Zahra bata da raini yarinyar akwai hankali da nutsuwa ba kamar su Atika ba. Duk da haka sai kin dage."
Haka dai sukayita hirarsu har Hafsat take bata labarin zaman hakurin da tayi da facalolinta wanda yasa Tasleem sakewa sosai. Sallamar Musty ta katsesu. Ya shigo suka hada ido da Tasleem yayi mata murmushi a sanyaye
"Babana ya akayi?" Cewar anti Hafsa kasancewar sunan kanin Liman yaci kuma mahaifi gareta. Hakanan mustapha jikan Dada ne mahaifiyarta sannan shi din maraya ne gaba da baya a hannun Dada ya girma har zuwa aurensa da Farida.
Ya zauna saman hannun kujera yana yamutsa fuska
"Ina fa lafiya kuna ji kuna gani an kwacemin matata." Duk suka dubeshi Tasleem kuwa saita dauki abun wasa ashe Antin ma wasa ta dauka jin tayi dariya tace
"Me zatayi dakai yarinya yar birni.?"
Ta fice daga dakin,Tasleem ta gaidashi yak'i amsawa
"Small ashe zaki iya auren wani ba ni ba?"
A mamakince ta yamutsa fuska kadan kamar bazatayi magana ba sai kuma tayita tamkar bataso
"Wai daman kana sona ne yaya?"
Musty ya ciji lebbansa cike da takaici
"Tun kina secondary nake dawainiya da sonki. Allah bai kaddaro ke zam fara aure ba sai Farida. Yanzu kuma gashi ina murnar dama tazo min sai kawai na tsinci labarin aurenki da wannan gayen."
Ya danyi shiru itama tausayinsa takeji,
"Haka Allah Ya kaddaromin. Allah Ya baki zaman lafiya da mijinki. Saidai ina fushi har yau gashi satinki daya cif a garin nan baki tako kinga matata ba shiyasa nima duk da dokin ganinki da takeyi domin ina yawan bata labarin sister dita mai sona amma na hanata zuwa."
Ya karashe a wasance,itama ta share wancan zancen watakila dai ya tuna a yanzun matar aure ce,
"Kayi hakuri dai yaya mustyna,zan shigo."
"Ai na mantaa yanzun saida iznin oganki ko?"
Gabanta ya fadi,ashe yanzu komai zatayi saida iznin Haris? Tab ai kuwa ta gwammace tayi ta zaman gidan gashi tana matukar son komawa wajen mahaifiyarta domin ta kara neman afuwarta.
"Bari na wuce."
Ya maidota daga kogin tunanin data shiga,ta dubeshi har yakai kofa
"Toh yaya saida safe." Itama ta mike ta koma dakin inna. Sallar isha'i kawai tayi kafin tayi zaman hira da inna. Sai ga Liman ya aiko kiranta. Ta iskeshi babu kowa a dakin sai shi. Nan yayi mata doguwar nasiha akan aure da nuna mata ita din yanzu fa karkashin ikon Haris take sannan ya gargadeta data dunga mutunta shigarta. A karshe ya damka mata sadakinta tace ita yanzu bata da abunda zatayi dashi,ya adana mata. Yace shikenan. Ta mike ta fita, zatayi ciki taji muryar Baharu a bayanta yana kiranta dole ta tsaya ta dubeshi ta lura dai d'asawa yakeyi da Haris sosai. Leda ya mik'omata yana dariya
"Gashi inji maigidanki."
Ita kam duk sadda aka dangantata da Haris sai gabanta ya fadi,tasa hannu ta karba babu ko godiya tayi ciki.
Waya ce da chajinta da komai,sai kwalinta da alama harda sim. Blackberry ce. Sai kayan ciye ciye, nan inna ta hau duddubasu tana fadin oh,abun dadi basu karewa a duniya. Wayar tayi k'arar shigowar sak'o. Ta bude ganin lamba.
"Ga waya nan,ban amince ki bawa kowane namiji damar mallakarta ba ke daidai da dan uwanki banda Abdullah banason ganin lambar kowaye!
"Harith"
Ta tabe baki ai shi d'inma bazaici darajar saving number nasa ba a wayar. Ta ajiye wayar ta mike domin watsawa kanta ruwa haka dai inna ta dauka tayita kalle kallenta tana fadin yanda wayar ta burgeta kwarai.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(59)
Cikin fushi inna ta ture tasleem daga jikinta
"Ke ni matsamin kibani wuri shashashar banza kawai! Aure hauka ne? Don za'ayi maki gata ke kuma kin kasa fahimta? Toh wallahi ba baki zanyi maki ba Tasleem,amma matukar kika bari batun auren nan naku ya rushe da yaron nan zaiyi wuya ki samu madadinsa. Ke kamar wata yarinya karama,a hakan ake cewa kinyi degree? Amma tabbas bakiyi kama da matan jami'a ba sam sam baki da wayewa. Mts. (Hhhh kuji fa! Baby ake fadawa duniya..cewar Rufaidarh)
Ta dago ta dubi inna dake faman zazzaga masifa
"Shi da bakinsa fa yace baya sona lik'a mi.."
"Kina nufin Liman k'arya yayi maki?"
Ita dai batace uffan ba,ai sai fadan inna ya k'aru karshe tace bazata iya ba saita had'ata da mamma. Sai kuma tayi shiru kafin ta kara cewa
"Allah Ya kyauta,namanta ashe ita dinma daren jiya tazo tana surutanta wai don me za'a yiwa Harisu haka? Saida na zageta tsaf na nuna mata kurenta sannan tace shikenan. Haka kawai kunbi kun tsani yaro na arziki ma."
Haka dai inna ta mike ta fice bayan ta dauki furar data kammala damunsa zata bayar a mik'awa bak'i.
Baby ringingine ta kwanta ta lumshe ido yayinda kwakwalwarta ke k'ara tunano mata bakaken maganganun Haris daya jefa mata. Zarginta ya tabbata kenan ba sonta yakeyi ba? Zahra,Zahra? Wacece ma hakan?
'Yar farar yarinyar nan dai siririya mai siririyar fuska. Kallo daya zakayi musu ita da Haris ka tabbatar da cewar jini d'aya suke saboda matukar d'ibar kamar da sukeyi da juna. Bata da mazauna sosai hakanan kirjinta baida cika sosai.
Tabbas ta tuno Zahra, itace dai wacce tayi mata rakiya gidansu KB. Murmushi kawai tasleem tayi tunawa da sanyin halinta. Babu ruwanta watakila shine dalilin da yasa Haris ke sonta. Kaico da rayuwarta,ita kam ba abun ta samu su Baffa ba tace bata kaunar auren nan.
"Taso kije Harisu ya aiko kiranki."
Ta bude idanuwanta sosai jin muryar inna. A sanyaye ta mike,ita fa batasan dalilin da yasa take shakkar Haris ba,kai bata taba kawowa bama zataji tsoron wani d'a namiji ba sai Haris.
"Don Allah ki mutuntashi babu kyau wulakanta mutum."
Murmushi tayi mai ciwo,ta mike ta dauki mayafinta ta fita bayan ta zura silifas. Ta nufi zauren saidai bayanan,ta karasa waje gabanta na dukan tara tara. Hon da taji ya tabbatar mata cikin motarsa yake, hakan yasa ta karasa kafin ta bude ta shiga. Bazata mance motar nan ba a tarihin rayuwarta,motar data fayyacewa Haris komai na sirrin rayuwarta?
"Baki iya gaisuwa bane ko kuwa dai rashin tarbiyya zaki gwadamin?"
Ta kalleshi
"Haris wai menayi maka hakane? Haris ka chanja ba haka...."
Kallon daya watsa mata shi ya sanyata yin shiru.
"Ba wannan na tambayeki malama."
"Barka da yamma."
Ya tabe baki kadan
"Rike abinki tunda rok'a nayi. Abunda nakeson sani shine,kinga period naki?"
Ta kauda kanta ga barin kallonsa
"Da asuba nayi wanka."
"Kina iya tafiya."
Shiru na mintuna,ganin bata da niyyar motsawa yasa shi saurin fita ya rabu da ita a motar. Tana kallonsa ya koma ciki,hawayenta suka kara kwaranyowa karo na ba adadi,toh zaman me takeyi kuma? Kawai saita bude ta fito itama.
*****
"Ayyiriri yiriri! Kai Alhamdulillah. Harda na Zahra?"
Batasan lokacin da cikinta ya murd'a ba,me kunnuwanta ke shirin ji mata ne? Innalillahi wa inna ilaihiraaji'un!
Da azama ta nufi bandaki domin rage cikinta......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar
(61)