Sashe 19
Yar Bariki Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Yaya mustyna kai dawa kuke tafe? Ya akayi kukasan da wannan ranar?"
Ya harareni
"Bayan da kika k'i kiranmu a waya ki sanar damu sai Abdullah dake a wata k'asar ne zai gayamana?"
Nayi dariya a shagwabance nace
"Afuwan yayana,yanzu kai da waye kuke tafe?"
Yana dariya yaja hannuna yana fadin
"Muje ki ganewa idonki."
Haka mukayita kutsawa taron jama'a bai tsaidani gaban kowa ba sai Mamma da gwaggo Hajara. Ihun murna na saki ban damu da wadanda suka kalloni ba. Na rukunkume Mamma kafin na saketa na rungumi Gwaggo Hajara. Bansan ya akayi ba kawai sai na fashe da kuka sosai,har wani malamin Chemistry dinmu sarkin shishshigi ya matso wai bai taba ganin kukan Headgirl ba(kasancewar mukamin dana rike kenan a makaranta)sai a yau. Su mamma sukayi dariya,nikam na harareshi dariya kawai yayi ya kara gaba bayan yace"Madam,your daughter is one of my best students,very talented." Mamma murmushi tayi kawai. Kirana da aka karayi ne naje nayi speech a matsayina na headgirl na mike na tashi bayan na damkawa Mamma certificate dina. Tiryan tiryan nayi na gama na yiwa manyan bak'i fatan komawa gida lafiya sannan na bada shawara ga juniors dinmu nan aka hau tafi raf raf akarshe na koma gasu Mamma mukayi ta daukar hotuna. Munnira da Jamila suma suka iso suka gaida Mamma.
Ina zaune kawai sai naga yaya musty ya shigo da kwalaye,nayi mamakin ganin jakunkunan rabo dauke da memo fa handfan a ciki. Na kalleshi idona taf da kwalla,yace
"Zaki soma kuma dai? Muddin kikayi kuka zan fasa baki."
Gwaggo Hajara tayi dariya
"Wannan hukunci yayi."
Nayi azamar share fuskata
"Kaga nabar kuka yayana."
Mukayi dariya,ashe tun sadda na sanarwa Yaya abdullah ya gayamusu. Shine Mamma ta bayar ayimin memo,anan shima Malam ya k'ara mata kud'i. Don farin ciki na rasa inda zansa raina.
"Hamida,hindatu."
Hamida ta kalleta ta tabe baki tayi gaba,hindatu ce ta tako ta gaishesu. Mamma ta dafa kanta tana murmushi bayan sun amsa. "Ina maminku? Ku gaisheta."
Kusan lokaci daya muka dubi Mamma nida gwaggo Hajara,gwaggo Hajara harararta tayi. Nikam mamakin rashin zuciya irin na Mamma nakeyi,bata fushi. Da hindatu kadai na dauki hotuna,a karshe yaya musty ya amshi camera dita da zummar zaisa a wankemin hotunan harda na tasa wayar. Naji dadi sosai.
Har kusan azahar muna tare kafin a watse suma su soma shirin komawa Kazaure. Anan ne idona ya raina fata,gwaggo Hajara ta dafani
"Haba 'yata,menene abun kukan? Kiyi hakuri,tunda kunyi hutu saiki tambayi Abbanki idan ya amince sai kizo mana koda sati kiyi kinji? Kukanki sai ya karyar da zuciyoyinmu."
Suka lallabani suka tafi.
A ranar kuwa nasha zagi wajen Raliya dana koma,saidai batayi gigin taba lafiyata ba. Aikin da acewarta na gudarwa,dole na yishi. A banza kam tunda na samu ranar nan ta tafimin cikin matsanancin farin ciki. Ban kwanta ba sai wajen goman dare. Anan ma banyi baccin ba don hira nayi tayi da hindatu akan makarantarmu kafin bacci ya suremu........!
Tun daga wannan ranar kuma sai na soma
sakewa Usman kadan kadan,nakan gaisheshi
hakanan nakan je dukkan wani aiken da zaiyimin
zuwa gidansa ko kicin din Raliya da sauransu.
Ban dai sakarmishi sosai ba,amma babu wannan
rainin sosai. Har kuwa zuwa lokacin bai rabu da
fita yawon dare ba. Nasha ganin Meena tazo
wajen Raliya tana bala'i akan ita ta soma gajiya
da bin mata irin na Usman,mutum tamkar wanda
aka yiwa asiri. Raliya saidai ta bata hakuri don
babu laifi iyayen meena akwai naira hakanan
takan lasawa Raliya sosai domin ita din macece
wacce bata godiya ga Allah. Duk da irin arzikin da
ta hau kai tayi zaune na Abba,ga kuma business
da takeyi,hakan bai hanata hangen na wasu ba.
Bayan watanni uku,lokacin Mamma ta kusa
shekara a gidansu,kawai na tsinci wayar Yaya
musty yana yimin albishir cewar an daurawa
Mammana aure da wani almajirin Malam. Har
tsalle nayi don murna. Yara da yawa sukanyi
bakin ciki idan uwarsu zatayi wani auren alhalin
ubansu na raye, kai koda ace baya raye akwai
yaran dake taya ubansu kishi amma nikam
baruwana ko a jikina. Daga dariya kuma sai na
fashe da kuka. Ina cewa shine ko a gayamin nazo
da wuri? Dariya yayi yace kada na damu anan
Kazaure Mamma zata zauna duk sanda naga
dama na tambayi Abba ya barni toh nazo na
ganta. Naji dadi kwarai ya kara tambayata game
da Yaya abdullah nace mishi sauran mishi
watanni uku kawai ya dawo. Daga haka mukayi
sallama tare da alkawarin idan yaje gidan zai
kirani mu gaisa da Mamma.
Ai kuwa ko awa biyu ba'ayi ba yayi kirana,na hau
bud'a karshe na saki dariya. Nayi mamaki dana ji
muryar Mamma a sanyaye har na tambayeta ko
bata farinciki da auren nan? Bata bani amsa ba
ta share da tambayar lafiyata. Nace
alhamdulillah,tace zan cigaba da karatune? Na
tabe baki "Bansani ba Mamma." "Kamar ya baki
sani ba Tasleem? Keda mahaifinki? Kije kiyi mishi
magana tun lokaci bai kure maki ba."
Na amsa da toh saidai kuma abunda Mamma
batasani ba shine,idan har sai naje ga Abba na
gwammace nayita zama haka a gidan. Haka
mukayi sallama da ita.
Bayan kwana biyu,Meena matar Yaya Usman ta
haife tsohon cikinta ta samu d'iya mace. Murna a
wajen yan gidan ba'a magana. Nikam ko ajikina
daman ba wani mutuncinsu nake gani ba.
*******
Bayan kwana uku da haihuwar meena,misalin
biyar na yamma,ina zaune a bakin firij na Raliya
ina gogewa,ita kuwa da yaranta suna falon suna
kallon wasan Hausa saidai ko inda suke bana
kalla ballantana film din da suke kallo ya dauki
hankalina don tun fil'azal fina finan hausa ba
burgeni sukeyi ba barni da da kallon Indian series
da Korea anan kam ko makiyina ke kallo zan saci
kallo. Sallamar Usman ta katsesu,Hamid bai
amsa ba saima ya mike ya fice saboda a yanzu
haushinsa yakeji akaina. Bayan su hamida sun
gaisheshi ya dubi Raliya.
"Wa kike ganin ya dace ta zauna wajen Meena
ne?"
Yayi maganar tamkar da sa'arsa,Raliya bata ko
damu ba ta kyabe baki
"A'a toh,ko Dijangala ai sai ta zauna. Idan kuwa
batason aikinta ga waccan tsiyar saiku kwasa."
Sai lokacin na dubeta kafin na watsawa Usman
mugun kallo wanda na jima banyi mishi irinsa ba.
Murmushi yayi ya dubi Raliya
"A'a dijangala shiririta ne da ita,tunda dai ga
gwaggon meena zata dunga yi musu wanka sai
Tasleem ta dunga gyare gyarem gidan."
Raliya bata musa ba domin duk yanda zan
kuntata a rayuwa shi tafi kauna. Tace
"Hakan ma yayi,ke! Idan kin kammala ki tattaro
kayanki ki koma gidan Usman har sai matarsa ta
gama wanka sannan zaki dawo."
Bance uffan ba don bakin ciki,a matukar fusata ta
kammala aikin na mike na shiga daki. Haka na
tattaro kayan na fito. Hamida mukayi arba da ita
ta tuntsire da dariya gami da yimin gwalo"Haka
zaki k'are." Kamar nace mata wani abu saidai na
fasa nayi gaba,Raliya har lokacin tana falon
banko kalleta ba nayi gaba abina a fusace.
Saida nazo daidai garden na zube anan na fashe
da kuka,wai haka rayuwata zata k'are? Wane irin
uba gareni da bai daukeni komai ba? Ya manta
da ya haifeni ne har ya banzatar dani a gidansa
ya maidani wofi? Ace yan aiki ma sun fini daraja
da kima a gidannan? Na daga kaina nakai duba
da d'an lilon da muka saba wasa da Yayana.
Haka zaiyita cillani yana goyani muna zagaye
garden dinnan muna dariya. Ba zato naji an
dafani ta baya,nayi azamar juyowa ganin Usman
bansan lokacin da naja tsaki ba nayi kokarin
mikewa yayi saurin dawowa ta gabana.
"Haba Tasleem,ashe tsanar da kika yimin har
takai ace kije ki taimakawa matata ki zauna kina
kuka? Duk cikinmu waye mai tausayinki bayan
ni? Haba Tasleem,banji dadi ba wallahi."
Ganin yanayin fuskarsa sai naga kamar ban
kyauta ba,nace
"Ni ba gidanka ko matarka na tsana ba ai,irin
wannan rainin hankalin da akeyimin a gidan
ubana ne na kasa gane dalilinsa. Bansan kuma
me na tsarewa mutane ba."
Na karashe cikin tsiwa,yayi dariya ya kawo hannu
zai dora kan lebbana nayi azamar ja da baya,cikin
tsoron yanayin kallon da yakemin
"Tasleem komai naki abun sha'awa ne wallahi. Ni
bana k'inki,inason ganin kanwata a kusa dani
shine ma dalilin da yasa na nemi alfarmar
zuwanki. Kiyi hakuri inajin dadin yanda kika kware
a gyara muhalli. Meena KAZAMAR GIDA ce,
banason ganin gidan nan da kazanta. Don Allah
kanwata wallahi tana yin arba'in I promise you
zaki komo gida."
Bance komai ba na mike na dauki jakata nayi
gaba yana magana ko juyowa banyi,menene
saukin da nan da can din?
****
Baby ta numfasa,hawayenta ya karu wani yana
bin wani. Haris ya miko mata (handkerchief)
dinsa,tasa hannu ta karb'a saidai bata da niyyar
share hawayen. Ta dubi Haris wanda shima ya
gaji da waigenta ya karkato gaba daya yana
duban fuskarta don jin dadin hirar.
"Haris a wannan zuwan nawa ne gidan Usman
komai na rayuwata ya soma tabarbarewa. Yanda
akayi kuwa shine......."
Ya harareni
"Bayan da kika k'i kiranmu a waya ki sanar damu sai Abdullah dake a wata k'asar ne zai gayamana?"
Nayi dariya a shagwabance nace
"Afuwan yayana,yanzu kai da waye kuke tafe?"
Yana dariya yaja hannuna yana fadin
"Muje ki ganewa idonki."
Haka mukayita kutsawa taron jama'a bai tsaidani gaban kowa ba sai Mamma da gwaggo Hajara. Ihun murna na saki ban damu da wadanda suka kalloni ba. Na rukunkume Mamma kafin na saketa na rungumi Gwaggo Hajara. Bansan ya akayi ba kawai sai na fashe da kuka sosai,har wani malamin Chemistry dinmu sarkin shishshigi ya matso wai bai taba ganin kukan Headgirl ba(kasancewar mukamin dana rike kenan a makaranta)sai a yau. Su mamma sukayi dariya,nikam na harareshi dariya kawai yayi ya kara gaba bayan yace"Madam,your daughter is one of my best students,very talented." Mamma murmushi tayi kawai. Kirana da aka karayi ne naje nayi speech a matsayina na headgirl na mike na tashi bayan na damkawa Mamma certificate dina. Tiryan tiryan nayi na gama na yiwa manyan bak'i fatan komawa gida lafiya sannan na bada shawara ga juniors dinmu nan aka hau tafi raf raf akarshe na koma gasu Mamma mukayi ta daukar hotuna. Munnira da Jamila suma suka iso suka gaida Mamma.
Ina zaune kawai sai naga yaya musty ya shigo da kwalaye,nayi mamakin ganin jakunkunan rabo dauke da memo fa handfan a ciki. Na kalleshi idona taf da kwalla,yace
"Zaki soma kuma dai? Muddin kikayi kuka zan fasa baki."
Gwaggo Hajara tayi dariya
"Wannan hukunci yayi."
Nayi azamar share fuskata
"Kaga nabar kuka yayana."
Mukayi dariya,ashe tun sadda na sanarwa Yaya abdullah ya gayamusu. Shine Mamma ta bayar ayimin memo,anan shima Malam ya k'ara mata kud'i. Don farin ciki na rasa inda zansa raina.
"Hamida,hindatu."
Hamida ta kalleta ta tabe baki tayi gaba,hindatu ce ta tako ta gaishesu. Mamma ta dafa kanta tana murmushi bayan sun amsa. "Ina maminku? Ku gaisheta."
Kusan lokaci daya muka dubi Mamma nida gwaggo Hajara,gwaggo Hajara harararta tayi. Nikam mamakin rashin zuciya irin na Mamma nakeyi,bata fushi. Da hindatu kadai na dauki hotuna,a karshe yaya musty ya amshi camera dita da zummar zaisa a wankemin hotunan harda na tasa wayar. Naji dadi sosai.
Har kusan azahar muna tare kafin a watse suma su soma shirin komawa Kazaure. Anan ne idona ya raina fata,gwaggo Hajara ta dafani
"Haba 'yata,menene abun kukan? Kiyi hakuri,tunda kunyi hutu saiki tambayi Abbanki idan ya amince sai kizo mana koda sati kiyi kinji? Kukanki sai ya karyar da zuciyoyinmu."
Suka lallabani suka tafi.
A ranar kuwa nasha zagi wajen Raliya dana koma,saidai batayi gigin taba lafiyata ba. Aikin da acewarta na gudarwa,dole na yishi. A banza kam tunda na samu ranar nan ta tafimin cikin matsanancin farin ciki. Ban kwanta ba sai wajen goman dare. Anan ma banyi baccin ba don hira nayi tayi da hindatu akan makarantarmu kafin bacci ya suremu........!
Tun daga wannan ranar kuma sai na soma
sakewa Usman kadan kadan,nakan gaisheshi
hakanan nakan je dukkan wani aiken da zaiyimin
zuwa gidansa ko kicin din Raliya da sauransu.
Ban dai sakarmishi sosai ba,amma babu wannan
rainin sosai. Har kuwa zuwa lokacin bai rabu da
fita yawon dare ba. Nasha ganin Meena tazo
wajen Raliya tana bala'i akan ita ta soma gajiya
da bin mata irin na Usman,mutum tamkar wanda
aka yiwa asiri. Raliya saidai ta bata hakuri don
babu laifi iyayen meena akwai naira hakanan
takan lasawa Raliya sosai domin ita din macece
wacce bata godiya ga Allah. Duk da irin arzikin da
ta hau kai tayi zaune na Abba,ga kuma business
da takeyi,hakan bai hanata hangen na wasu ba.
Bayan watanni uku,lokacin Mamma ta kusa
shekara a gidansu,kawai na tsinci wayar Yaya
musty yana yimin albishir cewar an daurawa
Mammana aure da wani almajirin Malam. Har
tsalle nayi don murna. Yara da yawa sukanyi
bakin ciki idan uwarsu zatayi wani auren alhalin
ubansu na raye, kai koda ace baya raye akwai
yaran dake taya ubansu kishi amma nikam
baruwana ko a jikina. Daga dariya kuma sai na
fashe da kuka. Ina cewa shine ko a gayamin nazo
da wuri? Dariya yayi yace kada na damu anan
Kazaure Mamma zata zauna duk sanda naga
dama na tambayi Abba ya barni toh nazo na
ganta. Naji dadi kwarai ya kara tambayata game
da Yaya abdullah nace mishi sauran mishi
watanni uku kawai ya dawo. Daga haka mukayi
sallama tare da alkawarin idan yaje gidan zai
kirani mu gaisa da Mamma.
Ai kuwa ko awa biyu ba'ayi ba yayi kirana,na hau
bud'a karshe na saki dariya. Nayi mamaki dana ji
muryar Mamma a sanyaye har na tambayeta ko
bata farinciki da auren nan? Bata bani amsa ba
ta share da tambayar lafiyata. Nace
alhamdulillah,tace zan cigaba da karatune? Na
tabe baki "Bansani ba Mamma." "Kamar ya baki
sani ba Tasleem? Keda mahaifinki? Kije kiyi mishi
magana tun lokaci bai kure maki ba."
Na amsa da toh saidai kuma abunda Mamma
batasani ba shine,idan har sai naje ga Abba na
gwammace nayita zama haka a gidan. Haka
mukayi sallama da ita.
Bayan kwana biyu,Meena matar Yaya Usman ta
haife tsohon cikinta ta samu d'iya mace. Murna a
wajen yan gidan ba'a magana. Nikam ko ajikina
daman ba wani mutuncinsu nake gani ba.
*******
Bayan kwana uku da haihuwar meena,misalin
biyar na yamma,ina zaune a bakin firij na Raliya
ina gogewa,ita kuwa da yaranta suna falon suna
kallon wasan Hausa saidai ko inda suke bana
kalla ballantana film din da suke kallo ya dauki
hankalina don tun fil'azal fina finan hausa ba
burgeni sukeyi ba barni da da kallon Indian series
da Korea anan kam ko makiyina ke kallo zan saci
kallo. Sallamar Usman ta katsesu,Hamid bai
amsa ba saima ya mike ya fice saboda a yanzu
haushinsa yakeji akaina. Bayan su hamida sun
gaisheshi ya dubi Raliya.
"Wa kike ganin ya dace ta zauna wajen Meena
ne?"
Yayi maganar tamkar da sa'arsa,Raliya bata ko
damu ba ta kyabe baki
"A'a toh,ko Dijangala ai sai ta zauna. Idan kuwa
batason aikinta ga waccan tsiyar saiku kwasa."
Sai lokacin na dubeta kafin na watsawa Usman
mugun kallo wanda na jima banyi mishi irinsa ba.
Murmushi yayi ya dubi Raliya
"A'a dijangala shiririta ne da ita,tunda dai ga
gwaggon meena zata dunga yi musu wanka sai
Tasleem ta dunga gyare gyarem gidan."
Raliya bata musa ba domin duk yanda zan
kuntata a rayuwa shi tafi kauna. Tace
"Hakan ma yayi,ke! Idan kin kammala ki tattaro
kayanki ki koma gidan Usman har sai matarsa ta
gama wanka sannan zaki dawo."
Bance uffan ba don bakin ciki,a matukar fusata ta
kammala aikin na mike na shiga daki. Haka na
tattaro kayan na fito. Hamida mukayi arba da ita
ta tuntsire da dariya gami da yimin gwalo"Haka
zaki k'are." Kamar nace mata wani abu saidai na
fasa nayi gaba,Raliya har lokacin tana falon
banko kalleta ba nayi gaba abina a fusace.
Saida nazo daidai garden na zube anan na fashe
da kuka,wai haka rayuwata zata k'are? Wane irin
uba gareni da bai daukeni komai ba? Ya manta
da ya haifeni ne har ya banzatar dani a gidansa
ya maidani wofi? Ace yan aiki ma sun fini daraja
da kima a gidannan? Na daga kaina nakai duba
da d'an lilon da muka saba wasa da Yayana.
Haka zaiyita cillani yana goyani muna zagaye
garden dinnan muna dariya. Ba zato naji an
dafani ta baya,nayi azamar juyowa ganin Usman
bansan lokacin da naja tsaki ba nayi kokarin
mikewa yayi saurin dawowa ta gabana.
"Haba Tasleem,ashe tsanar da kika yimin har
takai ace kije ki taimakawa matata ki zauna kina
kuka? Duk cikinmu waye mai tausayinki bayan
ni? Haba Tasleem,banji dadi ba wallahi."
Ganin yanayin fuskarsa sai naga kamar ban
kyauta ba,nace
"Ni ba gidanka ko matarka na tsana ba ai,irin
wannan rainin hankalin da akeyimin a gidan
ubana ne na kasa gane dalilinsa. Bansan kuma
me na tsarewa mutane ba."
Na karashe cikin tsiwa,yayi dariya ya kawo hannu
zai dora kan lebbana nayi azamar ja da baya,cikin
tsoron yanayin kallon da yakemin
"Tasleem komai naki abun sha'awa ne wallahi. Ni
bana k'inki,inason ganin kanwata a kusa dani
shine ma dalilin da yasa na nemi alfarmar
zuwanki. Kiyi hakuri inajin dadin yanda kika kware
a gyara muhalli. Meena KAZAMAR GIDA ce,
banason ganin gidan nan da kazanta. Don Allah
kanwata wallahi tana yin arba'in I promise you
zaki komo gida."
Bance komai ba na mike na dauki jakata nayi
gaba yana magana ko juyowa banyi,menene
saukin da nan da can din?
****
Baby ta numfasa,hawayenta ya karu wani yana
bin wani. Haris ya miko mata (handkerchief)
dinsa,tasa hannu ta karb'a saidai bata da niyyar
share hawayen. Ta dubi Haris wanda shima ya
gaji da waigenta ya karkato gaba daya yana
duban fuskarta don jin dadin hirar.
"Haris a wannan zuwan nawa ne gidan Usman
komai na rayuwata ya soma tabarbarewa. Yanda
akayi kuwa shine......."