← Book details Yar Bariki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 38

Sashe 21

Yar Bariki Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Wanki kuwa babu ranar da hannuna baya taba ruwa,hakanan daidai da undies din Meena ni nake aikin wanke mata su. Sau daya na taba gigin yi mata musu akan wankin ta jibgeni ba tare da kowa yayi yunkurin cetona ba. Hakanan nayi jinyata na warke domin alokacin Usman baya garin yaje daurin auren abokinsa a Zaria kamar yanda ya shaidamin.

Bakar ranar da bazan mance ba itace ranar da babu kowa a sashen usman sai ni. Gwaggo ta raka meena asibiti don allurar da zata kai Ummi,ina zaune a falo zaune kan kujera ina hutawa sanin da nayi matar gidan batanan balle kuma ta gani tunda dai ta rigaya ta sanyamin dokar hawa kujerunta nikam gajiya da aikin dana kammala yasa na shimfide saman kujerar ina kallon tashar Zeeworld da suke hasko series dinnan na Destiny wanda an riga anyimin nisa sakamakon jimawa da nayi ban kalla ba. Yawo naji wani abu kamar hannu yana yimin a kunnena nayi azamar mikewa zaune don ba karamin firgita nayi ba. Ganin Usman yasa nayi murmushi kadan ban kawo komai a raina ba na gaisheshi hade da tambayar
"Yaushe ka shigo?"

Wani kallo yake watsomin,hakan yasa cike da mamaki na dubi shigar dake jikina naga babu inda na kuskuro da shigar banza. Na kara dubansa "Lafiya dai baban ummi?"

Ya basar yana mai mikewa tsaye da dariya

"Lafiyar kenan Kanwata,kallonki nakeyi ina tausayawa rayuwarki. Ace ke kam baki da wani hutu sai masu gidan basunan kike da yancin sakewa tamkar ba gidan mahaifinki ba?"

Nayi murmushi ina mai jin dadin yanda Usman ke nuna damuwarsa akaina,alokacin na ayyana cewar ko na manta kowa bazan mance kaunar da Usman ya nunamin ba alokacin da dukkan gidan suka juyamin baya.

"Ayya,bakomai Baban ummi wataran sai labari fa."

Yayi dariya yace "Hakane kanwata,kiyi kallo abinki domin kuwa ina maki albishir cewar matar gidan bazata shigo yanzu ba don zata biya ta gidansu." Naji wani sanyin dadi shi kuwa yayo hanyar dakinsa na maida kaina ga kallo. Jimawa kadan ya fito ya shiga kicin bayan ya chanja suturar jikinsa zuwa doguwar jallabiya. Ban damu da sanin abunda zai aikata a kicin ba,a cewata ma,ai gwara kada ya matsamin ya barni na dan huta kafin hakimar tasa ta dawo. Hankalina ya nutsa sosai ga kallo saidai naji alamar ajiye kwalin a kusa dani. Hakan yasa na juyo na dubeshi,murmushi ya sakarmin yana kurbar lemon kwalin na Chi exotic dake hamnunsa,yayimin nuni da ido ga lemon da yake ajiye akan tebur kusa dani.

"Bismillah kina kallona,nasan rowa irin ta Meena bazaisa ta baki damar daukar abun sha ba. Bari na dan kwanta kafin nan da la'asar." Ya mike ya shige daki,nayi murmushi don nasan gaskiya ya fada. Meena rowan tsiya ne da ita,koda bak'i tayi sai sun nemi ruwa sannan ake basu balle akaima ga lemo. Na dubi kwalin lemun ina tunanin yaushe ma rabona dana samu yancin shan lemun kwali duk da a baya katon katon babu irin wanda Abba baya ajiyewa Mamma. Na dauka na bude na sha sosai,inayi ina kallo. Tsayawa nayi cak yayinda kaina yayimin nauyi,na ajiye kwalin lemun na dafe kaina ina mai runtse ido. A hankali na soma fita hayyacina,tun ina jiyo muryoyin dake fitowa a tv har dai na daina ji da ganin komai."

*****
Baby ta dakata tana mai sheshshekar kuka sosai,Haris cike da tausayawa ya daure yace

"Kiyi hakuri Tasleem."

Kamar bazatayi shiru ba,har ta soma rikita mishi tunani don hakikanin gaskiya ya tsani kukan mace. Dakyar ta nutsu ta goge fuskarta da (handkerchief) din daya bata. Kafin ta zubamishi jajayen idanunta wadanda sukayi kusan kwana uku suna zubar da ruwan hawaye.[2/3, 21:29] Rufy: 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(35) "Haris a wannan ranar Usman ya ketamin haddina.
Yayi amfani dani ba a hayyacina ba." Ta numfasa kafin
ta cigaba "Baccin nan bai sakeni ba sai wajen magriba.
Nayi mamakin irin radadin da naji a gabana. Na yunkura
da zummar mikewa daga shimfidar da nake kwana na
katifa a karamin dakin yar aikin meena wacce zuwana
yasa ta koma sashen raliya da aiki,saidai ko kalilan ban
iya motsawa ba. Kawai sai na fashe da matsanancin
kuka,a hankali kuma tunanina ya dawo da lemun dana
sha hakanan cikin magagin bacci na hango fuskar
Usman lokacin daya kwasheni zuwa dakina. Nayi
azamar duba pant dina,jinin dana gani ba karamin
dagamin hankali yayi ba. Ihu nasa hadi da fashewa da
kuka. Yayi daidai da shigowar Meena da Gwaggonta,wuf
suka fado dakin. Meena na fadin "Wane irin iskancin
banza ne zaki...." Sauran maganarta ta makale ganin
halin da nake ciki,gwaggo ta matso tana buga salati
"Mun shiga uku,Aminatu kinga abunda nake gani? Yau
tsinanniyar nan ta janyo mana abun magana." Meena ta
dubi Gwaggo tace"Wa?! Wallahi badai dani ba! Kanta ta
janyowa,karuwae banza da wofi. Bazaki janyomin zagin
mutane ba." Daga haka ta hau buguna kamar Allah Ya
aikota. Ihu nakeyi ina kuka kakkarfa saboda radadin
daya hademin biyu. Ta sakeni tayi wuf ta fita ina nan
zaune ina jan jikina zan shiga bandaki ta dawo rike da
bokiti,kafin na ankara ta gwalemin kafafuna ta
watsamin. Ai bansan sadda na saki razananniyar k'ara
ba saboda azabar ruwan zafin nan,daga haka na sume.
Ban farka ba sai a gadon asibiti. Nayi mamakin ganin
har da Abba cikin wadanda ke tsaye a kaina,sai Raliya
da kuma Gwaggon Meena. Na dubesu daya daya kafin
na maida dubana ga Abba cikin matsanancin tsanarsa.
Dukkansu babu masoyina ciki,makiyana ne. Bansan me
suka kawoni ayimin ba bayan sun rigaya sun gama da
rayuwata,inama ace sun barni na karasa rayuwata
anan. Na kauda kaina ina mai jin saukin radadin azabar
da nakeji a gabana bansani ba ashe wai har dinki
akayimin. "Munafuka,ke juya keyarki mana kin jawo
mana zagin mutanen gari. Haba Tasleem,me muka
rageki dashi da har sai kinje ga bibiyar yan iskan gari?
Har nawa suka baki kika basu kanki? Tir!" Cewar Raliya
tana matsar kwallar munafunci. Bance uffan ba,jira
nake naji abunda zai fito daga bakin Abba saidai baice
komai ba fuskarsa cike da bacin rai ya nufi hanyar
ficewa. "A'a Doctor ina zakaje kuma?" Cikin takaici ya
fice baiko k'ara kallonmu ba. Yana fita itama Gwaggon
Meena tace zata koma gida don ba aikin kula dani ya
kawota gidan ba. Bayan fitarta Raliya ta tuntsire da
dariya harda hawaye,idona na runtse inaji kamar na
mike na janyota na d'irka. Naji maganarta daf dani
"Usman ya biyani! Da ace tun farko nasan kudurin nan
yayi a kanki da tuni na bashi goyon baya hakanan da
banji bacin ran kulaki da ya dungayi ba. Ki godewa
Allah ma da abun ya tsaya a iya nan. Na tsaneki! Na
tsani uwarki da dukkan tsatsonta! Nafison ganina da ya
yana kadai a gidan ubanki.! Sai kiyi jinyar kanki!" Ta
kara tuntsirewa da dariya ta juya zata fita, wallahi
bansan lokacin dana fisgota ba na janyo almakashin
dake ajiye cikin tasa a gefen kaina. Saitin wuyanta na
sanya kafin na soma magana a fusace "Kina zaton kinci
galabar abunda kikayimin ko? Toh wallahi ki ajiye a
ranki saina dauki fansa akan Usman! Sai ya gane shayi
ma ruwa ne RALIYA! Don ina shanye dukkan wahalhalun
da kuke sanyani ba wai hakan yana nufin tsoronku
nakeji ba! Kawai dai biyayya nakeyi ga MAHAIFIYATA!
Wallahi ko ba dade ko ba jima sai na dauki FANSA.!" Na
wuncikalar da ita,na ajiye almakashin,a fusace tayo
kaina wanda hakan yayi daidai da shigowar nos. Ba don
taso ba ta bini da mugun kallo,na tabbata tayi mamakin
karfin hali irin nawa,da shekarunta da komai nayi mata
haka? Hum, bari dai akai mutum bango Haris, wani
abun da bai taba zaton zai aikata ba sai ya aikatashi.
Kwanana uku a asibitin Abba,wata nos me mutunci ke
kula da lafiyata bansani ba ko bisa umarnin Abban ne
kodai a'a. Ni nake lallabawa nayi wankana nasa sutura.
A rana ta hud'u ne ina zaune ina shan lemun b'awo naji
sallamar wanda banyi tsammanin ganinsa nan kusa ba.
YAYA ABDULLAH. Gaba daya ya chanja yayi
haske,saidai fa ya rame akan yanda naga hotonsa
kwanakin baya. Sanye yake da shirt da wandon jeans
bak'i ya dora brown jacket a samanta. Farin cikin
ganinsa ya koma ciki sakamakon yanayin dana gani a
fuskarsa. Kallon da yakeyimin ba karamin kad'amin 'yan
hanji sukayi ba. Salati na shigayi a zuci kafin na
russunar da kaina sai hawaye.......
Chapter 21 · 0% Book details