← Book details Yar Bariki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 38

Sashe 20

Yar Bariki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(33)
Kwana uku da yin candy dinmu,Abba ya dawo
daga tafiya hakanan Hamid shima ya dawo
daga makaranta anyi musu hutu. Zuciya irin
tawa ta hanani tunkarar Abba da zancen zuwa
Kazaure. Sai ince rabona da sanya Abba a ido
tun sadda yayi kirana yayimin batun komawa
sashen Raliya da zama.
Wataranar asabar ina gugar falon Raliya,ina yi
ina wake wakena wanda yana daya daga cikin
abunda ke konawa Raliya rai ganin bana nuna
damuwa a dukkan ayyukan da take sanyani.
Saidai batasan cewar kawai dannewa nakeyi
amma ji nakeyi kamar na shak'ota don bakin
ciki. Hamid ne ya shigo da takalmi ya bi ta inda
na taka zuwa bakin firij,na kalli yanda wajen ya
b'aci da k'asa bance komai ba na k'ara
gogewa,yazo ya kara wuce hannunsa rike da
lemon b'awo yana sha yana yarda kwallayen
nan ma bance uffan ba don na lura tsokanar
fad'a yakeyi. Saida nazo daf da kammalawa ya
kara tahowa zai shige. Ai kuwa na sanya mop
din na hankad'e kafafuwansa tuni ya zube a
wajen,banyi sanya ba na kara dauka na kwala
mishi a goshi. Ihun daya fasa yayi daidai da
shigowar Hamza da Usman da Nura. Tsayawa
nayi ina huci da fada"Wallahi gobe ma ka k'ara
gigin b'atamin aikina sai nayi maka abunda
yafi wannan haka kawai..."
Hannu Hamza ya daga da niyyar kwad'eni ga
mamakina Usman ya rikeshi,bani kadai ba
dukkansu suma sunyi mamaki hatta da Raliya
dasu Hamida da suka fito.
"Kana da hankali kuwa? Sakarmin hannu!"
Usman shima yace"Meyasa kake da son kaine
Hamza?(Kasancewar raini ya shiga tsakaninsu
bama kadan ba) Baka ganin laifin na dan
banzan yaron nan ne da har zakayi gigin marin
Tasleem? Wannan ma ai son kaine."
Ya saki hannunsa,ya dubeni
"Ke wuce ki tafi."
Na dauki mop da robar zan fita,Nura ya
dakamin tsawar data firgitani,ya iso ya janyo
rigata wannan yasa na fadi na zubda ruwan,ba
karamin buguwa k'uguna yayi ba. Kukana ya
tsaya sa'ilin da Usman ya daga hannu ya mari
Nura. Dakin yayi dif,ya cakumi wuyansa
"Wallahi ka kara gangancin taba lafiyarta saika
raina kanka! Metayi maka?!"
Nura ya fisge hannun Usman daga wuyansa
"Nika mara akan wannan yar iskar?"
"An mareka!!"
Nura yayi kwafa ya fice a fusace.
"Hamza bimin bayansa kada ka bari ya dawo
nan." Cewar Raliya sanin halin dabancin Nura
don ba karamin aikinsa bane ya dawo da wuka
ko wani makamin. Hamza ba musu ya fice.
Raliya ta dawo gaban Usman
"Meke yawo a kwakwalwarka?! Akan wannan
yar iskar ka daki kaninka abunda baka tabayi
ba shekara da shekaru sai yanzu da girmanku
da komai?! Me ta baka kaci?!"
Bai saurareta ba ya dawo gabana ya dagani
"Sannu Tasleem,tafi zansa a goge."
"Uban wa zakasa aikin? Wallahi kaji na rantse
maka idan baka fita harkar shegiyar nan ba
ranka zai mummunan baci. Dawo ki gogemin
waje!"
Ta dakamin tsawa,ina hawaye na sunkuya
dakyar zan dauki robar saboda zafin buguwar
da nayi saidai Usman ya rigani ya dauka ya
mikomin.
"Kiyi a hankali."
Raliya ta sanyashi ficewa na lura baiso hakan
ba,haka nayi aikin nan ina mamakin abunda ya
faru.

Tun daga wannan ranar kuma sai na soma
sakewa Usman kadan kadan,nakan gaisheshi
hakanan nakan je dukkan wani aiken da
zaiyimin zuwa gidansa ko kicin din Raliya da
sauransu. Ban dai sakarmishi sosai ba,amma
babu wannan rainin sosai. Har kuwa zuwa
lokacin bai rabu da fita yawon dare ba. Nasha
ganin Meena tazo wajen Raliya tana bala'i
akan ita ta soma gajiya da bin mata irin na
Usman,mutum tamkar wanda aka yiwa asiri.
Raliya saidai ta bata hakuri don babu laifi
iyayen meena akwai naira hakanan takan
lasawa Raliya sosai domin ita din macece
wacce bata godiya ga Allah. Duk da irin arzikin
da ta hau kai tayi zaune na Abba,ga kuma
business da takeyi,hakan bai hanata hangen
na wasu ba.
Bayan watanni uku,lokacin Mamma ta kusa
shekara a gidansu,kawai na tsinci wayar Yaya
musty yana yimin albishir cewar an daurawa
Mammana aure da wani almajirin Malam. Har
tsalle nayi don murna. Yara da yawa sukanyi
bakin ciki idan uwarsu zatayi wani auren
alhalin ubansu na raye, kai koda ace baya raye
akwai yaran dake taya ubansu kishi amma
nikam baruwana ko a jikina. Daga dariya kuma
sai na fashe da kuka. Ina cewa shine ko a
gayamin nazo da wuri? Dariya yayi yace kada
na damu anan Kazaure Mamma zata zauna
duk sanda naga dama na tambayi Abba ya
barni toh nazo na ganta. Naji dadi kwarai ya
kara tambayata game da Yaya abdullah nace
mishi sauran mishi watanni uku kawai ya dawo.
Daga haka mukayi sallama tare da alkawarin
idan yaje gidan zai kirani mu gaisa da Mamma.
Ai kuwa ko awa biyu ba'ayi ba yayi kirana,na
hau bud'a karshe na saki dariya. Nayi mamaki
dana ji muryar Mamma a sanyaye har na
tambayeta ko bata farinciki da auren nan? Bata
bani amsa ba ta share da tambayar lafiyata.
Nace alhamdulillah,tace zan cigaba da
karatune? Na tabe baki "Bansani ba Mamma."
"Kamar ya baki sani ba Tasleem? Keda
mahaifinki? Kije kiyi mishi magana tun lokaci
bai kure maki ba."
Na amsa da toh saidai kuma abunda Mamma
batasani ba shine,idan har sai naje ga Abba na
gwammace nayita zama haka a gidan. Haka
mukayi sallama da ita.
Bayan kwana biyu,Meena matar Yaya Usman
ta haife tsohon cikinta ta samu d'iya mace.
Murna a wajen yan gidan ba'a magana. Nikam
ko ajikina daman ba wani mutuncinsu nake
gani ba.
*******
Bayan kwana uku da haihuwar meena,misalin
biyar na yamma,ina zaune a bakin firij na
Raliya ina gogewa,ita kuwa da yaranta suna
falon suna kallon wasan Hausa saidai ko inda
suke bana kalla ballantana film din da suke
kallo ya dauki hankalina don tun fil'azal fina
finan hausa ba burgeni sukeyi ba barni da da
kallon Indian series da Korea anan kam ko
makiyina ke kallo zan saci kallo. Sallamar
Usman ta katsesu,Hamid bai amsa ba saima
ya mike ya fice saboda a yanzu haushinsa
yakeji akaina. Bayan su hamida sun gaisheshi
ya dubi Raliya.
"Wa kike ganin ya dace ta zauna wajen Meena
ne?"
Yayi maganar tamkar da sa'arsa,Raliya bata ko
damu ba ta kyabe baki
"A'a toh,ko Dijangala ai sai ta zauna. Idan
kuwa batason aikinta ga waccan tsiyar saiku
kwasa."
Sai lokacin na dubeta kafin na watsawa Usman
mugun kallo wanda na jima banyi mishi irinsa
ba. Murmushi yayi ya dubi Raliya
"A'a dijangala shiririta ne da ita,tunda dai ga
gwaggon meena zata dunga yi musu wanka
sai Tasleem ta dunga gyare gyarem gidan."
Raliya bata musa ba domin duk yanda zan
kuntata a rayuwa shi tafi kauna. Tace
"Hakan ma yayi,ke! Idan kin kammala ki tattaro
kayanki ki koma gidan Usman har sai matarsa
ta gama wanka sannan zaki dawo."
Bance uffan ba don bakin ciki,a matukar fusata
ta kammala aikin na mike na shiga daki. Haka
na tattaro kayan na fito. Hamida mukayi arba
da ita ta tuntsire da dariya gami da yimin
gwalo"Haka zaki k'are." Kamar nace mata wani
abu saidai na fasa nayi gaba,Raliya har lokacin
tana falon banko kalleta ba nayi gaba abina a
fusace.
Saida nazo daidai garden na zube anan na
fashe da kuka,wai haka rayuwata zata k'are?
Wane irin uba gareni da bai daukeni komai ba?
Ya manta da ya haifeni ne har ya banzatar dani
a gidansa ya maidani wofi? Ace yan aiki ma
sun fini daraja da kima a gidannan? Na daga
kaina nakai duba da d'an lilon da muka saba
wasa da Yayana. Haka zaiyita cillani yana
goyani muna zagaye garden dinnan muna
dariya. Ba zato naji an dafani ta baya,nayi
azamar juyowa ganin Usman bansan lokacin
da naja tsaki ba nayi kokarin mikewa yayi
saurin dawowa ta gabana.
"Haba Tasleem,ashe tsanar da kika yimin har
takai ace kije ki taimakawa matata ki zauna
kina kuka? Duk cikinmu waye mai tausayinki
bayan ni? Haba Tasleem,banji dadi ba wallahi."
Ganin yanayin fuskarsa sai naga kamar ban
kyauta ba,nace
"Ni ba gidanka ko matarka na tsana ba ai,irin
wannan rainin hankalin da akeyimin a gidan
ubana ne na kasa gane dalilinsa. Bansan kuma
me na tsarewa mutane ba."
Na karashe cikin tsiwa,yayi dariya ya kawo
hannu zai dora kan lebbana nayi azamar ja da
baya,cikin tsoron yanayin kallon da yakemin
"Tasleem komai naki abun sha'awa ne wallahi.
Ni bana k'inki,inason ganin kanwata a kusa
dani shine ma dalilin da yasa na nemi alfarmar
zuwanki. Kiyi hakuri inajin dadin yanda kika
kware a gyara muhalli. Meena KAZAMAR GIDA
ce, banason ganin gidan nan da kazanta. Don
Allah kanwata wallahi tana yin arba'in I
promise you zaki komo gida."
Bance komai ba na mike na dauki jakata nayi
gaba yana magana ko juyowa banyi,menene
saukin da nan da can din?
****
Baby ta numfasa,hawayenta ya karu wani yana
bin wani. Haris ya miko mata (handkerchief)
dinsa,tasa hannu ta karb'a saidai bata da
niyyar share hawayen. Ta dubi Haris wanda
shima ya gaji da waigenta ya karkato gaba
daya yana duban fuskarta don jin dadin hirar.
"Haris a wannan zuwan nawa ne gidan Usman
komai na rayuwata ya soma tabarbarewa.
Yanda akayi kuwa shine......."
'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(34)

"Usman ya dunga jana a jiki da wasa da dariya musamman idan ba idon matarsa a wajen. Tun ina daure masa har dai na hakikance dagaske tausayina yakeji kuma kauna ta don Allah yakemin. Hakan ya zamana na amince cewar bashi da wata manufa akaina. Yaya Abdullah kuwa munfi sati lokacin bamuyi magana dashi ba don bana samun kudin da zan sayi data,hakanan shima bansan meya hanashi kirana ba.

Wahala iri iri babu banayi a hannu meena,ni ce kula da jaririyarta da taci sunan uwar meena wato Sadiya suke kiranta da Ummi. A farko Usman so yayi ya sanya sunan mahaifiyarsa saidai ta murje idanunta tace sam bazata amince ba,UWA TAFI UWA don haka saidai a sanya sunan nata uwar. Haka dai Usman ya goyi bayanta,dayake itama Raliyar irin dukiyar da ake kawowa Meena daga gidansu a matsayinta na wacce ta haifi jikar fari ya hargitsa mata kai tace bakomai abi tsarin da Meena da takeso.
Chapter 20 · 0% Book details