← Book details Yar Bariki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 38

Sashe 26

Yar Bariki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Wallahi baka b'atamin ba Haris. Asalima burgeni kayi,dadi nakeji a kasan zuciyata. Tunda na soma harkar barikanci,babu wanda ya taba yunkurin gayamin gaskiya saikai. Tun farko haduwarmu saida na fahimci kai din daban kake. Ban kara sakankancewa da lamuranka ba saida na hadu dakai a karo na biyu. Tabbas Haris kai mutumin kirki ne wannan ne yasa nayi mamakin yanda ustaz ya iya aminta da mutum irin Kb."

Murmushi Haris yayi ya numfasa ya gyara zama kafin ya dubeta

"Muna iya tafiya gaida Mamma?"

Ta lumshe ido tana murmushi

"Da gudu ma."

Sukayi dariya kafin Haris ya mika mata ruwan roba daya siya zai sha

"Oya,ga wannan sauka ki wanke fuskar nan taki, ki d'anyi kwalliyar nan taki bebinsu."

Harararsa tayi a wasance,kafin ta narkar da fuska

"Au ba taka bace?"

Ya dubeta kafin ya basar da zancen ta hanyar fitowa ya bud'e b'angarenta ya amshi robar ruwan,yana kokarin budewa yace

"Juyo ki wanke fuskarki."

Ba musu ta gyara ta mika hannunta na hagu,yana zuba mata tana wankewa har fuskarnan tayi fayau,Baby ta gasken ta bayyana sannan ya zagayo ya bude boot ya dauko mata handbag dinta ya shigo motar kafin ya dire mata a cinya yana murmushi

"Ayi make up please."

Murmushin tayi kafin yayi addu'a ya daga gilasan ya kunna Ac,ya sanyamusu karatun al-kur'ani don kara nutsar da zuciyar Tasleem daga bisani yaja motar suka dauki hanyar Kazaure. Ita kuwa ta hau fente kyakkyawar fuskarta da kwalliya saidai bamai yawa ba. Bayan ta kammala ta dubeshi

"Baka sanar dani abunda zai kaika garinmu ba?"

Dam! Gaban Haris ya buga. Shaf ya mance da ainahin silar zuwansa Kazaure sai yanzu da Tasleem tayi tambayar. Ashe fa wai matar aure zaije zab'a.

"Kayu shiru??"

'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(42)

Ya dan dubeta,ya rigaya ya gama tabbatarwa kansa cewar baby kyakkyawa ce ta gani a fada,tabbas baiga laifi ga KB dake makale mata ba domin kuwa idan zaka biyewa kyawun halitta da surarta,bakasan sadda zaka fada tarkonta ba. Yayi murmushi kafin yace "Garin iyayena ne."

Ta fiddo ido kadan fuskarta ta washe "Haba? Ashe kaima dan garinmu ne? No wonder na ganka da kyau kamar aljani."

Kallonta kawai yayi ya sakar mata murmushin da saida ta jishi har tsakar kanta. Tasan tun haduwarsu ta farko,tana jin wani al'amari bak'o game da Haris,saidai ita kanta tasan Haris yafi karfinta. Me zaiyi da 'YAR BARIKI? Ta maida kanta ta kwantar tana sauraron karatun Al-Kur'ani mai girma. Shi din ma kogin tunanin ya fad'a. Anya bai fada tarkon son 'YAR BARIKI ba? "A'a ban fada ba,just ina girmamata ne a matsayinta na wacce ke bukatar taimako. Ina kuma tausayawa rayuwarta."

Ya fadi a ransa.

*******
Hankalinsa a tashe,nutsuwa tak'i samun mazauni a kwakwalwarsa da jikinsa. Yana zaune sai afkin kiraye kirayen waya yake. Daga ya kira Manal,sai ya koma Dalal kafin a karshe yaji ta bakin Hibba. Momy ma ya kirata sau d'aya saidai ita kanta bata da labarin duniyar da Baby ta shiga. Zuciyarsa tayi bak'i har hasko Baby yakeyi kwance a kirjin wani da namijin. Kishi matsananci wanda har ya janyo sauyawar kalar kwayar idonsa.

Tun tsawon daren jiya take lura da mijin nata, hakanan ko lokacin daya fidda kunya ko shayi yake waya a gabanta duk tana sauraronsa,hankalinta ya tashi jin cewar mace ce ta rikita Kabir har haka. Ta soma sharar kwallah saidai gogan baisan tana yi ba,kwata kwata ma baisan da wanzuwarta ba sai sambatu yakeyi a fili

"Ina kikaje? Wane dan iskan kika samu har kika kashe wayoyinki Babyna?"

Ire iren abunda yake fadi kenan. Maganarta ta katseshi

"Wacece haka prince?"

Ya dubeta,gaba daya baisan da ita ba a falon. Tsaki yaja ya mike ya dauki wayoyinsa zai shiga d'aki

"Yanzu akan wata 'yar iska kake..."

Fisgota da yayi ne a fusace ya sanya sauran maganar makalewa a fatar bakinta. Ya hau jijjigata cikin tsawa yace

"Koda wasa kika kuskura kika k'ara kiran Babyna yar iska wallahi Yasmeen saikin raina kanki."

Ta fisge jikinta tana hawaye itama a fusace tace

"An fad'a d'in! Yar iska! Yar bariki..."

Tass! Ya kwasheta da mari,kafin ya hankadata ta bugi bango ya nunota da yatsa

"Wannan kadan kika gani! Wallahi akan Baby zan iya rabuwa dake Yasmeen! Sannan ki ajiye a ranki! Baby saita shigo gidan nan matsayin matata!"

Ya kwashi wayoyinsa da suka tarwatse a k'asa yayi daki ya buga kofar a fusace. Yasmeen ta tsorata ainun,mikewa tayi ta nufi dakinta. Mayafinta da fos na kudadenta ta dauka,ta sab'i diyarta Nasreen dake bacci tayi waje. Ta rantse yau bazata kwana Abuja ba kuma ma a gidan mutum irin Kb. Maigadi yana tambayarta ko lafiya ta dakamishi tsawa "Budemin kawai!" Yayi mamaki don baisan Hajiyar tasu da haka ba,akwai ta da girmama na gaba da ita komin kankantar matsayinsa. Mace mai hankali da tunani,ga fara'a da hakuri. Ba musu ya bude a hanzarce ta sanya kai ta fita tana zubar hawaye. Yau kam sai KANO......!

****
Karfe uku da mintuna na rana sai gasu a Kazaure. Gaba daya garin ya chanjawa Baby harma ta kasa sanin ta yanda zata soma kwatantawa Haris gidansu. Ga mamakinta taga yana ta shiga wurare bai tsaya ko'ina ba sai kofar gidan Liman. Tabbas gidan kakan nata ma yaso ya sauya mata sakamakon fenti da shukoki da aka k'ara mishi. Ta tsaya cak tana kallon tsohon dake zaune akan tabarma tare da makwaftansa suna hira,saidai suma hankalinsu ya dawo kan motar. Fitowar wata yarinya karama ce ta basu mamaki,tamkar an tsaga kara an karya ita da Baby saboda tsananin kamar da sukayi,tana wani yanga irin ta kananun yara masu iyayi ta isa ga tsoffinan ta zauna saman cinyar tsohon nan. Haris da Baby suka dubi juna,ganin hawaye a fuskar Baby da kuma murmushi yasa ya girgiza mata kai. Ta kwashesu da hannunta

"Haris kayimin abunda har abada bazan mance dakai ba. Ka samu babban gurbi cikin zuciyata. Ina jinka sosai a jinin jikina kana yawo akowane sassa na jikina. Wallahi banajin zan taba mancewa da abunda kayimin. Nagode sosai."

Yaji maganganunta har cikin k'ok'on ransa,ya kasa dauke idanunsa daga kanta. Ya rasa me yakeji game da ita,ji yakeyi tamkar kada su rabu. Inama zasu shekara a haka bayajin zai damu. Murmushin nan nata wanda yake tayar mishi da tsikar jiki ta k'ara yi mishi.

"Fito muje,gaskiya ka bari ka huta saika karasa gida."

Ya girgiza mata kai ya saki lallausan murmushi idanunsa a kanta

"No,ki bari zan shigo anjima kinsan gobe fa zan tafi. Zanzo mu gaisa sai na kaiki ku gaisa da Kakannina."

Ta marairaice fuska,kwalla ta ciko idonta

"Gobe zaka tafi ka barni Haris?"

Maganar ta shigeshi,yana kara jin zuciyarsa na shiga wani yanayi. Kwankwansa gilashin da akayi ne ya maido hankulansu ga wajen,Haris ya sauke gilas kasancewar gilasan daga wajenm akwai duhu. Dan saurayi ne,yana murmushi yace

"Malam tambaya kukeyi ne?"

Haris ya girgiza kai,baby ta sanya dariya

"Baharu." Ta fada kafin ta fito,da gudu gudu ta isa ga Kakanta wanda da alama shi kam ya ganeta. Domin gaba daya ya mike yana farin cikin ganinta sosai,ta rungumeshi kafin kuma su zauna ta saki kukan farin ciki. Zuciyar Haris tayi babu dadi,ba abunda ya tsana sama da kukan nan. Dolensa ya bude motar ya fito suka gaisa da wanda ta kira da Baharu.....!
'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(44)

"Tasleem,kukan na menene kuma? Me ya samu hannun naki?"

Ta share fuskarta ganin yanayin Haris shima kamar baiji dadin ganin hawayen nata ba,ta dubi hannun kafin tace

"Buguwa ce nayi Malam,amma yanzu da sauki sosai ma."

Tsohon ya kurawa Haris ido da murmushi wanda haka halittarsa take,da wuya kaga gushewarsa akan fuskarsa.

"Yaro kana yimin yanayi da aminina Hussein."

Furucin Malam yasa Baby zubawa Haris ido kasancewar tasan Baffa Hussein sosai jefi jefi takan lek'a gidansu a baya idan tazo domin har baffa Hussein ya santa yana nuna kauna agareta har takanyi mamakin irin soyayya da shakuwar dake tsakanin wadannan bayin Allah biyu. Haris cikin murmushi yace

"Lallai ma tsohon nan,tabbas idan na koma zan fadawa Baffa ka mance da autan jikansa,Haris."

Mamaki karara ya sauka akan fuskar Baby hade da dariyar nan nata mai burgewa,haris ya daga mata gira yana murmushi. Malam kuwa hakora ya washe ya rungumo kafadar Haris yana dariya sauran tsoffi uku suna tayashi.

"Allahu,daman kaine Harisu? Haka ka girma? Lallai Harisu baku da zumunci,da ace kun yo halin iyayenku da ba haka ba. Ina d'an wajen dan auta?(Alhaji idris)"

"Yana can Abuja da zama. Kayi hakuri dan tsoho ba rashin zumunci bane,ayyuka suke rikemu acan."

Malam ya jinjina kai,baby kam murmushi takeyi,yayinda ta kasa dauke fararen idanunta akan kyakkyawar fuskar Haris wanda samun namijin daya hada komai irinsa a fannin kyau na sura da halayya abune mai matukar wuya a zamanin nan. Ya kallota,tayi azamar mikewa tsaye tana basarwa da cewa

"Bari naga kishiyoyina,don Allah dan tsoho kada ku bari yayana ya gudu tun yanzu,kunga fa ko abinci bamu ci ba."

Haris ya hararota yana murmushi,tayi mishi gwalo kadan. Malam yayi dariya

"Ai babu inda zai tafi yanzu,Baharu shigar da yayan naka dakinku yayi alwala yazo muyi sallah sai yaci abinci ko?"

Suka mike,tuni Baby tayi gaba tana fadin zata turo yaro ya shigar mata da akwatin kayanta.
*****

Tun a hanyarta take ta kiran wayoyin yayan nata amma yana ringing bai dauka ba. Taci kuka har ta koshi,ganin baya kusa yasa tayimishi dogon text inda ta gutsura mishi halin da suke ciki da KB da kuma tahowarta Kano da tayi. Daga karshe ta kashe wayarta gaba daya.

Yasmeen kenan!!

*****

Murna da hira ta karade bayan tsakanin mutanen gidan bayan da Baby tayi wanka da sallah. Tana sanye da doguwar rigar kanti. Alokacin tana zaune tana cin abinci anata hira. Makwafta sai shigowa sukeyi,Gwaggo Hajara ma nan tazo da kwanonta. Kowa yaga bandejin hannun Baby sai ya tanka,tana rufesu da fadin buguwa ce tayi. Wayoyinta kuwa har lokacin a kashe suke ta jonasu a chaji. Sallamar da akayi ta maido hankulansu,Haris ne a gaba sai Yaya musty a baya. Ganin Yaya musty yasa Baby sakin ihu ta mike ta rukunkumeshi suna dariyar farin cikin ganin juna. Gaban Haris ya shiga dukan uku uku,haka kawai ya tsinci kansa da jin haushin wannan rungumar da Baby ta yiwa wani.
Chapter 26 · 0% Book details