← Book details Tawa Ta Sameni Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 13

Sashe 13

Tawa Ta Sameni Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

yace ka da ki damu wasa ne.Patyn da aka shirya musu a Abuja nace zanzo sai yace kar nazo baya son ana kalle mishi ni,yaynmu akwai kishi. Da kyar ya bari na bisu Mami zuwa yola gurin Amira,cikina sai girma yake ko su Mama basu san ina dashi ba, tunda sanda muka je Yola bai fito ba sai a bikin Saudatu suka ganshi, Anty Yagana kece min watan sa nawa ne?nace ban sani ba suka ce banje Asibiti bane nace sai yaynmu ya iso jibi bikin saudatun ma mama na ma waya kuma ta mishi waya. Haj Yaya zaune a gaban boka tace gafarta malam so nake ka bani maganin da zamuyi amfani dashi yaron nan da yazo ya saki amaryarshi ya zauna da yar uwarshi,Boka yace ai Haj aikin gama ya gama dazu yar uwarki tazo ita da yarta sun amshi maganin da zasu kasheshi su zubar da cikin Amaryar su ci gado,Haj Yaya cikin tsoro tace kuma ka basu Malam?yace na basu ba aikin kudi bane kuma sun bani kudi sosai,Haj Yaya da tsoro da mamaki suka hanata magana can tace to ai malam ni ce mamarshi don dana ne shima, Bokan mamaki ya kamashi yace ai danki ne?tace dana ne wllh yace shine kike biye masu kuna mashi asiri lallai baki da hankali in ya mutu wanene da asara? Yarta zata auri wani kefa zaki haifi kamar shi?to aikin gama ya gama sai ki tashi in kinci sa'a basu bashi wani abinci ba ko abin sha, ki samu ki hana shi karasawa gidan ma don ko gidan ya taka sai yayi wani mummunan rashin lfy, maryar kuma in ta tsallaka kofar dakin cikin zai zube,ke kuma in kika amsa sallamar yar uwarki Haj Laure to zaki mutu, ai bata bari ya karasa ba ta tashi da gudu da gaggawa ta isa gida ta daga murya ta kira Kabir tana fadin Kabir kuna ina ynxu? Yace na dauko yaynmu ne yanzu mun isa gidanshi ta fasa ihu wayyo Kabir na shiga uku kada ku shiga gidan hannunta rike da wayan tana fadin kar ku shiga zai mutu idan kun shiga ko har kun shiga? yace eh,sai ko ta fadi sumammiya,Mama ta fito tana salati ruwa ta shafa mata, sauran kishiyoyin suna tsaye ta farko tana dubansu sai ta ganta a jikin Habiba nan ta soma kuka tana fadin ya mutu ko? Suka ce wa? tace yaynsu Haj Laure ta cuceni sannan ta fasa kuka mai karfi ,cikin kuka take masu bayani tana rufe baki sai akaga yaynmu da Kabir don har sun kunna kai cikin gidan sukayi waya da Haj don haka a rude suka shigo tana ganinsu tace ka shiga gidan? yace a'a menene? nan tayi musu bayani, tsaki yaynmu ya ja yace ai gara in mutu in huta da wannan balain,Hajiyata kin bani mamaki ya juyo ta ruko shi ina zaka? wllh ba zaka wannan gida ba yace matata can tana cikin hatsari sai in tsaya,Mama ta dube shi kar kaje itama Allah zai kareta,yace haba mmn Sagir daina wannan magana,Haj Yaya tace Kabir jeka zo da Iman gashi ance kar ta tsallaka kofar dakinta,yaynmu yana min waya ina babban kicin ya ce kizo gida ynxu ko me kike kar ki koma daki na ce cikin tsoro lfy yaynmu? yace ba kalau ba,kar fa ki shiga daki!ki jira Kabir a waje zai zo.Sai da ana kwashe komai sannan na fita cikin tsoro kun sanni da rudewa,duk muna dakin Haj Yaya tana mana bayani cikin kuka ta soma rokon Mama gafara,Mama tace dama ban rike ki ba,ta dubeni yar nan kiyi hakuri nace ba komai Haj,kamar daga sama mukaji sallamar Haj Laure ba wanda ya amsa mata,kowa yayi shiru tace Murja! Murja!! Murja!!! Sai ta sa ihu, kafin kace haka hauka tuburan,nan akayi waje da ita.can sai ga Aunty Mimi da Dady tana jina abinda ya faru sai kuka,yaynmu yace wa zakiyi ma kuka? Na sake ki tunda har kin amince ku kasheni sai a bar mana gida,Ummanki na gidanku sai kije kuyi jinya bani dana,ya amshi dady, Ni da yaynmu duk muna gida bamu koma can gidanmu ba, Haj Yaya anyi nadama tunda ynxu dakinta nake kwana, ta hanani naje dakin Mama, yaynmu dadi kamar ya kasheshi. Na fito wanka ina zaune a bakin gado ina shafa mai yaynmu ya shigo sai kallona yakeyi,yace Big gal yau fa zamu fita ina cikin takura fa masu aikin gidannan har ynxu ba su gama aikin ba duk kudin da nake turawa dan a takure nake, Na harareshi ka kara hakuri guy ina jin kunyar su Haj Yaya da Mama,yace zan tambayar maki nace kaga ina da ciki ba zan iya maka komi ba yace ai hakan ma kinfi bani sha'awa bari haj ta shigo nace a'a guy ba ruwana.... muryar Haj ta hanani karasawa tace menene naji ana cewa bari inzo?ya sosa keya yace am..in...dama zamuje unguwa ne tace ina ce yace ba nisa tayi murmushi kawai,mun fito na leka nace mama mun fita,ashe daki ya kama a Hamdala Hotel nan da nan sai gamu,lallai yaynmu yayi missing dina muna nan har tara nace mu tafi yace ina zuwa,ya fita can sai gashi da kaya niki niki ya dubeni yace duba kayane kala uku da takalma nace na menene yace siyowa nayi a waffa road don kwana uku na biya na zaro ido su mama fa da Haj? Yace karki damu ai sun san muna tare kuma tun da suka bani kesun san me zanyi ba gama cikina nan ba,nayi shiru kawai.munyi soyayya mai dadi cikin kwanakin bana zuwa ko ina gara shi in nace ina son wani abu ya kan fita nema min,ranar da mukaje gida kunya don kunya na kasa sukuni,yaynmu kam ko a jikinshi ba wanda yace ina muka je dama wayata ya kashe ta ma. Wata na biu a gida 'lokacin yaynmu ma ya tafi ' aka gama gyaran gidanmu komai na cikin gidan babana ya zuba mana, Yaynmu yazo muka koma sabon gidan karshen haduwa ya hadu,kwananmu arbain na tashi da nakuda naso kada yaynmu ya tashi amma ina da ya kaini asibiti sam yaki fita daga dakin haihuwar duk in da nace wash nan sai ya rike mun da haihuwa tazo shi da likita suna rike dani gam na sukuto yar babyna mai kama da yaynmu tamkar kwabo da kwabo. Gida aka maidani dakin Haj Yaya,naga gata ganin idona, ranar suna yarinya taci sunanta Murjanatu!sai muke ce mata Haj. Amira dasu Mami duk sunzo mana da danta Ammar, Amira da tsohon ciki.Bayan suna da sati daya yaynmu ya koma da niyar yin ritaya daga kwallo,Satinshi uku da tfy ya dawo,tsam ya rungumeni zamu kasance da juna big gal,ynxu wane abu zan fi mai da hankali a kai,nace kana da gurin sai da motoci kana da manyan stores sannan kana da gidan mai sai ka zaba.Haj ta shigo ganin muna rungume da juna tace yau naga ikon Allah kai kana da hankali? jego fa take yi ke kin zauna ya shigo maki da dan labubun jariri ta fita sai fada takeyi,nace ka gani guy na bani ya zanyi da kunya,yace dama zata koro mani ke da na huta da zaman kadaici,kai mata daya matsala ce dole na sake aure, nace dan Allah kar ka yi min haka guy yace to ba Haj tace kar ki shige min ba,nace ai a nan ne amma in mun koma gidanmu ai ka gane..na daga mishi gira yace naki wayon sai nayi amarya ya fita nace pls guy. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/? _e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347 Kasuwanci,shago babana ya bude min kan titin maf road,kayan dubai nake saida wa yaynmu ne ke sa ana kawo min don yaki naje,shi kuma kasuwanci ya amsu ta ko ina,sannan ya fada harkar siyasa abin da ya karanta, mutane suka matsa sai ya fito takarar dan majalisar jiha, ni da ban amince ba sai da kyar,cikin sa'a ya cinye, lokacin Haj Baby nada shekara,Dady ya shigo mamy kizo papanmu yace kiyi sauri nace yana ina?dady yace yana dakinshi nace ina baby haj?yace tayi bacci a falo nace muje ku kwanta bayan mun kwantar dasu daki na koma na tsuke cikin riga karama ko cibi bata kai ba gabamta igiyoyin ne dama albarkatun gasu nan a fili sai gajeran wando ya dameni na gyara kaina na sa turaruka, yana bakin gado yana duba wasu takardu yana duba na yayi jifa da takardun kan durowa ya mike tsaye sai da nazo daf dashi sai kuma na daure fuska na juya da sauri yace menene big gal?nace cikin shagwaba ba kace sai kayi aure ba?yace wasa ne big gal ba zan iya aure ba ke kadai ce na juya na rungume shi yace yawwa big gal dina zaki kashe ni da soyayya ya ja igiyar riga ta sai warware ta baya ya fada katifa nima na bishi.............Pens Uppp,cewar Auntyn mashi, Alhamdulillhi,Aunty Allah yakara Basira da Arziki, yakuma raya zuri'a,saikuma ni dana rubutamuke nakemuku fatan alkhairi,tsawon lokacin dana daukan kapin kammalashi nasan lallai na batawa wasu kamar yanda nasan nima wasu sunbatamin, saidai ta bangarena nayafemuku inna fatan kuma kuyafemin. Jinjina gareku Admins namu,Allah yabar zumunci,Allah yakara hada kawunanmu. Sakon gaisuwa ga dunbin Masoya dake min magana, inna alfahari damu,sanna Dan Allah gamasu kallona abai bai Musamman yayin da sukamin magana ban amsaba Dan Allah kusani inna sane daku, wasu lokutan abin kefin karfina, nagode Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/? _e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347

DOCUMENT CREATED BY
ZAHARADEEN SHOMAR
WHATSAPP 08168575100
Chapter 13 · 0% Book details