Sashe 6
Sauyin Lamari Part 1 Compplete Hausa Novel · about 8 min read
Baba ta fara zubawa abinci sai murmushi yake mata yana saka mata Albarka. Taso ta gaya masa kyautar da Suwaiba tayi mata, amma tasan idan ya sani bazai bari ta bayarba, zaice mata babu kyau maida kyauta. Suna cin abinci tana kallon yanda Asiya da Balaraba keta zirga-zirga da kayan abinci sashen Moha. Jiki Asiya sai uban rawa yake ta kasa nustuwa. Kai kawai Jadwah ta girgiza tana yiwa bayani bakon daya zo. In banda shirme wan nata take yiwa wannan rawar jikin kaman wani saurayi?. Wai to shi menene dashi haka da Amina ma ke sonshi?. Daga inda ta hango shi tasan ingarman namiji ne ga uban tsayi. Banda wannan bata ga komai tattare dashi ba da yake zuzuta mata.
Hmm Allah ya kyauta. D'urawa kai wahala. In bata manta ba har sark'ar ta hango a wuyan sa. Allah ya shirya mana zuri'a. Sanin tarbiyar gidan yasa bata ji komai kan sark'ar dake wuyan sa. Domin tasan dukkanin su babu tarbiya daga uwar har ya'yan. Shi yasa wani lokacin rufin asiri alheri ne ga wasu.
𝗦𝗔𝗨𝗬𝗜𝗡
𝑳𝑨𝑴𝑨𝑹𝑰.
𝔸𝘚Η𝔸𝑵𝚃Ⲩ 𐐛૦𝚅𝞔.♡︎
𝐏𝐆 6.
Yau ya kama ranan asabar, kwana biyu kenan da had'uwar ta da Moha. Tun ranan da suka had'u bata k'ara ganinsa ba. Itama kuma dama bata damu da k'ara had'uwa dashi. A gurguje ta fito sanye cikin kayan makaranta da nik'af a hannun ta tana k'ok'arin sawa tayiwa Baba sallama ta fito daga gida. Saboda saukar su dake matsowa yasa kwana biyu ake musu interview mai zafi. Tana k'ok'arin buɗe gate taji kaman ana kallonta. Da sauri ta juya inda take tunanin idon na binta. Tsaye ta hango shi bakin barandar sa sanye da bakin singlet mai yankakken hannun da bakin wando. Wuyansa irin ear pod d'innan ne na turawa da suke sawa.
Gashinsa dake jike ya d'an zubo goshin sa zuwa idon sa. Suna had'a ido taji wani irin shock ya ratsa ta tayi saurin buɗe k'ofar ta fice k'irjinta na harbawa da sauri. Tana fitowa bak'ar motar Camry ta faka gabanta Amina ta fito daga cikin motar. Da d'an mamaki ta kalli Amina tace
"Au kema wai baki tafi ba?"
"Eh shigo mu k'arasa"
Bata musa ba ta shiga motar ta zauna tana juyowa idan ta ya fad'a cikin na Junaid dake kallonta ta mirror. Da azama ta d'auke idon ta tana tunanin inda ta sanshi. Murmushi Junaid ya yi yaja motar suka bar k'ofar gidan. Har suka k'arasa gate na makaranta ,Amina da Junaid na hira ita ta kasa tankawa saboda kallon da yake mata ta mudubi. A hanzarce ta buɗe motar ta fice Amina itama ta fito da sauri tana cewa
"Wai saurin me ki ke ne? Ki tsaya mana mu tafi tare"
Batace komai ba ta juya ta shiga ⁰⁰⁰⁰makaranta Amina ta bi da sauri. Da ido Junaid ya bisu har suka shiga makarantar kafin ya ja motar yana murmushi. Tunda suka shiga aji Amina ke neman hanyar da zatayi wajen ganin ta fara kafa gwamnatin Junaid wajen Jadwah kaman yanda tayi masa alkawari, tunda ita ba waya ce da ita ba. To ko bayan da suka tashi k'arfe 11 suna fitowa suka samu Junaid jingine jikin mota yana jiransu. D'an bata rai Jadwah tayi don ta lura da take taken su shida Amina. K'ok'arin wucewa tayi ta tafi Amina tayi saurin riƙe ta ta b'ata rai
"Wai me ki ke nufi ne? Yayan nawa ne ya zama abun gudu ko me?"
Kallon Amina tayi taga yanda ta b'ata rai sosai. Ajiyar zuciya taja badan taso ba ta juya suka shiga motar. Tunda ta shiga takejin idan Junaid kanta, amma taki kallon inda yake zaune har suka k'arasa k'ofar gida. Da sauri ta fice daga motar babu ko sallama, Amina ta sauke glass tana k'ok'arin yi mata magana aka buɗe k'ofar k'aramin gate aka fito . Ido suka zubawa Moha daya fito sanye cikin k'ananan kaya. Ash d'in riga mai gajeren hannu da blue Jean's. Rigar ta kama k'irjin nan ta kwanta ko ya ya motsa sai kaga jijiyoyin hannun sa. Kar kuso kuga idon Amina yanda ya buɗe kaman wata horror. Baki hangame take kallon Moha dake tsaye bakin gate d'in hannu zube cikin aljihun wando, fuskarnan a mugun turb'une.
Ido suka had'a da Jadwah da k'irjin ta ya fara harbawa da k'arfi itama ta tamke fuska. Juyawa tayi ta kalli Amina dake kallonsa kaman wadda ta warke makanta. Dariya ta kusa kwacewa Jadwah tayi saurin danneta tana kallon Junaid daya fito daga cikin motar da saurin yana kiran Moha. Sai a lokacin ya d'auke idon sa daga kan Jadwah ya mayar kan Junaid dake tunkaro sa. Ganin haka Jadwah ta rab'a da sauri ta gefen sa ta shige gida ta ya bita da kallo ta gefen ido.
Kan benci ta samu Baba riƙe da radio yana ji. Har k'asa ta durkusa ta gaishe shi kafin ta shige d'aki ta chanza kayan makarantar ta zuwa doguwar riga d'an k'aramin hijabi mai hannu daya tsaya mata gwiwa. Kai tsaye ta fito don d'ura musu abincin rana. Shinkafa ta fara d'ura ta koma kan kayan miya ta gyara su ta wanke sannan ta samu guri ta zauna kusa da Baba tana jajjaga kayan miya. Babu zato Moha ya shigo ta k'aramin gate nasu. Kallo d'aya tayi masa ta d'auke kai ta cigaba da jajjagenta tana jin Baba na gaishe shi cikin girmamawa. Wani irin tukukin bak'in ciki ya d'arsu a ranta. Kaman mahaifin ta zai zubda girma yana gaisa da yaron daya haifa.?
Bai amsa ba ya wuce fuskar nan tashi babu emotions bare ka gane abunda ke cikin ransa. Baki Jadwah ta ciji har wasu hawayen bak'in ciki suka taron mata a ido ganin Baba Sam bai damu da abunda Moha ya yi masa ba, saima murmushi dake kwance kan fuskarsa . Haka ta gama abincin ranta na matuƙar suya. Wajen la'asar Suwaiba ta shigo gidan yauma dai maimakon ta wuce ciki bayan Jadwah da buɗe mata gate, sai ta faka motar ta fito har inda Baba suka gaisa da d'an girmamawa. Mamaki sosai ya kama Jadwah dake kallon yanda ta saki fuska sosai suna magana da Baba, kafin ta kalli Jadwah da wani abu kan fuskar ta ta miƙo mata leda mai kyau.
Harshe Jadwah ta taune tana kallon ledar. Sam ranta bai kwanta ba amma saboda idan Baba dake kanta ta matso cikin girmawawa ta karb'i ledan tana mata godiya. Kaman ance ta d'aga kai idan ta ya sarke dana Moha dake tsaya jikin window na saman d'akin sa fuskarnan da wani irin expression. Da sauri ta d'auke kai ta wuce d'aki da ledar a hannu. Cikin bakko ta tura ledar bata ma buɗe taga meke ciki ba. Maimakon ta fito saita samu guri ta zauna har saida taji Suwaiba tayi sallama da Baba ta wuce ciki. Ajiyar zuciya ta sauke mai k'arfi tana tunanin. Wai menene yasa kwana biyu mutanen nan suke neman shiga rayuwar ta ne?.
Washegari suka tashi da hayaniya ta motoci dake sunturi a gidan. Manya mata ne suka dinga turuwa zuwa da y'an mata. Kafin la'asar an fara k'awata farfajiyar gidan da kujeru. Daga Jadwah har Baba suna zaune gefe suna kallon shige da fice da ake. Wajen La'asar saiga Amina ta shigo idon nan ya yi jazur alamun taci kuka ta koshi. Da mamaki sosai Jadwah ke tambayar ta meke damunta. Amina na kuka sosai take ce mata taron da ake na d'auren Asiya ne da Moha. Wannan taron na yau wai pre-wedding d'insu ne . Nan da sati biyu masu zuwa za'a d'aura aure.
Baki Jadwah ta tab'e tana kallon Amina dake rusa kuka kaman wadda aka cewa uwarta ta mutu. Mtsww taja tsaki. Ita ta rasa menene da Moha haka da Amina take masa irin wannan so haka.
Wani irin jifa ya yi da remote d'in TV dake hannun sa ya juyawa Balaraba baya dake zaune ta d'ura k'afa daya kan d'aya tana kallonsa calmly. Da k'araji ya k'ara damke wayar dake hannun sa yace
"How could you Dad. Did you even aske me?, what age nake yanzu da ake neman yimin auren dole?"
Numfashi Balarabe yaja ta cikin wayar murya a matuƙar sanyaye yace
"Son, please. Kabi umarnin Mahaifiyar ka. Da kai da Asiya duk d'aya ne. I'm sure you will be happy da wannan choice d'in. Relax "
"Relax " Moha ya maimaita da wani irin mocking voice ya cigaba.
"Your telling me to relax ?. Are you even for real dear father ?. I refuse to be her puppet just like you. And she's not my mother "
Da k'araji Alhaji Balarabe yace da b'aci rai. " what did you just call me?"
Bai bashi amsa ba ya kashe wayar ya yi wani jifa da ita. Azafafe ya juyo kan Balaraba dake zaune har zuwa lokacin da murmushi kwance kan fuskarta. Abun mamaki yanda ya juyo da fushi da tsananin kiyayya. Kalaman dake kan harshen sa ya kasa furtawa kaman wanda aka d'aure harshe da mukulli. Matsanancin mamakin abunda ke faruwa dashi yasa ya zuba mata ido yana kallon ta. Murmushi ta k'arayi ta tako da wata tafiyar izza har inda yake tsaye tana kallonsa da k'ananan idonta . Hannu ta d'an had'a guri d'aya tace
"Good. Ina muka tsaya?. Yauwa. Yau ne pre-wedding naka kai da Asiya. I expect you ka shirya ka fito kuyi hutona. Kar kayi wani abu da zai b'atamin rai. Kaman yanda mahaifin ka ke gudun b'acin raina. I hope xaka bani had'in kai kar ran kowa ya b'aci. "
'I hate you ,you witch' abunda zuciyar sa ke furtawa kenan amma harshen sa ya kasa furta shi. Wani murmushin Balaraba tayi ta juya tana kallin agogon dake hannun ta tace
"Ka shirya nan da minti talatin. Nasa Isma'il ya gayyato dukkanin wasu abokan ka na nan zasu zo nan da minti ashirin. So get ready"
Har takai bakin k'ofa ta juyo " au na manta. Saboda abune na manya zamuyi kyauta na mota da gidaje guda ashirin. Iya na yau kawai saboda duniya tasan za'ayi biki na y'an gata. So ina son yanzu kasa hannu kan takardun da zamu bayar zan aiko Isma'il ya karb'a. "
Hmm Allah ya kyauta. D'urawa kai wahala. In bata manta ba har sark'ar ta hango a wuyan sa. Allah ya shirya mana zuri'a. Sanin tarbiyar gidan yasa bata ji komai kan sark'ar dake wuyan sa. Domin tasan dukkanin su babu tarbiya daga uwar har ya'yan. Shi yasa wani lokacin rufin asiri alheri ne ga wasu.
𝗦𝗔𝗨𝗬𝗜𝗡
𝑳𝑨𝑴𝑨𝑹𝑰.
𝔸𝘚Η𝔸𝑵𝚃Ⲩ 𐐛૦𝚅𝞔.♡︎
𝐏𝐆 6.
Yau ya kama ranan asabar, kwana biyu kenan da had'uwar ta da Moha. Tun ranan da suka had'u bata k'ara ganinsa ba. Itama kuma dama bata damu da k'ara had'uwa dashi. A gurguje ta fito sanye cikin kayan makaranta da nik'af a hannun ta tana k'ok'arin sawa tayiwa Baba sallama ta fito daga gida. Saboda saukar su dake matsowa yasa kwana biyu ake musu interview mai zafi. Tana k'ok'arin buɗe gate taji kaman ana kallonta. Da sauri ta juya inda take tunanin idon na binta. Tsaye ta hango shi bakin barandar sa sanye da bakin singlet mai yankakken hannun da bakin wando. Wuyansa irin ear pod d'innan ne na turawa da suke sawa.
Gashinsa dake jike ya d'an zubo goshin sa zuwa idon sa. Suna had'a ido taji wani irin shock ya ratsa ta tayi saurin buɗe k'ofar ta fice k'irjinta na harbawa da sauri. Tana fitowa bak'ar motar Camry ta faka gabanta Amina ta fito daga cikin motar. Da d'an mamaki ta kalli Amina tace
"Au kema wai baki tafi ba?"
"Eh shigo mu k'arasa"
Bata musa ba ta shiga motar ta zauna tana juyowa idan ta ya fad'a cikin na Junaid dake kallonta ta mirror. Da azama ta d'auke idon ta tana tunanin inda ta sanshi. Murmushi Junaid ya yi yaja motar suka bar k'ofar gidan. Har suka k'arasa gate na makaranta ,Amina da Junaid na hira ita ta kasa tankawa saboda kallon da yake mata ta mudubi. A hanzarce ta buɗe motar ta fice Amina itama ta fito da sauri tana cewa
"Wai saurin me ki ke ne? Ki tsaya mana mu tafi tare"
Batace komai ba ta juya ta shiga ⁰⁰⁰⁰makaranta Amina ta bi da sauri. Da ido Junaid ya bisu har suka shiga makarantar kafin ya ja motar yana murmushi. Tunda suka shiga aji Amina ke neman hanyar da zatayi wajen ganin ta fara kafa gwamnatin Junaid wajen Jadwah kaman yanda tayi masa alkawari, tunda ita ba waya ce da ita ba. To ko bayan da suka tashi k'arfe 11 suna fitowa suka samu Junaid jingine jikin mota yana jiransu. D'an bata rai Jadwah tayi don ta lura da take taken su shida Amina. K'ok'arin wucewa tayi ta tafi Amina tayi saurin riƙe ta ta b'ata rai
"Wai me ki ke nufi ne? Yayan nawa ne ya zama abun gudu ko me?"
Kallon Amina tayi taga yanda ta b'ata rai sosai. Ajiyar zuciya taja badan taso ba ta juya suka shiga motar. Tunda ta shiga takejin idan Junaid kanta, amma taki kallon inda yake zaune har suka k'arasa k'ofar gida. Da sauri ta fice daga motar babu ko sallama, Amina ta sauke glass tana k'ok'arin yi mata magana aka buɗe k'ofar k'aramin gate aka fito . Ido suka zubawa Moha daya fito sanye cikin k'ananan kaya. Ash d'in riga mai gajeren hannu da blue Jean's. Rigar ta kama k'irjin nan ta kwanta ko ya ya motsa sai kaga jijiyoyin hannun sa. Kar kuso kuga idon Amina yanda ya buɗe kaman wata horror. Baki hangame take kallon Moha dake tsaye bakin gate d'in hannu zube cikin aljihun wando, fuskarnan a mugun turb'une.
Ido suka had'a da Jadwah da k'irjin ta ya fara harbawa da k'arfi itama ta tamke fuska. Juyawa tayi ta kalli Amina dake kallonsa kaman wadda ta warke makanta. Dariya ta kusa kwacewa Jadwah tayi saurin danneta tana kallon Junaid daya fito daga cikin motar da saurin yana kiran Moha. Sai a lokacin ya d'auke idon sa daga kan Jadwah ya mayar kan Junaid dake tunkaro sa. Ganin haka Jadwah ta rab'a da sauri ta gefen sa ta shige gida ta ya bita da kallo ta gefen ido.
Kan benci ta samu Baba riƙe da radio yana ji. Har k'asa ta durkusa ta gaishe shi kafin ta shige d'aki ta chanza kayan makarantar ta zuwa doguwar riga d'an k'aramin hijabi mai hannu daya tsaya mata gwiwa. Kai tsaye ta fito don d'ura musu abincin rana. Shinkafa ta fara d'ura ta koma kan kayan miya ta gyara su ta wanke sannan ta samu guri ta zauna kusa da Baba tana jajjaga kayan miya. Babu zato Moha ya shigo ta k'aramin gate nasu. Kallo d'aya tayi masa ta d'auke kai ta cigaba da jajjagenta tana jin Baba na gaishe shi cikin girmamawa. Wani irin tukukin bak'in ciki ya d'arsu a ranta. Kaman mahaifin ta zai zubda girma yana gaisa da yaron daya haifa.?
Bai amsa ba ya wuce fuskar nan tashi babu emotions bare ka gane abunda ke cikin ransa. Baki Jadwah ta ciji har wasu hawayen bak'in ciki suka taron mata a ido ganin Baba Sam bai damu da abunda Moha ya yi masa ba, saima murmushi dake kwance kan fuskarsa . Haka ta gama abincin ranta na matuƙar suya. Wajen la'asar Suwaiba ta shigo gidan yauma dai maimakon ta wuce ciki bayan Jadwah da buɗe mata gate, sai ta faka motar ta fito har inda Baba suka gaisa da d'an girmamawa. Mamaki sosai ya kama Jadwah dake kallon yanda ta saki fuska sosai suna magana da Baba, kafin ta kalli Jadwah da wani abu kan fuskar ta ta miƙo mata leda mai kyau.
Harshe Jadwah ta taune tana kallon ledar. Sam ranta bai kwanta ba amma saboda idan Baba dake kanta ta matso cikin girmawawa ta karb'i ledan tana mata godiya. Kaman ance ta d'aga kai idan ta ya sarke dana Moha dake tsaya jikin window na saman d'akin sa fuskarnan da wani irin expression. Da sauri ta d'auke kai ta wuce d'aki da ledar a hannu. Cikin bakko ta tura ledar bata ma buɗe taga meke ciki ba. Maimakon ta fito saita samu guri ta zauna har saida taji Suwaiba tayi sallama da Baba ta wuce ciki. Ajiyar zuciya ta sauke mai k'arfi tana tunanin. Wai menene yasa kwana biyu mutanen nan suke neman shiga rayuwar ta ne?.
Washegari suka tashi da hayaniya ta motoci dake sunturi a gidan. Manya mata ne suka dinga turuwa zuwa da y'an mata. Kafin la'asar an fara k'awata farfajiyar gidan da kujeru. Daga Jadwah har Baba suna zaune gefe suna kallon shige da fice da ake. Wajen La'asar saiga Amina ta shigo idon nan ya yi jazur alamun taci kuka ta koshi. Da mamaki sosai Jadwah ke tambayar ta meke damunta. Amina na kuka sosai take ce mata taron da ake na d'auren Asiya ne da Moha. Wannan taron na yau wai pre-wedding d'insu ne . Nan da sati biyu masu zuwa za'a d'aura aure.
Baki Jadwah ta tab'e tana kallon Amina dake rusa kuka kaman wadda aka cewa uwarta ta mutu. Mtsww taja tsaki. Ita ta rasa menene da Moha haka da Amina take masa irin wannan so haka.
Wani irin jifa ya yi da remote d'in TV dake hannun sa ya juyawa Balaraba baya dake zaune ta d'ura k'afa daya kan d'aya tana kallonsa calmly. Da k'araji ya k'ara damke wayar dake hannun sa yace
"How could you Dad. Did you even aske me?, what age nake yanzu da ake neman yimin auren dole?"
Numfashi Balarabe yaja ta cikin wayar murya a matuƙar sanyaye yace
"Son, please. Kabi umarnin Mahaifiyar ka. Da kai da Asiya duk d'aya ne. I'm sure you will be happy da wannan choice d'in. Relax "
"Relax " Moha ya maimaita da wani irin mocking voice ya cigaba.
"Your telling me to relax ?. Are you even for real dear father ?. I refuse to be her puppet just like you. And she's not my mother "
Da k'araji Alhaji Balarabe yace da b'aci rai. " what did you just call me?"
Bai bashi amsa ba ya kashe wayar ya yi wani jifa da ita. Azafafe ya juyo kan Balaraba dake zaune har zuwa lokacin da murmushi kwance kan fuskarta. Abun mamaki yanda ya juyo da fushi da tsananin kiyayya. Kalaman dake kan harshen sa ya kasa furtawa kaman wanda aka d'aure harshe da mukulli. Matsanancin mamakin abunda ke faruwa dashi yasa ya zuba mata ido yana kallon ta. Murmushi ta k'arayi ta tako da wata tafiyar izza har inda yake tsaye tana kallonsa da k'ananan idonta . Hannu ta d'an had'a guri d'aya tace
"Good. Ina muka tsaya?. Yauwa. Yau ne pre-wedding naka kai da Asiya. I expect you ka shirya ka fito kuyi hutona. Kar kayi wani abu da zai b'atamin rai. Kaman yanda mahaifin ka ke gudun b'acin raina. I hope xaka bani had'in kai kar ran kowa ya b'aci. "
'I hate you ,you witch' abunda zuciyar sa ke furtawa kenan amma harshen sa ya kasa furta shi. Wani murmushin Balaraba tayi ta juya tana kallin agogon dake hannun ta tace
"Ka shirya nan da minti talatin. Nasa Isma'il ya gayyato dukkanin wasu abokan ka na nan zasu zo nan da minti ashirin. So get ready"
Har takai bakin k'ofa ta juyo " au na manta. Saboda abune na manya zamuyi kyauta na mota da gidaje guda ashirin. Iya na yau kawai saboda duniya tasan za'ayi biki na y'an gata. So ina son yanzu kasa hannu kan takardun da zamu bayar zan aiko Isma'il ya karb'a. "