← Book details Sahra Hot Love Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 24

Sashe 12

Sahra Hot Love Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washe gari, kinbari suhada i'do tayi saboda tsananin kunyan abunda yay mata jiya ..koda asuba dataji motsin sa ya dawo da sauri tatashi daga kan abin sallan datake ta kwanta gado tarufe duka jikinta da bargo. haryazo yagama shirin office yafita duk tana jinshi a haka bcc ya dauke ta.

Da yamma suna zaune a garden dake kusa da part dinsu i'ta da baby sukajiyo muryan hajja tana cewa "Aliyu kabiyoni nan muje ance matar taka tana lambu basai kuje tatayaka wanka ba , zama kafi jin da dinsa ,,,shegen taurin kai kamar arnen farko.wuce muje." Ta fixgo hanunshi sukayi garden din.

I'ta kam tanajin hajja ta amsabi aliyu kirjinta yafara disco ba shakka da i'ta daya ce buya zatayi a wani gurin . hajja tana hangota ta washe baki tajuya ta kallesa tace "kaganta nn ta rangwada maka kwalliya,,,,ea wllh yaron nan kayi dace ..shege mai katon kai saura kuma i'ta ma karinka hade mata wnn fuskar taka mai kama dana bosawan india." Tazungure masa kai dai2 suna karasawa gurin.

Harara hajja ta zabga ma baby da i'ta ma hararan nata take tace "rasa kunya, wato ke kika jawota nn kina mata hudubar rashin mutunci ko?,,, kedai wllh kinyi asara da fitsara.. duk cikin jikokina ba mara mutunci kamar ke ..shegeya girman burodi kawai." Tawullar da hanun baby dake kan kafadan sahra.

Murguda baki tayi ta zungurewa hajja kai tagudu tabar gurin , da gudu itama hajja ta bita ganin tatsere matane yasa tadawo tana zazzaga bala'i.

"Wllh yau saidai mahammadu yazaba koni ko wnn shegeyar 'yar tasa mai bakin rashin mutunci...i'na nan bazan tafiba saiya koreta tabar gidan nan." Shidai aliyu yana tsaye kamar an dasashi don yana magana akan baby zatace ea dama bakinsu daya duk wani rashin mutunci shiyake koya mata.

Harta karaso gurin bata daina bala'i ba saida sahra tace "inayina..." Ta washe baki tazauna gefenta tace "lafiya lau yarnan , injidai bawata matsala dakike fuskan a gidan?." Gyada mata kai tayi tace "eh..." Kara washe baki hajja tayi tace "to madalla haka nakeson ji.

Amma dakinga wani abun dabai gamekiba ki karbi wayar mijinki kikirana. ki kuma kula sosea kiyi taka tsantsan dawasu...barin dayar matar ba uwar su mijin nakiba abokiyar zaman nata me manyan kumatu kamar cincin..kiyi kaffa kaffa da'ita saboda ban yarda da i'ta ba." B'ata fuska aliyu yayi yace "hajja wai meye kika hakane, rashin kunya kike koya matafa knn." Harara ta zabga masa tace "uwar rashin kunya ba rashin kunyaba, hakawai inbarta cikin duhu tayi mu'amala da mutumin zadai cutarta ,,,,tofa wllh bazai yiyuba saina fada." Jan hanun Sahra tayi sukabar gurin tanata bambami a liyu, yayi tsaki yabi bayansu .

Afalo yatardasu hajja tasata gaba sai magana kasa2 take mata , ko inda suke bai kallaba ya shigewarsa bedroom yashiga wanka.

Sunfi minti goma hajja ta na mata magana kasa2 daga karshe tace "bari inbarki haka tunda mijin naki yashigo ,,,amma dai kikula sosea kuma kibi mijin ki duk abinda yace dake kiyi don jikan nawa wani irin hali gareshi zama dashi sai mai hakuri ..kiyi hakuri kikara hakuri dashi." "To hajja...ngde." Mikewa tsaye tayi tace "lala bakomai ea yiwa kaine,,kinga nayi nan." Tafice abunta.

Da ido ta bita tasauke ajiyan zuciya a cikin ranta tace "to..i'ta kuma haka take?." Tashi tayi ta bude bedroom din a hankali ta leka taga baya ciki sai wayarsa a kango gado,,,harta juya zata rufe saikuma tashigo a hankali tadauki wayar tafice . kitchen tashiga tarufe ta jingina jikin kofar ta danna wayar takawo haske.

Ajiyan zuciya ta sauke ganin ba security takurawa photon kan wayar ido ..yana sanye da kananun kaya blue din riga da bakin wando yazuba hannayensa cikin aljihu baiyi murmushi ba amma hakan bai hanashi yin kyauba saboda abu mai koya yake mai kyau ne.

Tafi minti goma tana ganin photon sannan tarubuta number abbanta tai dailing.

Daga dayan bangaren yana zaune falo yana karatun al Qur'an yaji wayanshi na ring , saida yakai aya ya daga wayar yasa a kunne yace "assalamu alykum." Lumshe ido tayi lokaci daya taji hawaye yaciki idon cikin rawar murya tace "Abba!." Wara ido yayi jin muryanta yawaiga yaga Omomy batanan yatashi yashiga dakinsa yarufe kofa "Habibty!." Fashewa tayi da kuka tace "Abba na...kananan lpy?." tausayinta ne yaji ya gama rufesa yace "habibty ina nan lpy, Yaya kike inafatan bawani matsala dakike fuskan ta?uhm?,,bakya jine?" Kuka tafashe dashi sosea harda shashshek'a tace "bakomai abba,,,amma what about my school?

Abba inason inci gaba da karatuna." Gyara tsayuwansa aliyu yayi da tunda yafito yaji shashshek'ar kuka a hanyar kitchen yazo yatsaya gun.

Ajiyan zuciya abba yayi yace "kiyi hakuri habibty kiyi keeping karatunnan a site kinga yanzu zaman aure kike nd bakuma lallai mijin yayarda kici gaba ba...inamai baki hakuri daduk abinda yafaru kiyi hakuri kizauna lpy sai hankalina ya kwanta." Shiru tayi batace komai ba sai uban kukan datake cizga harda majina, nasiha yarinka yimata yana kwantar mata da hankali daga karshe yakatse kiran.

Sulalewa tayi nn kasa tade kai da gwiwa taci gaba da kukanta.

Dafata taji anyi bashiri ta dago ta wara ido tafara ja baya tana girgiza kai "kayi hakuri dan Allah,, wllh bazan kara daukar maka waya ba ..abbana nakira...inji lafiyarsa.

" kallonta yarinkayi duk tagama tsorata saida takai aya snn ya lumshe ido yabude su a hankali yasauke kan fuskanta.

Karasawa gurin ta yayi yakoma hanunta cikin wani irin yanayi suka fito falo. zaunarta yayi kan sofa ya bude fridge yadauko mata bottle water mai sanyin gaske yazuba mata cikin glass cup yamika mata,,, Ba musu ta karba tasha rabi yakarbi sauran ya ajiye gefe..ganin yanda yakura mata ido yasa ta sauke kanta kasa tana wasa da finger dinta.

Kamo hanun datake wasa dashi yayi yace "kinason komawa school!?." Saurin dagowa tayi ta gyada masa kai hawaye na zubo mata...

Girgiza mata kai yayi yace "kibar kuka SAHR!." Yafada cikin wata irin kasalalliyae murya..

Har cikin ranta taji yanda yakira sunan nata taji bawan da ya'iya furta sunan kamar shi.

A hankali yadaura yatsansa kan fuskanta yagoge mata hawayen yana ganin kwayar idonta yace "kina islamiyya? .

" gyada mishi kai tayi tace "eh..ina aji hudu, a boko kuma ss3." Gyada kai yayi yace "gud..zakici gaba da school dinki." Wani irin farin ciki taji yakama cikin sanyi murya tace "ngde." Mikarta yayi yawanke mata fuska a toile yakama hanunta suka tafi main house.
_Aunty rash nagode sosea Allah yabar zumunci
nayi fushi,,nayi tunanin zanga manyan leda amma shiru
View wattpad @habiebahlurv
Beenaf/beelurv
SAHRA
Hot love
25....

A general falo suka tadda duk yan gidan banda samha da tun safe tafita school har yanzu bata dawoba, gaidasu duka sahra tayi tasamu guri gefen baby ta zaune tai tsim! tanajin hiran nasu..don ita batada nacewa.

Kallonta majeed yayi ya kalli aliyu yace "nikan matar taka bata maganane !?." Harara ya zabga masa yace "kai ka maidata kurma?, ko kuma baku taba gaisawa bane!?." Tabe baki yayi yadaga kafada yace "naga ko yaushe shiru take ne!." Baby tadan bugi kafarta kasa kasa tace mata "sis kirinka magana don Allah,,, hakan dakike ba dadi." Kallonta tayi kamar zatayi magana sai kuma ta dauke kanta ..i'ta batasan mezata ceba.

Turowa kofar falon tayi tashigo tana taku high hill din kafarta sai kara yake kwas2 gakuma chewing gum datake taunawa, murmushi small mom tasaki tace "wlcm back daughter." Kokadan bata jiba don hankalinta gaba daya yagama tafiya akan aliyu da yana ganin ta yawani hade rea kamar bai taba dariya..dukda de more especially ran nashi ba'a sake yakeba.

So take ya d'ago ido ya kalleta amma hakan baiyiyu ba saima ido daya zubawa sahra da kanta ke a kasa, gaisuwan munafurci tashiga yi tafara gaidasu onebyone saida tazo kansa tawani kashe murya tace "barka da yamma ya aliyu." Kokadan baiso ya amsa ba ,,amma ganin rashin dacewar hakan yasa yace "brk!." Batare daya dago da ido ba bare yaga site din datake.

Hakan dayayi yayi matukar bata mata rea ,, watode har yanzu bata ishesa ko kallo bama,,,lallai da sake.

Wucewa tayi falonsu tana saka abubuwa dazata aikata.

Sai karfe goma bayan sunyi dinner sunyi hira sosea har sahra tadan saki jiki da majeed yanda yake mata hira sosea na abin dariya suka tafi part dinsu.

Yau aliyu baifita ko i'naba kasancewar weekend ne suna zaune falo bamai cewa kowa komai, dan satan kallonta yayi yaga idonta nakan TV yadan gyara muryansa kadan yace "ran Monday zaki fara fita school tareda baby..da yamma zakuje islamiya tare. nama shugaban makarantar magana hijab mai girma zaki sa,,,kisan irin rayuwar da zakayi acan don aure gareki!." Sosea maganar auren yadaki zuciyarta amma taji dadi sosea na komawanta school.

"Ngde!." Tace tana kallon sa.

Gyada kai yayi yace "anything 4 u dear.....bai karasaba yay saurin rufe bakinsa yadan saci kallonta yaga har lokacin tana kallonsa yace " am kishiga kitchen ki hada mana lunch yau!." Tashi tayi tadau hanyar kitchen saikuma ta juyo tace "me za'a dafa!?." "Anything u like!." Yafada yana mikewa kan 3sitter. juyawa tayi ya bita da kallo har saida tashige snn yatashi yazauna yafara tunanin "yakamata sukafa zaman aure!

Irinna kowani mata da miji!." Zubawa store din dake cikin kitchen din ido tayi,, gakayan abinci kala2 tana tunanin wanda zata dafa , tafi minti shida a haka kafin tayi making mind dinta tayi coconut Rice da vegetables soup mai redmeat snn tayi banana shaka juice.

Cikin awa daya da rabi ta hada kamai ta zubasu cikin designer food Flack's data gani cikin kitchen din tazuba su cucumber da cabbage data yanka cikin wani bowl taje tajera kan dinning.

Koda tafito falo bayanan don tun shiganta kitchen yafita masallaci bai dawoba har yanzu.

Wanka tayi tasaka wani atamfa da mami ta aiko mata tadanyi light makeup tayi sallan azahar snn tafito ..

Kafeta yayi da lumsassun idonsa ya rinka kallonta yanajin wani abu yana tabar masa zuciya..sosea kayan yay mata kyau ya burgeshi kowani shape na jikinta ya fita .Ganin irin kallon da yake mata yasata zama kan kujera bashiri ta sauke kanta kasa murya a hankali tace "nagama!, yana dining!." Maganar datayine yadawo dashi yay saurin dauke kansa ya kalli dining area din.

Sosea yadda tatsara gurin ya burge shi "she's nyc!
Chapter 12 · 0% Book details