Sashe 4
Rayuwar Safeeya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Malam wallahi ni ba y'ar iska bace ni ba karuwa bace abinda kuke tunanin inayi da Abubakar wallahi ba haka bane hasalima bai taba neman hakan a gurina ba, kuma kai da ka nema bazan baka ba na hana babban kwabo kawai mts"
Naje na samu mamana in fada mata duk yadda akayi gudun kar taji zancen a waje tayi zaton ko bani da gaskiya washegari ta daukeni ta kaini gurin kanwarta ta fada mata duk yadda mukayi da musa.
Kanwarta tace,
"Kin gani tunda kinsan yaron nan Abubakar yana son safiya ki kyalesu suyi soyayyarsu"
Mamana tace,
"Wallahi bazan bari ba ai nasan duk wanda zai ce yana son safiya a yanzun to ba sonta yake ba wayo zai yi mata ya rabata da darajarta"
Kanwarta tace,
" Daman ni shawara ce na baki don karki manta a yanzun Ss 2 zata shiga a ganina don ta tsaya da saurayi ba wani abu bane"
Mamana tace,
"A'a ita fa bata yarda da hakan ba a dole kanwarta ta kyaleta tayi min fada sosai akan na cigaba da kame kaina, nayi mata godiya muka nufo gida ni da mamana.
Haka rayuwar taci gaba da juyamin a kullum sai an shirya labari an fadawa mamana ita kuwa daman ba ruwanta da bincike zata nada min duka ne kawai.
Kuma babu mai kwata na agidan duk yawan gidan.
Daga baya ma mamana da kanta ta koreni daga dakin ta tace bazata zauna dani a daki guda ba, uwargidan Babana ita tace,
"Ai baza'ayi hakaba ki dawo dakina ki zauna ai nima uwace"
Na tattaro kayana na koma dakinta da zama kwata-kwata mamana ta fita har kata ta cireni a gabanta bata ma san Allah yayi ruwana a gidan ba, rayuwarta kawai take yi bata da damuwa don bata kaunar naje gurin ta.
Shekara ta zagayo kowa mahaifiyarshi tayi masa dinkin sallah amman banda ni kuma ga uwata a raye ubana a raye amman saboda Abubakar na rasa su tare da duk wata hidimarsu gareni.
Babbar matsalar Mamana rashin bincike komai aka fada mata ta zauna a kanshi kenan bata la'akari da halayyar mutum zai aikata ko bazai aikata ba, duk abinda akace mata y'arta ko danta yayi a gurinta ya aikata ne kawai bazata tambayeshi ba zata yanke hukunci.
Haka nan akayi sallah kowa yasa sabon kayansa ni kuma na wanke tsohon kayana nasa abina.
Haka nan nacigaba da rayuwar kunci a gidan mahaifina, ga kuma firdausi ta dawo da halinta a kaina ganin bana tare da mahafiyata tasani gaba, ta ringa hadani da jikokin hajiya rabi har sai da mukayi fada sosai hakan yasa itama ta koroni daga dakin ta tace,
"Bazan iya ba na taimakeki amman kina fada da jikokina ki koma dakin uwarki mai bakin hali kawai uwarki ta koreki ma ballantana ni"
Na kwashe kayana ina kuka na nufi gidan kanwar mamana na fada mata duk abinda ke faruwa mamaki tayi sosai ta kuma ce na dawo gidanta na zauna, na koma gidanta.
Wata na biyu a gidanta sannan ta samu ta shawo kan mamana ta hakura na koma gidanmu.
Alkalumman:
Maman nurul huda👄
And
Maman ihsan😍
Pls share and comment
[6/30, 2:05 PM] MAMAN IHSAN 😍: *RAYUWAR SAFIYAH*
*True life story*
Story by : Maman Nurul Huda👄
Written by: Maman Ihsan😍
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM !
🌟GORGEOUS WRITER FORUM🌟
🌟G. W. F🌟
Home of gorgeous intelligent and expert writers, we are the best among the rest.
Page 15/16
Na dawo gidan naci gaba da zama cikin kunci da matsi kowa ya tsangwameni magana daya biyu safiya yar iska.
Wata rana ina fita naje makotanmu a ranar banma hadu da abubakar ba amman mamana tana dawowa akace mata wai anganni da Abubakar yana latse ni, a take muna haduwa mamana ta dauramin wani gigitaccen mari wanda yasa na dauke numfashin wucin gadi na fara ganin juwa tana daukana,
Nan mama tayi min duka zancen duk ya karade unguwarmu dama family house dinmu dake zaria kasancewar y'ay'an hajiya Rabi sunfi rayuwa acan shi yasa suka kwashe karya da gaskiya suka fadawa dangin mu, cewar nazama y'ar iska bin maza nakeyi na zama karuwa harda ciki nayi aka zubarmin hakan yasa duk sukaja kunnen y'ay'ansu akan su daina mu'amala da ni.
Duk family din mu babu inda zanje na samu salama saboda anbata min sunana ako ina kowa gudu na yakeyi,
Kaf din yaran gidanmu mata babu wadda babanmu ya taba daga hannu ya daketa sai ni saboda makiya na da magulmata na da kuma *Sharrin y'an uba* sai da aka zigashi yayi min dukan tsiya.
Hakan yasa na fara kokarin cire Abubakar daga zuciyata duk da irin son da nake yi masa na fara ja baya daga gareshi.
A lokacin da na shiga Ss 3 sai kuma farin jini na ya karu masu kudi suna yawan zuwa gurina har gidanmu duk da bawai ni ke nuna musu gidanmu ba tambaya suke yi.
Nan fa zance yakara bin gari yanzun iskancin nawa ya karu gashinan harda alhazai masu motoci ke biyoni har gida.
Duniyar ta kara yimin kunci, ada ina tunanin idan na rabu da Abubakar za'a sakarmin mara nayi fitsari ashe ba haka bane, wani ballin daban ne zai kunno kai.
Babban wana ya kamani yayimin dukan tsiya, na zamo tamkar jaka wannan ya daka wancan ya daka kullum cikin duka duk iya kokarin da nakeyi don na fahimtar dasu amman sun kasa fahimta ta.
Haka nan nayi ta rayuwata mahaifiyata bata bani fuska ba ballantana na sanar da ita damuwata ba har na gama secondary school, acikin yayyena mata wadanda suka yi aure yayarmu babba mace a dakin mu ita kadai ce take tausayamin.
Nan ta fara cewa inje wurin ta inyi mata hutu sai inje sati daya nake yi na dawo bazan dade ba zata kuma neman nazo, tana son zama dani don bani da k'iywar aiki domin a unguwarsu basu da ruwa sai kayi tafiya kafin kaje inda ruwan yake haka zan kwashi bokitai na tafi na debo mata ruwan.
Don nafi son zaman gurinta akan gidan mu duk da ina mata aiki amman nafi sakewa akan na zauna gurin da kullum ina cikin cin duka.
Kullum sai naje dibar ruwa hakan yasa na fara sabawa da mutanen unguwar muna dan gaisawa a tsakanin mu, wata rana naje dibar ruwa na dawo sai aka aiko ana sallama da ita sai ta fita don ganin wake kiranta.
Tana fita sai taga police a tsaye bayan sun gaisa yace,
"Don Allah yarinyar nan da take dibar ruwa kullum 'yar aikin ki ce?"
Sai tace masa
"A'a ba 'yar aikina bace kanwata ce mamanmu daya da ita baban mu daya tazo hutu ne"
Nan yayi mata fada akan don ba ita tahaifeni ba shi yasa kullum take aikana dibar ruwa, ta kalleshi da mamaki tace,
"Malam yarinyar nan fa kanwata ce uwa daya uba daya kuma bani da ruwan nan mene aibu don ta debo min ruwa?"
Sai yace, " wannan ne kawai matsalar?"
Tace masa "Eh "yace,
"Toh ni zansa a ringa kawo muku ruwa amman ta daina zuwa dibar ruwa"
Tace, "Toh" tare da yi masa godiya yayi tafiyarshi,
Haka ake kawo ruwa kura daya kullum, rannan ta fita unguwa sai wasu samari a unguwar suka gaidata tare da tambayarta
"Kwana biyu mun daina ganin kanwarki tana zuwa dibar ruwa "
Sai tayi dariya tace,
"Ya akayi kukasan kanwata ce?"
Sai sukace, "Ai daga ganin ta ansan kanwarki ce ba sai an fada ba"
Tayi murmushi tace, "Tana gida"
Sai suka ce," don Allah muna neman Alfarma a gurin ki?"
Tace,
"Ina jinku Allah yasa bata fi karfi na ba"
Sukace, "Dibar ruwan da takeyi muke so ta daina zamusa mai ruwa yana kawo miki ruwan"
Abin ya bata mamaki ya kuma daure mata kai tayi musu godiya ta je ta dawo ta sameni tace,
"Safiya daman irin farin jinin da kike dashi kenan? Gaskiya dole ki samu matsala a gida saboda ba lallaine aganki da irin wannan farin jinin ba ba tare da anbiki da mugun abu ba"
"Kinsan me yasa kika ga na daina turaki dibar ruwa?"
Na girgiza kai nace, "A'a" tace ,
"Rannan wani police ni ban ma san a inda yake ba shine ya dauki nauyin kawo mana ruwa kuma gashi yau wasu samari suma sunce na daina turaki dibar ruwa zasu sa a kawo mana"
Washegari na shirya zanje gida domin inje inga gida sai tace tare zamuje,
Muka je gida tare suna hira take cewa,
"Goggo Ki daina dukan safiya akan samari domin ba yin kanta bane Allah ne ya yita mai farin jini duk inda ta shiga saita samu masoya"
Nan mamana ta rufeta da fada sosai tana cewa,
"Karki kara fada min wannan maganar don kuwan safiya ta riga ta lalata kanta"
Ta fada mata cewar,
"Wallahi goggo ada ni nake zuwa na debo ruwa da safiya tazo sai na fara aikenta inta kaice miki yanzun kurar ruwa biyu ake kawo min kullum saboda safiya kuma bata san wadan da suke kawo waba"
Mamana ta kafe sam bata yarda ba wai hada baki mukayi ni da ita tazo tana mata dadin baki.
A bisa kaddara sai kariyar arziki ya samu mijin yaya Aisha da yake gidan haya suke sai aka koresu ta dawo nan gida dakin mamana ta zauna.
Kaf din gidan nan ita kadaice ke kwata ta a hannun mamana ta bata hakuri idan tana dukana kuma tayita lallashina.
Ana haka itama yayata wadda nake binta ta dawo gida nan itama ta matsamin tayita min fada har sai yayarmu Aisha ta tsawatar mata, don maman mu ko daga kai batayi ballantana ta nuna tasan abunda muke yi.
Ana nan sai naga zaman haka bazai yi min ba sai na fara hada sitati irin wanda ake sawa a shadda ina siyarwa duk yin da nayi saina saida kuma ina samun riba sosai na fara tara kudina don inason in yi waec saboda shekara ta zagayo ban samu nayi ba.
Ana cikin wannan lokacin irin y'an siyasar nan masu campain suka biya mana neco mukayi lesson sannan muka zana neco.
Allah ya taimakeni na fito da credit uku English, geograph da government amman bani da maths.
Naje na samu mamana in fada mata duk yadda akayi gudun kar taji zancen a waje tayi zaton ko bani da gaskiya washegari ta daukeni ta kaini gurin kanwarta ta fada mata duk yadda mukayi da musa.
Kanwarta tace,
"Kin gani tunda kinsan yaron nan Abubakar yana son safiya ki kyalesu suyi soyayyarsu"
Mamana tace,
"Wallahi bazan bari ba ai nasan duk wanda zai ce yana son safiya a yanzun to ba sonta yake ba wayo zai yi mata ya rabata da darajarta"
Kanwarta tace,
" Daman ni shawara ce na baki don karki manta a yanzun Ss 2 zata shiga a ganina don ta tsaya da saurayi ba wani abu bane"
Mamana tace,
"A'a ita fa bata yarda da hakan ba a dole kanwarta ta kyaleta tayi min fada sosai akan na cigaba da kame kaina, nayi mata godiya muka nufo gida ni da mamana.
Haka rayuwar taci gaba da juyamin a kullum sai an shirya labari an fadawa mamana ita kuwa daman ba ruwanta da bincike zata nada min duka ne kawai.
Kuma babu mai kwata na agidan duk yawan gidan.
Daga baya ma mamana da kanta ta koreni daga dakin ta tace bazata zauna dani a daki guda ba, uwargidan Babana ita tace,
"Ai baza'ayi hakaba ki dawo dakina ki zauna ai nima uwace"
Na tattaro kayana na koma dakinta da zama kwata-kwata mamana ta fita har kata ta cireni a gabanta bata ma san Allah yayi ruwana a gidan ba, rayuwarta kawai take yi bata da damuwa don bata kaunar naje gurin ta.
Shekara ta zagayo kowa mahaifiyarshi tayi masa dinkin sallah amman banda ni kuma ga uwata a raye ubana a raye amman saboda Abubakar na rasa su tare da duk wata hidimarsu gareni.
Babbar matsalar Mamana rashin bincike komai aka fada mata ta zauna a kanshi kenan bata la'akari da halayyar mutum zai aikata ko bazai aikata ba, duk abinda akace mata y'arta ko danta yayi a gurinta ya aikata ne kawai bazata tambayeshi ba zata yanke hukunci.
Haka nan akayi sallah kowa yasa sabon kayansa ni kuma na wanke tsohon kayana nasa abina.
Haka nan nacigaba da rayuwar kunci a gidan mahaifina, ga kuma firdausi ta dawo da halinta a kaina ganin bana tare da mahafiyata tasani gaba, ta ringa hadani da jikokin hajiya rabi har sai da mukayi fada sosai hakan yasa itama ta koroni daga dakin ta tace,
"Bazan iya ba na taimakeki amman kina fada da jikokina ki koma dakin uwarki mai bakin hali kawai uwarki ta koreki ma ballantana ni"
Na kwashe kayana ina kuka na nufi gidan kanwar mamana na fada mata duk abinda ke faruwa mamaki tayi sosai ta kuma ce na dawo gidanta na zauna, na koma gidanta.
Wata na biyu a gidanta sannan ta samu ta shawo kan mamana ta hakura na koma gidanmu.
Alkalumman:
Maman nurul huda👄
And
Maman ihsan😍
Pls share and comment
[6/30, 2:05 PM] MAMAN IHSAN 😍: *RAYUWAR SAFIYAH*
*True life story*
Story by : Maman Nurul Huda👄
Written by: Maman Ihsan😍
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM !
🌟GORGEOUS WRITER FORUM🌟
🌟G. W. F🌟
Home of gorgeous intelligent and expert writers, we are the best among the rest.
Page 15/16
Na dawo gidan naci gaba da zama cikin kunci da matsi kowa ya tsangwameni magana daya biyu safiya yar iska.
Wata rana ina fita naje makotanmu a ranar banma hadu da abubakar ba amman mamana tana dawowa akace mata wai anganni da Abubakar yana latse ni, a take muna haduwa mamana ta dauramin wani gigitaccen mari wanda yasa na dauke numfashin wucin gadi na fara ganin juwa tana daukana,
Nan mama tayi min duka zancen duk ya karade unguwarmu dama family house dinmu dake zaria kasancewar y'ay'an hajiya Rabi sunfi rayuwa acan shi yasa suka kwashe karya da gaskiya suka fadawa dangin mu, cewar nazama y'ar iska bin maza nakeyi na zama karuwa harda ciki nayi aka zubarmin hakan yasa duk sukaja kunnen y'ay'ansu akan su daina mu'amala da ni.
Duk family din mu babu inda zanje na samu salama saboda anbata min sunana ako ina kowa gudu na yakeyi,
Kaf din yaran gidanmu mata babu wadda babanmu ya taba daga hannu ya daketa sai ni saboda makiya na da magulmata na da kuma *Sharrin y'an uba* sai da aka zigashi yayi min dukan tsiya.
Hakan yasa na fara kokarin cire Abubakar daga zuciyata duk da irin son da nake yi masa na fara ja baya daga gareshi.
A lokacin da na shiga Ss 3 sai kuma farin jini na ya karu masu kudi suna yawan zuwa gurina har gidanmu duk da bawai ni ke nuna musu gidanmu ba tambaya suke yi.
Nan fa zance yakara bin gari yanzun iskancin nawa ya karu gashinan harda alhazai masu motoci ke biyoni har gida.
Duniyar ta kara yimin kunci, ada ina tunanin idan na rabu da Abubakar za'a sakarmin mara nayi fitsari ashe ba haka bane, wani ballin daban ne zai kunno kai.
Babban wana ya kamani yayimin dukan tsiya, na zamo tamkar jaka wannan ya daka wancan ya daka kullum cikin duka duk iya kokarin da nakeyi don na fahimtar dasu amman sun kasa fahimta ta.
Haka nan nayi ta rayuwata mahaifiyata bata bani fuska ba ballantana na sanar da ita damuwata ba har na gama secondary school, acikin yayyena mata wadanda suka yi aure yayarmu babba mace a dakin mu ita kadai ce take tausayamin.
Nan ta fara cewa inje wurin ta inyi mata hutu sai inje sati daya nake yi na dawo bazan dade ba zata kuma neman nazo, tana son zama dani don bani da k'iywar aiki domin a unguwarsu basu da ruwa sai kayi tafiya kafin kaje inda ruwan yake haka zan kwashi bokitai na tafi na debo mata ruwan.
Don nafi son zaman gurinta akan gidan mu duk da ina mata aiki amman nafi sakewa akan na zauna gurin da kullum ina cikin cin duka.
Kullum sai naje dibar ruwa hakan yasa na fara sabawa da mutanen unguwar muna dan gaisawa a tsakanin mu, wata rana naje dibar ruwa na dawo sai aka aiko ana sallama da ita sai ta fita don ganin wake kiranta.
Tana fita sai taga police a tsaye bayan sun gaisa yace,
"Don Allah yarinyar nan da take dibar ruwa kullum 'yar aikin ki ce?"
Sai tace masa
"A'a ba 'yar aikina bace kanwata ce mamanmu daya da ita baban mu daya tazo hutu ne"
Nan yayi mata fada akan don ba ita tahaifeni ba shi yasa kullum take aikana dibar ruwa, ta kalleshi da mamaki tace,
"Malam yarinyar nan fa kanwata ce uwa daya uba daya kuma bani da ruwan nan mene aibu don ta debo min ruwa?"
Sai yace, " wannan ne kawai matsalar?"
Tace masa "Eh "yace,
"Toh ni zansa a ringa kawo muku ruwa amman ta daina zuwa dibar ruwa"
Tace, "Toh" tare da yi masa godiya yayi tafiyarshi,
Haka ake kawo ruwa kura daya kullum, rannan ta fita unguwa sai wasu samari a unguwar suka gaidata tare da tambayarta
"Kwana biyu mun daina ganin kanwarki tana zuwa dibar ruwa "
Sai tayi dariya tace,
"Ya akayi kukasan kanwata ce?"
Sai sukace, "Ai daga ganin ta ansan kanwarki ce ba sai an fada ba"
Tayi murmushi tace, "Tana gida"
Sai suka ce," don Allah muna neman Alfarma a gurin ki?"
Tace,
"Ina jinku Allah yasa bata fi karfi na ba"
Sukace, "Dibar ruwan da takeyi muke so ta daina zamusa mai ruwa yana kawo miki ruwan"
Abin ya bata mamaki ya kuma daure mata kai tayi musu godiya ta je ta dawo ta sameni tace,
"Safiya daman irin farin jinin da kike dashi kenan? Gaskiya dole ki samu matsala a gida saboda ba lallaine aganki da irin wannan farin jinin ba ba tare da anbiki da mugun abu ba"
"Kinsan me yasa kika ga na daina turaki dibar ruwa?"
Na girgiza kai nace, "A'a" tace ,
"Rannan wani police ni ban ma san a inda yake ba shine ya dauki nauyin kawo mana ruwa kuma gashi yau wasu samari suma sunce na daina turaki dibar ruwa zasu sa a kawo mana"
Washegari na shirya zanje gida domin inje inga gida sai tace tare zamuje,
Muka je gida tare suna hira take cewa,
"Goggo Ki daina dukan safiya akan samari domin ba yin kanta bane Allah ne ya yita mai farin jini duk inda ta shiga saita samu masoya"
Nan mamana ta rufeta da fada sosai tana cewa,
"Karki kara fada min wannan maganar don kuwan safiya ta riga ta lalata kanta"
Ta fada mata cewar,
"Wallahi goggo ada ni nake zuwa na debo ruwa da safiya tazo sai na fara aikenta inta kaice miki yanzun kurar ruwa biyu ake kawo min kullum saboda safiya kuma bata san wadan da suke kawo waba"
Mamana ta kafe sam bata yarda ba wai hada baki mukayi ni da ita tazo tana mata dadin baki.
A bisa kaddara sai kariyar arziki ya samu mijin yaya Aisha da yake gidan haya suke sai aka koresu ta dawo nan gida dakin mamana ta zauna.
Kaf din gidan nan ita kadaice ke kwata ta a hannun mamana ta bata hakuri idan tana dukana kuma tayita lallashina.
Ana haka itama yayata wadda nake binta ta dawo gida nan itama ta matsamin tayita min fada har sai yayarmu Aisha ta tsawatar mata, don maman mu ko daga kai batayi ballantana ta nuna tasan abunda muke yi.
Ana nan sai naga zaman haka bazai yi min ba sai na fara hada sitati irin wanda ake sawa a shadda ina siyarwa duk yin da nayi saina saida kuma ina samun riba sosai na fara tara kudina don inason in yi waec saboda shekara ta zagayo ban samu nayi ba.
Ana cikin wannan lokacin irin y'an siyasar nan masu campain suka biya mana neco mukayi lesson sannan muka zana neco.
Allah ya taimakeni na fito da credit uku English, geograph da government amman bani da maths.