← Book details Mutun Ko Aljana Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 14

Sashe 6

Mutun Ko Aljana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kai Baba ya geÉ—a musu sannan ya yi musu nuni da su tafi sai suka soma tafiya,

Wannan karon Malam Iliyasu bai h'au kekensa ba da kafa yaƙe tak'owa shi ma.

"Baba ka h'au keken mana"

"A'a Ɗana ku dai bari mu tafi tare yafi dad'i akan na yi gaba ni ƙad'ai ".

Murmushi Asaf ya É—an yi sannan shi ma ya ce"Baba gaskiya abokina ya faÉ—a ka h'au kekenka, ka ga mu yara ne zamu iya yin dogon tafiya lafiya lau "

Wani irin kallo Musab ya yi wa Asaf irin karya ka ke yi d'in nan,

Dan tun da yaƙe da Asaf bai taɓa ganin ya yi tafiya mai nisa ba.

Amma shi ne yanzu yaƙe cewa su yara ne za su iyayin tafiya mai nisa.

Daƙer aka lallaɓa malam Iliyasu ya h'au kekensa suka bisa a baya.

Wata ƙwa ta ,ce suka zo sallakawa sai Asaf ya faɗi a ciki,

"Subhanallah!".

Malam Iliyasu ya faÉ—i yana s'auka daga kan kekensa sannan ya karasa wajan

Musab kam dariya ya kama yi, yan da yaga Asaf cikin ƙwa ta

Kunu Asaf ya sha sannan ya ce "Taimaka min za ka yi na fito ko saya wa za ka yi ka ci gaba da dariya ?".

"Sorry abokina ga hannun na wa"

Hannun Musab ! Asaf ya kamo ya taimaka masa ya fito

Lokacin tu ni 'ƴan Ƙauyen sun taru dan ganin mai yaƙe faruwa

Kun san 'ƴan Ƙauye da gulma,

Duk da fuskarsa ya ɓaci da ƙwa ta amma su na iya ganin ky'aun da Allah ya yi ma sa,

Ƴ'emmata de ye wa ya burge su,

Ana cikin haka ne Siyama ta dawo daga wajan ɗiba ruwan da ta tafi ta zo ta tarar da abunda yaƙe faruwa

Idonta ne ya sauka akan Asaf ai ba ta san san da ta saƙi ihuuu ba.

"Wayyoooo Baba fatalwa Baba ga fatalwa kuna saye ba za ku guÉ—u ba?".

Kafin Baban ta yi magana ta juya da niyar guduwa Asaf ya fusgi botiƙin da ke kanta ya zuba ruwan dake cikin botiƙin akansa,

Da yaƙe da karfi Asaf ya fusgi botiƙin s'aura k'irin Siyama ta faɗi,ai Asaf na ganin za ta faɗi ya yi s'aurin y'er da botiƙin ruwan ya rikota ta faɗa irjinsa.

Kallo su ke wa juna ba bu ko giftawa ga ruwan da ya zuba a lallausan gashin kansa na siyayo mata akan fuskarta kamar an kunna famfo...

*Fulanin of Jajirtattu ✍️*

Comments and share fisabilillah 👏
[08/09, 19:16] Sakeena Isma'il Cameroon🥰: 💫MUTUN 👩‍🦰KO ALJANA 👹💫

Story and Written ✍️

By: Sakeena Isma'il Cameroon
(Mom Muwadda)

________________________________________________

Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/KN5jaKvQOu02sqXTMBtbRJ

________________________________________________

https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️

________________________________________________

*Diamond 💎Star 🌟 Ladies* 🧝‍♀️
*(We stand together)*
🤝🤝🤝

Paid Book ₦500

Free page8️⃣

Bismillahi rahmani rahim

Kallon su ke wa juna ba bu ko giftawa ga ruwan da ya zu ba a lallausan gashin kansa na siyayo mata akan fuskarta kamar an kunna famfo.

"Inna lillahi wa inna ilahi rajiun! Mutanan wajan su ke ta maimaita wa,sai da murmushin da yake Mus'ab ya yi ya kallesu ya shiga tambayar su "Lafiya na ji kuna Inna lillahi wa inna ilahi rajiun ?" ."Ina fa lafiya abokinka ya rungume Æ´ar uwarmu".

Tsaki Mus'ab ya ja kana ya ce"Toh ba taimaka mata ya yi da ga faÉ—uwan da take son yi ba?".

"Toh ai ƙado! nan Ƙauyen mu ɗuk kankantar na miji ba'a bari ya taɓa mace ballantana wannan k'aton".

Ki na nufin ko da kuwa ba ta da lafiya ko kuma wani abu makamacin haka ya faru kamar yan da yanzu ya faru ba'a isa a taimaka wa mace ba?".

"Eh ko da kuwa ha kan ta faru ba'a taɓa mace sai dai wanda ya ke muharraminta kuma ka ga wannan yellow mutumin nan ba muharraminta ba ne"

Kallon in da mahaifin Siyama yaƙe tsaye Mus'ab ya yi su na haɗa ido da shi ya ja kekensa ya wuce gida.

Cikin san yin jiki Mus'ab ya taɓa Asaf ai ya na taɓa Asaf tun kafin ma ya yi magana Asaf ya yi s'aurin sakin Siyama ya na tsaki.

Bangaren Siyama kuwa ana sakin ta_ ta juya ta bar wajan ta na kuka,

Sai a lokacin mutanan wajan suma su ka watse

Cikin san yin jiki Mus'ab ya kalli Asaf ya ce ma sa"Abokina mu haƙura da jira bakanikin nan mu koma in da motar mu ta ke sai mu kira dreva ya kawo mana wata motar da ga nan ma sai ya taho mana da bakanikin da zai gyara mana motar"
"Eh gaskiya ka kawo shawara mai kyau ni tun d'azu ma ban yi wannan tunanin ba wallahi ka ga da ace tun d'azu muka yi wannan tunanin ma da yanzu mun daÉ—e da barin wajan nan tun da ba wani nesa muka yi sosai ba".

"Haka ne"
Cewar Mus'ab,

"Toh amma me ya sa na gan ka wani iri ?"

"Wai kana nufin baka ji a abunda mutanan nan suka faÉ—a ba?"

Kai Asaf ya girgiza alamon bai gane ba.

Kwashe komai Mus'ab ya yi ya gaya ma sa ya kara da cewa "Toh ka ga gwara mu bar wajan nan,dan in mun zauna ba mu san wana irin huƙunci za su ɗ'auka akan ka ba,ni wallahi bam ma san me ya sa ka taɓa ta ba kai da ko hannun mace ba ka ta ba taɓa wa ba,sai ga shi yau har da riƙe Kwankwason mace ka na kallon ta.
Kai ka san me? abun fa ya burge ni gaskiya "Mus'ab ya kare magana ya na fashewa da dariya harda riƙe ciki.

Asaf kam ba karamin kulewa ya yi ba da irin dariyan da Mus'ab ya ke yi uwa uba shi bai ga abun dariya nan ba, da har zai tsaya ya na dariya,

Juyowa ya yi ya soma tafiya,

Mus'ab na ganin haka ya sai da dariyarsa da yake yi ya ce "Asaf ba mu je mun yi wa Baba sallama ba za mu tafi ".

Sai da tafiya Asaf ya yi ya juyo ya ce"Kai tun da Babanka ne sai ka je ka yi masa sallaman ai "

Ya na gama faÉ—ar haka ya juya ya ci ga ba da tafiya

"Tsaya É—ana akwai wata magana mai mahimmanci da na ke so mu yi kafin ka tafi"

Ya ji an faÉ—a cak ya tsaya shi bai juya
ba.shi bai ci gaba da tafiya ba.

"Ku zo mu shiga É—aga ciki" Ya tsake ji an faÉ—a.

Wannan karon juyowa ya yi ya kalli Malam Iliyasu ya ce "Ai Baba na kira dreva gidan mu zai kawo mana wata mota har ma da mai gyaran motar É—uka "

Murmushi irin na su na manya Malam Iliyasu ya yi kana ya ce"Shi ke nan ba bu damuwa amma dai ku zo mu je ciki kafin drevan na ku ya kara so da ga nan ma sai ku samu ku sha furan da Siyama ta dama muku "

Har Asaf ya buÉ—e baki zai yi magana jin an ambaci sunan fura ne ya sa shi yin shiru .

Saboda shi mutun ne da yake kaunar fura sosai a rayuwar sa,

Uwa uba ba karamin Æ´inwa yake ji ba,tun da bai karya ba ya fito,

Juyowa Malam Iliyasu ya yi ya fara tafiya,

Bayan shi su ka bi har su ka karasa z'auren gidan da aka yi shi kamar bukka

Wata bukka da sai an sunkuya sosai ake iya shiga ya nuna musu da su shiga,kallon Mus'ab Asaf ya yi shi ma Mus'ab kallon Asaf din ya ke yi dan sun rena bukkan sosai

Kamar Malam Iliyasu ya shiga zuciyoyinsu ya ce "Ku shiga zai ishe ku"Kai su ka geÉ—a sannan su ka shiga,

Ka san cewa ba wani jiki ne da su nazo ka gani ba, shi ya sa ba su wani sha wahala wajan shiga bukkan ba.

Sai da malam Iliyasu ya tabbar sun shiga kafin ya juya ya koma cikin gidan ya kalli Siyama da tun d'azu take ta aikin rusa kuka ya ce.

Ke in kingama kukan naki ki É—auki wannan furan da ki ka dama mun d'azu ki kai musu ki zo mu yi magana "

Kai kawai Siyama ta geɗa ba tare da ta yi magana ba,ta miƙe ta shiga ɗak'in mahaifinta ta d'auki kwariyar furan da ta dama ta fita,

Da ta zo bakin kofar shiga É—ak'in sai da ta tsaya ta gyara mayafinta kafin ta chusa kanta ciki haÉ—e da yin sallama.

Su na z'aune cikin bukkan sai karewa bukkan kallo su ke yi dan Asaf ma Mus'ab kallon bukkan,

Duk da bukka ne amma ko mai dake cikin bukkan saf _saf ba bu ko datti ko kaÉ—an a ciki,ga wani kamshin turaren tsinke dake ta shi a ciki,

Katifa ne a cikin É—ak'in sai bargo da aka ajiye akan katifan sain wani dan karamin carpet ma daidaici da aka shimfiÉ—a a kasa,ka san cewa garin akwai sanyi sosai shi ya sa rabuwa da wuta a É—akin,kullun cikin kunna gawayi su ke a É—ak'in.

ÆŠak'in ba karamin burge Asaf ya yi ba,har ya ji zai iya rayuwa a cikin É—ak'in ba tare da ya ji komai ba.

Duk da shi mutun ne da ya tsani Ƙauye amma ya ji wannan Ƙauyen ya bambanta da sauran k'auyukan da yake zuwa,kuma bai san me ya sa ba.

Haka ma bangaren Mus'ab shi ma ba karamin burgesa É—ak'in ya yi ba,É—uk da kuwa shi da ma can ba shi da masa'ala zai iya rayuwa a ko ina,

Jin siriryar murya na yin sallama a bakin kofa ne ya sa shi É—agowa haÉ—e da amsa sallamar da aka yi,

zu ba wa ba kin kofar shiga É—ak'in idanu ya yi yana jiran ya ga mamallakin muryan

Fararen hannunta ta sa ta yaye labulan É—ak'in.

Kanta a kasa ta nufo in da su ke zaune,durkusawa ta yi ta ajiye kwariyar furan a gefen kafarsa,

Idanunta ne ya sauka a kan kafararen kafafunsa sai da ta tsaya ta yi wa kafar kallo na y'en second kafin ta ce "Ina wuninku?"
Chapter 6 · 0% Book details