Sashe 9
Masarautar Gobir Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tun daga wannan rana zama mai farin ciki haɗi da zaman lafiya ya wanzu a gidansu Amadi,duk da wasu lokutan Inna ta kan ɗaure ma Fatimah fuska saboda masu zuga da kan zugata da cewa Fatimah dai ce ta kashe malam ana su tunani duk bai tashi mutuwa ba sai da Fatimah ta shigo gidan a matsayin mata?
Ita kuwa Fatimah da zarar ta ga Inna cikin wannan yanayin sai ta bar mata wajen gaba ɗaya wani sa'in ma gidan su take tafiyarta.
A kwana a tashi asarar mai rai,yau auren su Amadi ya cika shekara guda cur amman shiru kake ji Fatima ko tsallaken wata ba ta taɓa yi ba balle a sa ran ciki.
Wannan batu shi ya dagula lissafin Amadi,tun ya na haƙuri har ya kasa ya ƙara aure inda ya auro wata mata mai suna Hassia.
A budurwa ya aureta, duka-duka ba za ta wuce sa'ar Fatimah ba.Tsohon ɗakin malam ta tare,watan farko Hassia ta fara amai isar su asibiti aka tabbatar da ta na da shigar ciki.Murna gun Amadi ai ba a faɗa,uwa uba Inna wacce duk duniya ba ta da maƙiyiya kamar Fatimah.
Tunda Hassia ta samu cikin nan kullum cikin gori take yi ma Fatimah,ita kuwa baiwar Allah sai dai ta yi kuka ta rarrashi kanta sauƙin abun ma dai dan Amadi na haukan sonta har yanzu.
A wani yammacin juma'a Hassia ta fara naƙuda,Inna ta kaita asibiti babu jimawa Allah ya sauketa lafiya ta haifo ɗanta namiji.Amadi yayi masa huɗuba da sunan Yakubu wato sunan Marigayin malam,har washegari Fatimah ba ta san an yi haihuwar ba saboda ciwon mara da ta tashi.
Kwaramniyan ƴan Barka yasa ta farga da haihuwar,da jan ƙafafu ta isa banɗaki dan watsa ruwa amman kafin ta kai ga shiga jiri ya kwasheta ta faɗi.Amadi wanda tunda aka sallamo su daga asibiti bai fita ba ya yo kanta,da taimakonsa ta miƙe ta na cewa "jiri nake gani ka riƙe ni"Amadi ya ƙwala ma wata yarinya kira yace "je ki taro min taxi"da to ta amsa kafin ta fita,zuwa can ta dawo ta shaida ga mai taxi nan ƙofar gida.
Tambayoyi likita ya fara yi mata kafin a sa mata ledar ruwa,a kwance ta ke Amadi na gefenta fuskar nan fal farin ciki sakamakon albishir ɗin da likita yayi masa Fatimah na ɗauke da ciki.
Lokacin da ta farka Amadi ya shaida mata har da kuka tsabar murna,Innaro wacce ke gefe ma murnar take ita ma za ta ga jikanta.
Amadi ya koma gida ya bar Innaro tayi jinyar ƴarta saboda likita yace sai ta yi traitement na 6days kafin a sallame su duba da yadda jininta ya hau saboda damuwa.
Bayan kwana shidda aka sallamo su,a cike suka tarar da gidan da ƴan biki.
Innaro ta ɗauki robar da kayansu suke ciki yayinda Fatimah ta shige gaba,ta buɗe ɗakinta wanda Amadi ya share sa tsaf ya saka turare.
"Fatimah ki kula da shan magani banda saka damuwa a rai,ki kula da kyau ni zan wuce gida"Innaro ta faɗa kafin tayi ma Fatimah sallama.
Da rana bayan Fatimah ta tashi daga barcin da ya zame mata jiki tayi wanka ta saka sabbin kaya,kuɗi ta ɗauka kafin ta fita zuwa ɗakin Hassia.
Da sallama ta shiga dagin Hassia ne suka amsa ita baya da cije fuska babu abinda ta yi saboda haushin Fatimah da ya ƙaru a zuciyarta jin tana da ciki.
"Ashe Allah ya sauke ki lafiya? To Allah raya kan sunnah ga shi a saya ma baby kwalli "ta miƙa kuɗi yayar Hassia ta karɓa ta yi godiya.
Fatimah ta yi tsaye tana kallon Hassia na shayar da kyakkyawan yaronta,a zuci tace 'Allah sa ni ma yarona yayi kyau kamar wannan,ji yadda yake da kyau kamar aljani'
Jin sallamar Lauriya ya saka Fatimah fitowa suka taɓa kafin su tafi ɓangaren ta,su na tsaka da hira suka jiyo kururuwa Hassia "wayyo Allah na shiga uku na lalace mayya ta lashe min yaro sai bulle-bulle yake wayyo jama'a ku taimaka min"zuciyar Fatimah ce ta fara dakan uku-uku tuni suka fito ita da Lauriya,jariri kuwa sai canyara kuka yake kamar ransa zai fita kafin wani lokaci duk ya wahala jikinsa yayi jajur duk ko ina burdi ne...
★★★ TIBIRIN GOBIR 👑
Duk wani tsarin masarauta Yarima wanda ya kansace sarki a yanzu ya canza su ya ɗora jadawalin rashin mutumcinsa.Kwana uku kacal da hawansa kan karagar mulki al'ummar yankin Tibiri suka gane ashe gata ne Sarki Garba yayi masu,saboda yadda Yarima ya tara mutanen gari ya ɗora dokoki wanda ko a mulkin mallaka sai haka.
Dogari Ɗan Tani wanda ya kasance mai kula da abincin bayi gaba ɗaya na masarauta ba ƙaramin haushi ya ji ba,dama can Sarki Garba ya sakar masa ragamar store tsabar ƙeta ya sa shi rinƙa yiwa bayi wainar fulawa a kullum sai ya na yin ƙasa da faɗi wajen kwashe kayan masarufi.To yanzu kam Sarki Bilal ya ɗora sabon jadawali inda ya zartar da hukunci bayi za'a rinƙa yi masu tuwon jar masara a duk daren Allah,da rana a jiƙa masu kwakwi a barbaɗa ɗan gishi.
Waziri wanda ya kasance aboki ga tsohon Sarki,ya shigo palais ya na mai rusunawa ya kwashi gaisuwa ya na mai cewa "Allah ja da zamanin mai martaba,al'ummar ka na son ganin ka su na can a waje su na ƙus-ƙus akan hukuncin da ka yanke na duk kowane magidanci zai biya kuɗin lanwo ko wacce safiya,su na son a sassauta a mayar da shi ko da duk bayan sati ne "
Sarki Bilal ya miƙe cike da ƙasaita dogarai na take masa baya,waje ya fito inda mutane suka yi cincirindo.
Duk tashi suka yi domin girmamawa ga shugaba,ya gyara tsayuwa haɗi da gyaran murya yace "Sultan ke magana,na ji koken ku sannan na karɓa sai dai ku sani da sharaɗi guda duk wani mutum da ke nan yanki zai bayar da yaro guda domin yin hidima ga masarauta.Abu na gaba da zan shaida maku shine ban yarda wani ko wata ya ɗaga kansa sama ba balle har na ji wani sabon ƙorafi,dogarai ku bi gida-gida ku fito min da yaro ɗaya-ɗaya ku tabbatar kun shiga gidan kowa da ke wannan yankin"ya na gama faɗa ya juya izuwa ciki,jama'ar gari kuwa kamar ruwa ya ci su haka duk suka fita jiki duk a mace yayin da dogarai suka fara aikin da Sultan ya saka su.
A ɓangaren Sarki kuwa banda rikicewa babu abinda ciwonsa ke yi,sai allurai ake yi masa amman ga banza.
Ranar da Prince Khalid ya dawo normal ne ya koma sashen da aka kai Sarki,kallon tsaf yayi masa kafin daga bisani yace "shi yasa ake so a ko wane lokaci mutum ya kasance na ƙwarai,miye ribar ka a yanzu ? Ka raini yaron da ba naka ba ka nuna masa ƙauna ka susuta shi amman yanzu daga ƙarshe ga yadda ya mayar da kai nan"ya tsagaita ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ci gaba "ba zan ce ban sonka ba,saboda kai mahaifina ne sai dai ka sani ka zalunce ni tunda har ka raba ni da abar ƙaunata."
Idon sarki suka ciko taf da ruwa ya na son yin magana sai dai bai iyawa,aka turo ƙofa aka shigo wani dogari ne riƙe da ƙaton gora mai cike da ruwan zam-zam.
Prince Khalid ya karɓa sannan ya shiga toilet ya ɗauro alwala ya shimfiɗa tapis ya zuba ruwan zam-zam ɗin a kofi ya ɗago kofin kusa da bakinsa.
Da Bismillah ya fara sannan ya karanta wannan surorin:
Alfatiha⁷
Falaq³
An Nas³
Al kafirun ³
Ayattul ƙursiyu¹
Amanar Rasuluh²
Ya na gamawa ya je ya buɗe bakin Sarki ya fara ɗiga masa ruwan,har zai aje sauran ruwan kawai sai kuma ya shiga yayafa masa su a jiki.Nan take jikin Sarki ya fara rawa ya na mai jin sassaucin azabar da yake ji,ganin haka ya sa Prince Khalid ɗaura niyyar zuwa maraice zai yi masa ruwan wanka.Waje ya fita ya bai wa wani bawa ƙaton buhu yace ya figo masa ganyen magarya.
Bayan an kawo masa ne ya ta saɓa sa a turmi kafin ya samu bokitin ruwa ya fara karanto surorin da ke karye sihiri kamar haka:
Suratul Fatiha¹¹
Falaq¹¹,Nas¹¹,Kafirun ¹¹
Ayattul ƙursiyu¹¹
Shafin suratul Safat na farko
Suratul Yaseen¹
*Ayoyi daga cikin wasu surori*
Alhqaf Aya ta 31
Al isra Aya ta 82
An nisa Aya ta 54
Ashu'ara Aya ta 80
At tauba Aya ta 14
Fusilat 44
Al hashir Aya ta 21
Al Mulk Aya ta 3
Al Qalam Aya ta 51
Al'araf Aya ta 117 zuwa 199
At tauba Aya ta 26 da kuma ta 40
Al fatahi Aya ta 26, 18,da kuma ta 4
Bayan ya gama karanta wannan ayoyi sai kuma ya ƙara da:
_As'alullahu azhim,rabbal arshil azhim an yashfiyak⁷
_A'uzhu bikalmatillahi tammati min kulli shaitanin wa hammat wa min kulli ainin lammah ³
_Allahumma Rabban nas,adbihil ba'asa ishfi anta ash'shfi laa shifa'ia illa shifa'uka,shifa'an laa yugadiru saqama³
_Hasbiyallahu la'ilaha illa huwa aleyhi tawali'u wa huwa Rabbul arshil azhim ⁷
_Bisimillahi³
_A'uzhu bi'izzatillahi wa ƙudiratihi min sharri ma'ajidu wa'uhazhir
Tsawon lokaci Prince Khalid ya ɗauka ya karance duk wannan ayoyin kafin ya zuba saura a cikin flask na ruwa,sauran kuma wanka ya yiwa sarki a nan inda ya ke kwance kamar yadda aka haramta yin wanka da ruwan da aka yi ma ruƙiya a banɗaki.
Wani irin siraci ke fita daga jikin Sarki kamar tukunyar da aka ɗora kan ruwa,tuni jikinsa ya fara saɓewa daga kumburin da yayi.
"Alhamdullah , Sarki ka ga ikon Allah ko? To ina so daga yau ka cire hannun ka da dukan wasu saɓon Allah ka tuba ka koma garesa shi ɗin mai yafiya ne kuma mai jinƙai"murmushi kan fuskar sarki ya jinjina kai.
Tun daga wannan lokaci Prince Khalid ke kula da mahaifinsa,sosai kuma suke ganin sauƙi dan yanzu sarki ya na iya tashi da kansa haka ya na yin magana saɓanin da.
*BAYAN WANI DOGON ZANGO*
★★★ DUNIYAR IFIRITU
Ita kuwa Fatimah da zarar ta ga Inna cikin wannan yanayin sai ta bar mata wajen gaba ɗaya wani sa'in ma gidan su take tafiyarta.
A kwana a tashi asarar mai rai,yau auren su Amadi ya cika shekara guda cur amman shiru kake ji Fatima ko tsallaken wata ba ta taɓa yi ba balle a sa ran ciki.
Wannan batu shi ya dagula lissafin Amadi,tun ya na haƙuri har ya kasa ya ƙara aure inda ya auro wata mata mai suna Hassia.
A budurwa ya aureta, duka-duka ba za ta wuce sa'ar Fatimah ba.Tsohon ɗakin malam ta tare,watan farko Hassia ta fara amai isar su asibiti aka tabbatar da ta na da shigar ciki.Murna gun Amadi ai ba a faɗa,uwa uba Inna wacce duk duniya ba ta da maƙiyiya kamar Fatimah.
Tunda Hassia ta samu cikin nan kullum cikin gori take yi ma Fatimah,ita kuwa baiwar Allah sai dai ta yi kuka ta rarrashi kanta sauƙin abun ma dai dan Amadi na haukan sonta har yanzu.
A wani yammacin juma'a Hassia ta fara naƙuda,Inna ta kaita asibiti babu jimawa Allah ya sauketa lafiya ta haifo ɗanta namiji.Amadi yayi masa huɗuba da sunan Yakubu wato sunan Marigayin malam,har washegari Fatimah ba ta san an yi haihuwar ba saboda ciwon mara da ta tashi.
Kwaramniyan ƴan Barka yasa ta farga da haihuwar,da jan ƙafafu ta isa banɗaki dan watsa ruwa amman kafin ta kai ga shiga jiri ya kwasheta ta faɗi.Amadi wanda tunda aka sallamo su daga asibiti bai fita ba ya yo kanta,da taimakonsa ta miƙe ta na cewa "jiri nake gani ka riƙe ni"Amadi ya ƙwala ma wata yarinya kira yace "je ki taro min taxi"da to ta amsa kafin ta fita,zuwa can ta dawo ta shaida ga mai taxi nan ƙofar gida.
Tambayoyi likita ya fara yi mata kafin a sa mata ledar ruwa,a kwance ta ke Amadi na gefenta fuskar nan fal farin ciki sakamakon albishir ɗin da likita yayi masa Fatimah na ɗauke da ciki.
Lokacin da ta farka Amadi ya shaida mata har da kuka tsabar murna,Innaro wacce ke gefe ma murnar take ita ma za ta ga jikanta.
Amadi ya koma gida ya bar Innaro tayi jinyar ƴarta saboda likita yace sai ta yi traitement na 6days kafin a sallame su duba da yadda jininta ya hau saboda damuwa.
Bayan kwana shidda aka sallamo su,a cike suka tarar da gidan da ƴan biki.
Innaro ta ɗauki robar da kayansu suke ciki yayinda Fatimah ta shige gaba,ta buɗe ɗakinta wanda Amadi ya share sa tsaf ya saka turare.
"Fatimah ki kula da shan magani banda saka damuwa a rai,ki kula da kyau ni zan wuce gida"Innaro ta faɗa kafin tayi ma Fatimah sallama.
Da rana bayan Fatimah ta tashi daga barcin da ya zame mata jiki tayi wanka ta saka sabbin kaya,kuɗi ta ɗauka kafin ta fita zuwa ɗakin Hassia.
Da sallama ta shiga dagin Hassia ne suka amsa ita baya da cije fuska babu abinda ta yi saboda haushin Fatimah da ya ƙaru a zuciyarta jin tana da ciki.
"Ashe Allah ya sauke ki lafiya? To Allah raya kan sunnah ga shi a saya ma baby kwalli "ta miƙa kuɗi yayar Hassia ta karɓa ta yi godiya.
Fatimah ta yi tsaye tana kallon Hassia na shayar da kyakkyawan yaronta,a zuci tace 'Allah sa ni ma yarona yayi kyau kamar wannan,ji yadda yake da kyau kamar aljani'
Jin sallamar Lauriya ya saka Fatimah fitowa suka taɓa kafin su tafi ɓangaren ta,su na tsaka da hira suka jiyo kururuwa Hassia "wayyo Allah na shiga uku na lalace mayya ta lashe min yaro sai bulle-bulle yake wayyo jama'a ku taimaka min"zuciyar Fatimah ce ta fara dakan uku-uku tuni suka fito ita da Lauriya,jariri kuwa sai canyara kuka yake kamar ransa zai fita kafin wani lokaci duk ya wahala jikinsa yayi jajur duk ko ina burdi ne...
★★★ TIBIRIN GOBIR 👑
Duk wani tsarin masarauta Yarima wanda ya kansace sarki a yanzu ya canza su ya ɗora jadawalin rashin mutumcinsa.Kwana uku kacal da hawansa kan karagar mulki al'ummar yankin Tibiri suka gane ashe gata ne Sarki Garba yayi masu,saboda yadda Yarima ya tara mutanen gari ya ɗora dokoki wanda ko a mulkin mallaka sai haka.
Dogari Ɗan Tani wanda ya kasance mai kula da abincin bayi gaba ɗaya na masarauta ba ƙaramin haushi ya ji ba,dama can Sarki Garba ya sakar masa ragamar store tsabar ƙeta ya sa shi rinƙa yiwa bayi wainar fulawa a kullum sai ya na yin ƙasa da faɗi wajen kwashe kayan masarufi.To yanzu kam Sarki Bilal ya ɗora sabon jadawali inda ya zartar da hukunci bayi za'a rinƙa yi masu tuwon jar masara a duk daren Allah,da rana a jiƙa masu kwakwi a barbaɗa ɗan gishi.
Waziri wanda ya kasance aboki ga tsohon Sarki,ya shigo palais ya na mai rusunawa ya kwashi gaisuwa ya na mai cewa "Allah ja da zamanin mai martaba,al'ummar ka na son ganin ka su na can a waje su na ƙus-ƙus akan hukuncin da ka yanke na duk kowane magidanci zai biya kuɗin lanwo ko wacce safiya,su na son a sassauta a mayar da shi ko da duk bayan sati ne "
Sarki Bilal ya miƙe cike da ƙasaita dogarai na take masa baya,waje ya fito inda mutane suka yi cincirindo.
Duk tashi suka yi domin girmamawa ga shugaba,ya gyara tsayuwa haɗi da gyaran murya yace "Sultan ke magana,na ji koken ku sannan na karɓa sai dai ku sani da sharaɗi guda duk wani mutum da ke nan yanki zai bayar da yaro guda domin yin hidima ga masarauta.Abu na gaba da zan shaida maku shine ban yarda wani ko wata ya ɗaga kansa sama ba balle har na ji wani sabon ƙorafi,dogarai ku bi gida-gida ku fito min da yaro ɗaya-ɗaya ku tabbatar kun shiga gidan kowa da ke wannan yankin"ya na gama faɗa ya juya izuwa ciki,jama'ar gari kuwa kamar ruwa ya ci su haka duk suka fita jiki duk a mace yayin da dogarai suka fara aikin da Sultan ya saka su.
A ɓangaren Sarki kuwa banda rikicewa babu abinda ciwonsa ke yi,sai allurai ake yi masa amman ga banza.
Ranar da Prince Khalid ya dawo normal ne ya koma sashen da aka kai Sarki,kallon tsaf yayi masa kafin daga bisani yace "shi yasa ake so a ko wane lokaci mutum ya kasance na ƙwarai,miye ribar ka a yanzu ? Ka raini yaron da ba naka ba ka nuna masa ƙauna ka susuta shi amman yanzu daga ƙarshe ga yadda ya mayar da kai nan"ya tsagaita ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ci gaba "ba zan ce ban sonka ba,saboda kai mahaifina ne sai dai ka sani ka zalunce ni tunda har ka raba ni da abar ƙaunata."
Idon sarki suka ciko taf da ruwa ya na son yin magana sai dai bai iyawa,aka turo ƙofa aka shigo wani dogari ne riƙe da ƙaton gora mai cike da ruwan zam-zam.
Prince Khalid ya karɓa sannan ya shiga toilet ya ɗauro alwala ya shimfiɗa tapis ya zuba ruwan zam-zam ɗin a kofi ya ɗago kofin kusa da bakinsa.
Da Bismillah ya fara sannan ya karanta wannan surorin:
Alfatiha⁷
Falaq³
An Nas³
Al kafirun ³
Ayattul ƙursiyu¹
Amanar Rasuluh²
Ya na gamawa ya je ya buɗe bakin Sarki ya fara ɗiga masa ruwan,har zai aje sauran ruwan kawai sai kuma ya shiga yayafa masa su a jiki.Nan take jikin Sarki ya fara rawa ya na mai jin sassaucin azabar da yake ji,ganin haka ya sa Prince Khalid ɗaura niyyar zuwa maraice zai yi masa ruwan wanka.Waje ya fita ya bai wa wani bawa ƙaton buhu yace ya figo masa ganyen magarya.
Bayan an kawo masa ne ya ta saɓa sa a turmi kafin ya samu bokitin ruwa ya fara karanto surorin da ke karye sihiri kamar haka:
Suratul Fatiha¹¹
Falaq¹¹,Nas¹¹,Kafirun ¹¹
Ayattul ƙursiyu¹¹
Shafin suratul Safat na farko
Suratul Yaseen¹
*Ayoyi daga cikin wasu surori*
Alhqaf Aya ta 31
Al isra Aya ta 82
An nisa Aya ta 54
Ashu'ara Aya ta 80
At tauba Aya ta 14
Fusilat 44
Al hashir Aya ta 21
Al Mulk Aya ta 3
Al Qalam Aya ta 51
Al'araf Aya ta 117 zuwa 199
At tauba Aya ta 26 da kuma ta 40
Al fatahi Aya ta 26, 18,da kuma ta 4
Bayan ya gama karanta wannan ayoyi sai kuma ya ƙara da:
_As'alullahu azhim,rabbal arshil azhim an yashfiyak⁷
_A'uzhu bikalmatillahi tammati min kulli shaitanin wa hammat wa min kulli ainin lammah ³
_Allahumma Rabban nas,adbihil ba'asa ishfi anta ash'shfi laa shifa'ia illa shifa'uka,shifa'an laa yugadiru saqama³
_Hasbiyallahu la'ilaha illa huwa aleyhi tawali'u wa huwa Rabbul arshil azhim ⁷
_Bisimillahi³
_A'uzhu bi'izzatillahi wa ƙudiratihi min sharri ma'ajidu wa'uhazhir
Tsawon lokaci Prince Khalid ya ɗauka ya karance duk wannan ayoyin kafin ya zuba saura a cikin flask na ruwa,sauran kuma wanka ya yiwa sarki a nan inda ya ke kwance kamar yadda aka haramta yin wanka da ruwan da aka yi ma ruƙiya a banɗaki.
Wani irin siraci ke fita daga jikin Sarki kamar tukunyar da aka ɗora kan ruwa,tuni jikinsa ya fara saɓewa daga kumburin da yayi.
"Alhamdullah , Sarki ka ga ikon Allah ko? To ina so daga yau ka cire hannun ka da dukan wasu saɓon Allah ka tuba ka koma garesa shi ɗin mai yafiya ne kuma mai jinƙai"murmushi kan fuskar sarki ya jinjina kai.
Tun daga wannan lokaci Prince Khalid ke kula da mahaifinsa,sosai kuma suke ganin sauƙi dan yanzu sarki ya na iya tashi da kansa haka ya na yin magana saɓanin da.
*BAYAN WANI DOGON ZANGO*
★★★ DUNIYAR IFIRITU