Sashe 3
Masarautar Gobir Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tun daga ƙafafunta wanda suka sha lallen Hausa ya fara bi da ido har izuwa fuskarta wacce aka yi ma simple kwalliya,kai ya fara gyaɗawa kamar wani ƙadangare kafin ya yiwa Jakadiya alamu da ido ta fita.
Fitar ta ke da wuya Yarima ya miƙa ma Maryam hannu alamun ta tawo,jikinta ne ya fara rawa duk da cewa tun kafin su shigo an yi mata bayanin komi.
Wani irin fizgota yayi ta faɗa jikinsa ya lumshe ido ya na shaƙar ƙamshin turarenta wanda ya san aikin Jakadiya ne,shafar ta ya fara yi gami da aika mata saƙonni a ɓangarori mafi daraja a jikin mace.
★★★ MADARUMFA
Kwalokwalo(jirgin ruwa) ya gyara ma zama kafin mutane su fara shiga shi kuwa gefe ya koma ya na kallon wata bafulatana ta kasa shiga tsabar tsoro.
Ya gyara tsayuwa ya na ƙara kallon ikon Allah yadda bafulatanar nan ta ke shiga jirgi sai ta zauna sai kuma ta fito ta na zarar ido, murmurshi yayi a zuci yace "ashe dai dagaske ne Fulani sokwaye ne,yanzu miye a cikin jirgin ruwa da har ta ke tsoro?"
Maganar waɗanda suke tare da ita ne ta katse zancen zucin Amadi, "Fatimah ki shigo ki zauna kin ga saura mutum biyu kawai jirgin ya cika kuma in wasu suka zo shikenan za mu bar ki a nan"Lauriya ke faɗa yayin da sauran suke kallon wacce aka kira da Fatimah suna masu haɗin baki wajen cewa "ki shigo dan Allah"
Fatima ta maƙe kafaɗa tace "aradun Allah ba zan higa ba,wannan ai mun yi mashi yawa sai ya nutse da mu cikin ruwan"
Dariya Amadi ya ɓarke da ita yace "halan daga ƙauye kike?" Fatimah ta waigo bayanta ta na mai dubansa wanda shi ɗin ma ita ya ke kallo.
"Daga ƙarƙashin ƙasa na ke"ta bashi amsa cikin jin haushi kafin ta daure ta shiga jirgin,duk da maganar ta yi ma Amadi zafi hakan bai sa ya fusata ba sai ma cewa yayi "to madallah zan tabbatar"ya na gama faɗa shi ma ya shiga jirgin ya na mai tsoma muciyar da suke tuƙi da ita cikin ruwa .
A sannu suka fara tafiya cikin tabkeken tabkin,ba ka jin komi sai kukan tsuntsaye da ƙwari,iska mai haɗe da sanyi da ƙamshin ruwa sai kaɗawa ta ke.
Sun zo daidai tsakiya Fatima ta ji tamkar ana yafito ta,cike da tsoro ta buɗe idonta wanda ta rufe tun farkon soma tafiyar su ai kuwa kamar walƙiya haka ta ga wani abu "wuuul!"ta cikin ruwa babu zato ba tsammani sai jinta tayi ta faɗa canɓal cikin ruwan.
Ihu su Lauriya suka fara yayin da Amadi ke gumtse dariyarsa,can kuma ya tsayar da jirgin haɗi da ce ma wani namiji "ka ida fitar da ku,ni zan shiga na cirota"ba tare da wani jinkiri ba ya faɗa "tsumbul".
Ko da suka isa gaɓar ruwa duk cirko-cirko suka yi su na kuka ganin har yanzu babu labarin Amadi balle Fatimah.
Tsawon lokaci kafin su tsinkayi Amadi saɓe da Fatimah a hannu kamar wata jaririya,a ƙasa ya kwantar da ita dogon gashinta wanda ya warware ya baje a ƙasa yayin da kayan Fulanin ta suka jiƙe sharkaf.
Cikinta ya shiga dannawa ruwa na ta ɓulbulowa daga hancinta,bakinsa ya sa a nata bayan ya matse hancinta ya hura iska.
Da sauri ya janye jin ruwan da ta sha sun shiga bakin sa,tari ta soma sosai ta lumsar ido kamar wacce ta yi maye gabanin ta fara kallon mutanen gun da suka taru su na yi mata sannu.
"Sannu Fatimah,ya kike jin kan ki yanzu?"Lauriya ta tambaya cike da tausayi,kawar da kai ta yi gefe ta na mai tashi tsaye ta na son tuna abin da ya faru da ita lokacin da ta faɗa cikin ruwan.
Amadi yayi murmurshi yace "ƴar fullo ko zaki koma inda kika baro ne"da sauri ta kalle sa nan take jikinta ya hau tsuma a guje ta arta da gudu ƴan uwanta suka shiga kiranta Amadi kuwa sai dariyar ƙeta ya ke kwasa.
Fatimah ba ta zarce ko ina ba sai gidan Abdu wanda dama can sukan je kafin zuwan gulbi,Nana matar Abdu ta fito jin an shigo a guje.
"Fatimah?lafiya daga ina kike?waye ya biyo ki haka a guje?"Nana ta jera mata tambayoyin,Lauriya ce ta bata amsa "ruwa ta faɗa sai da mai jirgin ya shiga ya tsamota,shine fah mafarin gudun"Hannuwa Nana ta fara taɓawa ta na salalami kafin ta yi masu iso zuwa cikin ɗaki.
Sai yamma lis sannan su Fatimah suka baro gidan Nana,wannan karon zagaye suka yi ba su bi ta gulbi ba dan kuwa aradun Allah wacce Fatimah ta ja a kan ba za ta shiga jirgin ruwa ba ta cika buhu.
Amadi bawon Allah tun ya na zuba ido ya ga dawowar su Fatima har ya haƙura ya nufi gida.
Tun a bakin ƙofa ya ke jin ihun wani ƙaton saurayi,tsuki yayi a fili ya furta "aikin kenan kullum cikin ihu kamar gidan mahaukata mtws...kawai an mayar mana da gida faɗar cirar aljanu"
"Amadi tare min shi kar ya fice"cewar Malam mahaifi ga Amadi,babu yadda ya iya haka ya tare saurayin ya riƙe sa tamau kamar ɗaurin goro.Har cikin ɗakin da Malam ke Ruƙiya Amadi ya kai wannan saurayi,cikin daka tsawa yace "zauna nan kuma in ka saki ka fita sai na gundile ma kai,bari ganin ka na da Jinnu to na bisa kaina sun fi ƙarfin naka"abu kamar almara haka saurayin nan ya lafe waje guda ya na kallon Amadi fuskarsa ƙarara tsoro.
Malam yayi murmushi yace "yawwa Amadina gwara da ka gargaɗe sa na san kuwa in ba ni nace ya fita ba to fah babu inda zai je"Amadi yace "to Malam in ba abun ka ba waye bai tsoron Tabarno,su kansu aljanun yanzu tsorona suke"cike da murna Malam ya kuma cewa "shi yasa nake ma kwaɗayin shiga sahun maluman Ruƙiya"ɗif fara'ar fuskar Amadi ta ɗauke yace "haba Malam sai kace dan aljanu mu ka zo duniya?a bar ni da iya sarautar Sarkin ruwa"Malam bai ce komi ba saboda haushi dan ya jima ya na son saka yaron nasa harakar cire ma mutane Jinnu duba da yadda ya ke da ilimi sosai ga kuma wata baiwa da aljanun ruwa suka bashi.
Alwala sallar magrib Amadi yayi kafin ya wuce masjid,ko da ya dawo ya tarar da Inna ta zuba masa abinci.
Kan tabarmar kaba ya zauna ya tanƙwashe ƙafafunsa kafin ya jawo langar tuwon dawa, Bismillah yayi ya ɗibi abinci zai kai baki kwatsam sai Fatimah ta faɗo masa a rai.
Lomar tuwon ya mayar ya na mai sakin murmushi ya dubi Inna wacce ita ma shi ta ke kallo "Inna albishirin ki?"
"Goro"cewar Inna, Amadi yace "na samu matar aurena, bafulatanar da na ke baki labari ta na zo min cikin mafarki to yau dai kam na gan ta a zahiri"
Inna tace "Amadi ban son shirmen banza,ta ya aka yi ka gane ita ce ?"ya ɓata fuska yace "Allah Inna ita ce,dan tabbatarwa har masarauta na kai ta" "wace masarauta?"Inna ta tambaya ta na mai ƙure sa da ido,ƙeya ya sosa da alamu yayi suɓul da baka kawai sai ya jawo abinci ya fara ci.
Sai da ya ci ya ƙoshi sannan ya miƙe,hannu ya wanke ya cika moɗa da ruwa ya shanye kafin ya shiga ɗakinsa.
Wata ƙwarya ya fiddo daga ƙarƙashin gado mai cike da ruwa,iskan bakinsa ya hura ruwan suka rausaya kafin hoton fuskarta ya bayyana a ciki ƙwaryar na ɗaukar wani irin haske kamar an saka fitila.
Kwance take sanye da kayan Fulani farfaru,gashin kanta a warware duk ya zuba kan jikin Innaro wacce ke shafa mata ɗanyen man shanu a kai.
Murmurshi Amadi ya saki daga nan ya hura iska gashin kanta wanda ya rufe gefen fuskarta ya ɗan tashi sama,wata zabura ta yi ta tashi zaune Amadi kuwa kallonta kawai ya ke.
Ɗif hasken ya mutu sakamakon shigowa da Inna ta yi,da sauri ya mayar da ƙwaryar kafin ya maido hankalinsa ga Inna wacce ke yi masa kallon tuhuma.
"Amadi tsafi kake?kenan har yanzu ba ka bar wannan rufa idon ba?"Inna ta tambaya murya na ɗan rawa.
Cikin alamu na maras gaskiya yace "a'a fah Inna kawai baiwa ce Allah ya bani,kuma ke da kan ki kin faɗa kin ce tun ina ɗan yaro nake abubuwan mamaki"Inna ba ta sake cewa komi ba ta fice daga ɗakin.
★★★ MARADI
Fitar ta ke da wuya Yarima ya miƙa ma Maryam hannu alamun ta tawo,jikinta ne ya fara rawa duk da cewa tun kafin su shigo an yi mata bayanin komi.
Wani irin fizgota yayi ta faɗa jikinsa ya lumshe ido ya na shaƙar ƙamshin turarenta wanda ya san aikin Jakadiya ne,shafar ta ya fara yi gami da aika mata saƙonni a ɓangarori mafi daraja a jikin mace.
★★★ MADARUMFA
Kwalokwalo(jirgin ruwa) ya gyara ma zama kafin mutane su fara shiga shi kuwa gefe ya koma ya na kallon wata bafulatana ta kasa shiga tsabar tsoro.
Ya gyara tsayuwa ya na ƙara kallon ikon Allah yadda bafulatanar nan ta ke shiga jirgi sai ta zauna sai kuma ta fito ta na zarar ido, murmurshi yayi a zuci yace "ashe dai dagaske ne Fulani sokwaye ne,yanzu miye a cikin jirgin ruwa da har ta ke tsoro?"
Maganar waɗanda suke tare da ita ne ta katse zancen zucin Amadi, "Fatimah ki shigo ki zauna kin ga saura mutum biyu kawai jirgin ya cika kuma in wasu suka zo shikenan za mu bar ki a nan"Lauriya ke faɗa yayin da sauran suke kallon wacce aka kira da Fatimah suna masu haɗin baki wajen cewa "ki shigo dan Allah"
Fatima ta maƙe kafaɗa tace "aradun Allah ba zan higa ba,wannan ai mun yi mashi yawa sai ya nutse da mu cikin ruwan"
Dariya Amadi ya ɓarke da ita yace "halan daga ƙauye kike?" Fatimah ta waigo bayanta ta na mai dubansa wanda shi ɗin ma ita ya ke kallo.
"Daga ƙarƙashin ƙasa na ke"ta bashi amsa cikin jin haushi kafin ta daure ta shiga jirgin,duk da maganar ta yi ma Amadi zafi hakan bai sa ya fusata ba sai ma cewa yayi "to madallah zan tabbatar"ya na gama faɗa shi ma ya shiga jirgin ya na mai tsoma muciyar da suke tuƙi da ita cikin ruwa .
A sannu suka fara tafiya cikin tabkeken tabkin,ba ka jin komi sai kukan tsuntsaye da ƙwari,iska mai haɗe da sanyi da ƙamshin ruwa sai kaɗawa ta ke.
Sun zo daidai tsakiya Fatima ta ji tamkar ana yafito ta,cike da tsoro ta buɗe idonta wanda ta rufe tun farkon soma tafiyar su ai kuwa kamar walƙiya haka ta ga wani abu "wuuul!"ta cikin ruwa babu zato ba tsammani sai jinta tayi ta faɗa canɓal cikin ruwan.
Ihu su Lauriya suka fara yayin da Amadi ke gumtse dariyarsa,can kuma ya tsayar da jirgin haɗi da ce ma wani namiji "ka ida fitar da ku,ni zan shiga na cirota"ba tare da wani jinkiri ba ya faɗa "tsumbul".
Ko da suka isa gaɓar ruwa duk cirko-cirko suka yi su na kuka ganin har yanzu babu labarin Amadi balle Fatimah.
Tsawon lokaci kafin su tsinkayi Amadi saɓe da Fatimah a hannu kamar wata jaririya,a ƙasa ya kwantar da ita dogon gashinta wanda ya warware ya baje a ƙasa yayin da kayan Fulanin ta suka jiƙe sharkaf.
Cikinta ya shiga dannawa ruwa na ta ɓulbulowa daga hancinta,bakinsa ya sa a nata bayan ya matse hancinta ya hura iska.
Da sauri ya janye jin ruwan da ta sha sun shiga bakin sa,tari ta soma sosai ta lumsar ido kamar wacce ta yi maye gabanin ta fara kallon mutanen gun da suka taru su na yi mata sannu.
"Sannu Fatimah,ya kike jin kan ki yanzu?"Lauriya ta tambaya cike da tausayi,kawar da kai ta yi gefe ta na mai tashi tsaye ta na son tuna abin da ya faru da ita lokacin da ta faɗa cikin ruwan.
Amadi yayi murmurshi yace "ƴar fullo ko zaki koma inda kika baro ne"da sauri ta kalle sa nan take jikinta ya hau tsuma a guje ta arta da gudu ƴan uwanta suka shiga kiranta Amadi kuwa sai dariyar ƙeta ya ke kwasa.
Fatimah ba ta zarce ko ina ba sai gidan Abdu wanda dama can sukan je kafin zuwan gulbi,Nana matar Abdu ta fito jin an shigo a guje.
"Fatimah?lafiya daga ina kike?waye ya biyo ki haka a guje?"Nana ta jera mata tambayoyin,Lauriya ce ta bata amsa "ruwa ta faɗa sai da mai jirgin ya shiga ya tsamota,shine fah mafarin gudun"Hannuwa Nana ta fara taɓawa ta na salalami kafin ta yi masu iso zuwa cikin ɗaki.
Sai yamma lis sannan su Fatimah suka baro gidan Nana,wannan karon zagaye suka yi ba su bi ta gulbi ba dan kuwa aradun Allah wacce Fatimah ta ja a kan ba za ta shiga jirgin ruwa ba ta cika buhu.
Amadi bawon Allah tun ya na zuba ido ya ga dawowar su Fatima har ya haƙura ya nufi gida.
Tun a bakin ƙofa ya ke jin ihun wani ƙaton saurayi,tsuki yayi a fili ya furta "aikin kenan kullum cikin ihu kamar gidan mahaukata mtws...kawai an mayar mana da gida faɗar cirar aljanu"
"Amadi tare min shi kar ya fice"cewar Malam mahaifi ga Amadi,babu yadda ya iya haka ya tare saurayin ya riƙe sa tamau kamar ɗaurin goro.Har cikin ɗakin da Malam ke Ruƙiya Amadi ya kai wannan saurayi,cikin daka tsawa yace "zauna nan kuma in ka saki ka fita sai na gundile ma kai,bari ganin ka na da Jinnu to na bisa kaina sun fi ƙarfin naka"abu kamar almara haka saurayin nan ya lafe waje guda ya na kallon Amadi fuskarsa ƙarara tsoro.
Malam yayi murmushi yace "yawwa Amadina gwara da ka gargaɗe sa na san kuwa in ba ni nace ya fita ba to fah babu inda zai je"Amadi yace "to Malam in ba abun ka ba waye bai tsoron Tabarno,su kansu aljanun yanzu tsorona suke"cike da murna Malam ya kuma cewa "shi yasa nake ma kwaɗayin shiga sahun maluman Ruƙiya"ɗif fara'ar fuskar Amadi ta ɗauke yace "haba Malam sai kace dan aljanu mu ka zo duniya?a bar ni da iya sarautar Sarkin ruwa"Malam bai ce komi ba saboda haushi dan ya jima ya na son saka yaron nasa harakar cire ma mutane Jinnu duba da yadda ya ke da ilimi sosai ga kuma wata baiwa da aljanun ruwa suka bashi.
Alwala sallar magrib Amadi yayi kafin ya wuce masjid,ko da ya dawo ya tarar da Inna ta zuba masa abinci.
Kan tabarmar kaba ya zauna ya tanƙwashe ƙafafunsa kafin ya jawo langar tuwon dawa, Bismillah yayi ya ɗibi abinci zai kai baki kwatsam sai Fatimah ta faɗo masa a rai.
Lomar tuwon ya mayar ya na mai sakin murmushi ya dubi Inna wacce ita ma shi ta ke kallo "Inna albishirin ki?"
"Goro"cewar Inna, Amadi yace "na samu matar aurena, bafulatanar da na ke baki labari ta na zo min cikin mafarki to yau dai kam na gan ta a zahiri"
Inna tace "Amadi ban son shirmen banza,ta ya aka yi ka gane ita ce ?"ya ɓata fuska yace "Allah Inna ita ce,dan tabbatarwa har masarauta na kai ta" "wace masarauta?"Inna ta tambaya ta na mai ƙure sa da ido,ƙeya ya sosa da alamu yayi suɓul da baka kawai sai ya jawo abinci ya fara ci.
Sai da ya ci ya ƙoshi sannan ya miƙe,hannu ya wanke ya cika moɗa da ruwa ya shanye kafin ya shiga ɗakinsa.
Wata ƙwarya ya fiddo daga ƙarƙashin gado mai cike da ruwa,iskan bakinsa ya hura ruwan suka rausaya kafin hoton fuskarta ya bayyana a ciki ƙwaryar na ɗaukar wani irin haske kamar an saka fitila.
Kwance take sanye da kayan Fulani farfaru,gashin kanta a warware duk ya zuba kan jikin Innaro wacce ke shafa mata ɗanyen man shanu a kai.
Murmurshi Amadi ya saki daga nan ya hura iska gashin kanta wanda ya rufe gefen fuskarta ya ɗan tashi sama,wata zabura ta yi ta tashi zaune Amadi kuwa kallonta kawai ya ke.
Ɗif hasken ya mutu sakamakon shigowa da Inna ta yi,da sauri ya mayar da ƙwaryar kafin ya maido hankalinsa ga Inna wacce ke yi masa kallon tuhuma.
"Amadi tsafi kake?kenan har yanzu ba ka bar wannan rufa idon ba?"Inna ta tambaya murya na ɗan rawa.
Cikin alamu na maras gaskiya yace "a'a fah Inna kawai baiwa ce Allah ya bani,kuma ke da kan ki kin faɗa kin ce tun ina ɗan yaro nake abubuwan mamaki"Inna ba ta sake cewa komi ba ta fice daga ɗakin.
★★★ MARADI