Sashe 6
Masarautar Gobir Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tashin hankali maras misaltuwa ya shigi Amadi, Fatimah ma haka dan kusan ma ta fi shi damuwa.
Amadi ne zaune gaban gaɓar ruwa jikinsa babu kaya tumɓur yake haihuwar uwarsa,idonsa a lumshe ya na motsa bakinsa.A sannu a hankali ruwan suka fara tunkuɗowa suna zuwa gunsa har ya zama sun kai shi can tsakiyar gulbin,wani haske ya gewaye shi mai kama da garwashin wuta kafin wata murya ta fara yi masa magana kamar haka ```baƙar akuya mai gemu,jajayen bunsuru biyu sai budurwa kaza wacce ba ta taɓa yin ƙwai ba.Ka yanka su ka zubar da jinin cikin gulbin mawaliya```
Kamar walƙiya sai kuma ruwan suka janye suka koma inda suke,Amadi ya tashi ya ɗauki kayansa da ya maida sannan ya wuce gida.
Washegari gari kuwa Amadi ya bazama cikin kasuwa ya sawo abubuwan da aljan
nunsa suka buƙata,zuwansa gida ke da wuya ya yanke su kaf bayan ya tara ƙwarya jinin ya zuba a ciki.
Duk abin da yake Inna na kallonsa sai dai ita zuwa yanzu al'amarin Amadi tsoro yake bata,Amadi bai taushe hannu ba ya isa gulbin mawaliya ya zuba jinin.Da farko jinin sama ya yi ya takure gu ɗaya kafin daga bisani a fara jansa zuwa ƙasa kamar yadda yaro ke shan daddaɗar madara.
Wani gurnani haɗi da nishi ya taso daga ƙasan ruwan can kuma ya ɗauke,ganin haka Amadi ya nufi gida.
Mutane ya tarar ƙofar gida sun yi cirko-cirko ana leƙen gidansu kafin a juyo duk ana kallon sa.......
[07/09 à 07:40] MRS SADAUKI 👑M~SHURAIM🤍: *MASARAUTAR GOBIR*
LoVe and HoRoR StOrY
*Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo
(MRS SADAUKI💫✍️)
*Lambar waya:* +22795045822
*FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️*
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation.
*Sadaukar wa:* Ga duk Gobirawan duniya.
_____________________
7-8
Ko kafin Amadi ya kai ga tambayar lafiya,Innaro wato mahaifiya ga Fatimah ta kuma sakin wani ihun ta na suratai maras kan gado yayin da kuma ta ke tiƙar rawa irin yadda ƴan bori su ke yi.
Wani sanyi ne ya ratsa zuciyar Amadi,da farko ya ji tsoro kar ace Malam ko Inna aka ɗauka matsayin sacrifice kasancewar lokacin da zai bayar da jinin da yayi alƙawari ya gabato.
Cikin gidan ya wuce tare da samun waje ya zauna ya na kallon yadda Innaro ta rasa hankalinta lokaci guda ba tare da ta shirya ba,a idon mutane aljanu ne suke ganin ta na da amman wurin Amadi shi ya san haukacewa ne ta yi.
"Innaro je ki zauna"Amadi ya faɗa cikin bayar da umarni,cak ta tsaya da rawar sai kuma dare-dare irin na sabon kamu.
Innuwa ta samu ta zauna,a zuci Amadi yace 'au !haukan bai gama rufe ki ba tunda har kin san banbancin innuwa da kuma rana'
Inna ta leƙo ta na mai ɓoyewa bayan ƙyauren ɗakinta,ta na tsinkayar Amadi ta ƙwala masa kira ya taso ya na ƙumshe dariya ganin Inna ta ɓoye a ɗaki har da saka sakata tsabar tsoro.
Ya na zuwa tace "dan Allah ka taimaka kace ta tafi gida, wannan masifa da mi ta yi kama mu na zaman zamanmu ka ɗebo mana fitina"
Amadi yace "Ni kuma?"Inna ta harare sa tace "eh kai ɗin ko ka zata ban san aikin ka ne ba?"Amadi ya sosa ƙeya kafin yaje gun inda Innaro ta ke.
Duƙawa yayi ya fara magana "Innaro kin yarda da auren mu ni da Fatimah ko kuwa?"da sauri ta gyaɗa kai shi kuma ya saki murmushi yace "to tashi ki tafi gida"kamar wata doluwa haka ta yunƙura ta tashi tare da fita waje ba ta zame ko ina ba sai gidanta nan ta tarar da Fatimah da Abdu.
Da sauri ya nufota ya na tambayar ta "Innaro lafiya?na zo na tarar Fatimah na kuka,ke kuma ba kya nan yanzu da kika dawo kayan ki duk sun yi dauɗa?"
Innaro ba tace komi ba ta wuce ɗaki,Abdu ya take mata baya.Ko kafin ya sake yin wata magana tace "maganar auren Fatimah a fara shiri,ban so ya haura sati biyu a kaita kowa ya huta"cike da mamaki Abdu ya kalleta yace "haba Innaro matsafin za mu bai wa aure?"Inna ta yi masa daƙuwa kafin tace "gidan uban wa ka ga yayi tsafin?kawai sharrin mahasada ne dan sun ga duk illahirin garin nan babu mai maganin aljanu kamar sa"
Abdu ya yi ajiyar zuciya kafin yace "to Allah kyauta"Innaro ta amsa masa da "amen" ta na mai bin bayansa da harare a zuci ta na cewa 'Ni ai nafi kowa sanin matsafi ne ,ni da ya turo ma ciwon hauka da rana tsaka duk da na ƴan mintina ne amman ai na wahala'
Fatimah wacce ke waje duk ta ji hirar da suka zanta,cike da murna ta cika bokiti da ruwa ta kai ma Innaro banɗaki kafin ta ɗaga labule tace "ki tasho kiyi wanka na kai maki ruwa"kai ta gyaɗa mata alamar toh kafin a zuci tace 'muguwa ai doli ki kai min ruwa tunda kin kwaso mana masifa mu na zaman-zamanmu'Innaro na shiga bayi Fatimah ta arce ba ta zame ko ina ba sai gidansu Amadi.
Da sallama a bakinta sai dai babu kowa sai kukan wani maras lafiya mai cutar Jinnu da aka kawo ma malam,har za ta fito sai ta tsinkayi riga da wando rataye a katangar banɗaki.
Fatimah ta saki murmushi ta nufi ɗakin Amadi domin jiransa,ba ta wani daɗe da zama ba ya shigo.Kanta sunne a ƙasa ba tare da gaisuwa ba tace "Innaro ta amince da aurenmu shine nace bari na zo na faɗa ma"
Amadi yayi murmushi yace "ai na sani,yanzu haka wankan zuwa gidan ku ne na yi amman tunda ga ki kin zo mu je kawai gaɓar ruwa"
Babu wani muso ta miƙe tsaye ta bi bayansa,su na tafe su na hirar soyayya har suka kawo gaɓar ruwa.
Amadi ya ɗauki ƙanƙara ya jefa a ciki ta bada sautin "tsulum"can sai ga kifi ya fito daidai inda babu ruwa ya na motsi,Amadi ya duƙa ya ɗauki ƙaton kifin kafin ya koma gefe ya cire masa wuya.Wuta ya hura ya fara gasa kifin,ita dai Fatimah na gefe ta na kallon siddabarun Amadi kala-kala.
Cike da burgewa ta ƙaraso gun sa,cikin muryata ta Fulani tace "yanzu in nace sai ka mayar da kifin nan ɗanye ya za ka yi?"Amadi wanda ke ƙoƙarin juya kifin dan ya fara gasuwa ya ɗago ya dubeta yace "tsaf zan maidosa ɗanye kuma da ransa"Fatimah ta waro ido tace "da gaske?"ya jinjina mata kai.Ta rufe baki da dukan hannuwanta kafin tace "to mayar na gani"wata formula Amadi ya faɗa nan take kifin da ke kan wuta yayi tsul ya faɗi a ƙasa ya dawo ɗanye har ya na motsi.Fatimah ta waro ido tace "to mayar da shi gasashe"ko ida rufe bakinta ba ta yi ba kifin ya koma yadda ya ke a gashe bisa garwashi.
Ganin yadda Fatimah ta shiga nishaɗi yasa Amadi mayar da abun wasa sai kifin ya gasu sai kuma ya mayar da shi ɗanye ita kuwa wawiya sai dariya ta ke saboda ita ba ta ganin dogon hannun da ke yin masanyar kifin balle ta farga da rufa ido ake yi mata.
★★★ MARADI
"Ta ya aka yi kika shigo rayuwata ba tare da na shirya ba?"Yarima ya tambaya bayan ya hau kan gadon da Saffa take zaune a tsakiya.
"Ta yadda ka yaudare ni kace za ka sa Prince Khalid ya so ni bayan na ci amanar ƴar uwata"Saffa ta basa amsa
"Ban yaudare ki ba,akasi aka samu ko da na farka ban ga Marwa ba sannan sai naji wai an shirya hidimar auren mu"Yarima ya faɗa,Saffa ta taɓe baki tace "dama ranar da Amma ta zo sashen mu na yi mafarkin haka,ƙaddara za ta raba mu kuma za mu sake kasancewa a tare sai dai ban san tsawon wane lokaci hakan za ta faru ba"
"Ko da ta dawo nan to za ta zo ne a ƙuraren lokaci,saboda sai bayan Yarima ya hau karagar mulkin da ta ke tamaƙa za ta ɗora wanin Yarima"murya Amma ta daki kunnuwansu duk sai suka waigowa su na kallonta cike da mamaki saboda sun kulle ƙofa ta yaya ta shigo kenan?
Amma ta saki murmushi tace "da zarar kun raya daren farkon ku to wannan tsohon banzar zai sabka daga karagar mulki kai kuma Yarima ka hau"a zafafe Yarima ya yo kan Amma ya ɗaga hannu zai sharara mata mari ta riƙe hannunsa ta na "kul!kul!Kar ka soma taɓa fuskar nan yin haka zai sa ka samu tsinuwar Mala'iku saboda wannan fuskar ta mahaifiyar ka ce"
"Mahaifiya?"Yarima ya maimaita kalmar ,Amma ta juya baya tace "tabbas Yarima kai Ɗana ne,na jima ina jiran wannan ranar wacce za ta zo na fasa ƙwan" sam Yarima bai samu bakin magana ba sai Saffa ce ta tambayi Amma "ta yaya kika zamo mahaifiyarsa?sannan shi kuma Prince Khalid fah?"
Amma tace "labari ne mai tsayi,yanzu dai zan barku domin raya wannan daren zan koma sashena jiran har izuwa lokacin da zan ji an buga tamburan juyin mulki"ta na gama faɗa ta fice ba tare da ta jira cewar su ba.
Saffa ta dafa Yarima tace "tabbas biri yayi kama da mutum,sai yanzu na ida fahimtar mi yasa Amma ba ta son Prince Khalid ya auri Marwa" Yarima ya dubeta yace "mi kika gane?"ba ta basa amsa ba ta fara tura masa saƙon da ya zautar shi izuwa raya daren farkon su.
Amadi ne zaune gaban gaɓar ruwa jikinsa babu kaya tumɓur yake haihuwar uwarsa,idonsa a lumshe ya na motsa bakinsa.A sannu a hankali ruwan suka fara tunkuɗowa suna zuwa gunsa har ya zama sun kai shi can tsakiyar gulbin,wani haske ya gewaye shi mai kama da garwashin wuta kafin wata murya ta fara yi masa magana kamar haka ```baƙar akuya mai gemu,jajayen bunsuru biyu sai budurwa kaza wacce ba ta taɓa yin ƙwai ba.Ka yanka su ka zubar da jinin cikin gulbin mawaliya```
Kamar walƙiya sai kuma ruwan suka janye suka koma inda suke,Amadi ya tashi ya ɗauki kayansa da ya maida sannan ya wuce gida.
Washegari gari kuwa Amadi ya bazama cikin kasuwa ya sawo abubuwan da aljan
nunsa suka buƙata,zuwansa gida ke da wuya ya yanke su kaf bayan ya tara ƙwarya jinin ya zuba a ciki.
Duk abin da yake Inna na kallonsa sai dai ita zuwa yanzu al'amarin Amadi tsoro yake bata,Amadi bai taushe hannu ba ya isa gulbin mawaliya ya zuba jinin.Da farko jinin sama ya yi ya takure gu ɗaya kafin daga bisani a fara jansa zuwa ƙasa kamar yadda yaro ke shan daddaɗar madara.
Wani gurnani haɗi da nishi ya taso daga ƙasan ruwan can kuma ya ɗauke,ganin haka Amadi ya nufi gida.
Mutane ya tarar ƙofar gida sun yi cirko-cirko ana leƙen gidansu kafin a juyo duk ana kallon sa.......
[07/09 à 07:40] MRS SADAUKI 👑M~SHURAIM🤍: *MASARAUTAR GOBIR*
LoVe and HoRoR StOrY
*Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo
(MRS SADAUKI💫✍️)
*Lambar waya:* +22795045822
*FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️*
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation.
*Sadaukar wa:* Ga duk Gobirawan duniya.
_____________________
7-8
Ko kafin Amadi ya kai ga tambayar lafiya,Innaro wato mahaifiya ga Fatimah ta kuma sakin wani ihun ta na suratai maras kan gado yayin da kuma ta ke tiƙar rawa irin yadda ƴan bori su ke yi.
Wani sanyi ne ya ratsa zuciyar Amadi,da farko ya ji tsoro kar ace Malam ko Inna aka ɗauka matsayin sacrifice kasancewar lokacin da zai bayar da jinin da yayi alƙawari ya gabato.
Cikin gidan ya wuce tare da samun waje ya zauna ya na kallon yadda Innaro ta rasa hankalinta lokaci guda ba tare da ta shirya ba,a idon mutane aljanu ne suke ganin ta na da amman wurin Amadi shi ya san haukacewa ne ta yi.
"Innaro je ki zauna"Amadi ya faɗa cikin bayar da umarni,cak ta tsaya da rawar sai kuma dare-dare irin na sabon kamu.
Innuwa ta samu ta zauna,a zuci Amadi yace 'au !haukan bai gama rufe ki ba tunda har kin san banbancin innuwa da kuma rana'
Inna ta leƙo ta na mai ɓoyewa bayan ƙyauren ɗakinta,ta na tsinkayar Amadi ta ƙwala masa kira ya taso ya na ƙumshe dariya ganin Inna ta ɓoye a ɗaki har da saka sakata tsabar tsoro.
Ya na zuwa tace "dan Allah ka taimaka kace ta tafi gida, wannan masifa da mi ta yi kama mu na zaman zamanmu ka ɗebo mana fitina"
Amadi yace "Ni kuma?"Inna ta harare sa tace "eh kai ɗin ko ka zata ban san aikin ka ne ba?"Amadi ya sosa ƙeya kafin yaje gun inda Innaro ta ke.
Duƙawa yayi ya fara magana "Innaro kin yarda da auren mu ni da Fatimah ko kuwa?"da sauri ta gyaɗa kai shi kuma ya saki murmushi yace "to tashi ki tafi gida"kamar wata doluwa haka ta yunƙura ta tashi tare da fita waje ba ta zame ko ina ba sai gidanta nan ta tarar da Fatimah da Abdu.
Da sauri ya nufota ya na tambayar ta "Innaro lafiya?na zo na tarar Fatimah na kuka,ke kuma ba kya nan yanzu da kika dawo kayan ki duk sun yi dauɗa?"
Innaro ba tace komi ba ta wuce ɗaki,Abdu ya take mata baya.Ko kafin ya sake yin wata magana tace "maganar auren Fatimah a fara shiri,ban so ya haura sati biyu a kaita kowa ya huta"cike da mamaki Abdu ya kalleta yace "haba Innaro matsafin za mu bai wa aure?"Inna ta yi masa daƙuwa kafin tace "gidan uban wa ka ga yayi tsafin?kawai sharrin mahasada ne dan sun ga duk illahirin garin nan babu mai maganin aljanu kamar sa"
Abdu ya yi ajiyar zuciya kafin yace "to Allah kyauta"Innaro ta amsa masa da "amen" ta na mai bin bayansa da harare a zuci ta na cewa 'Ni ai nafi kowa sanin matsafi ne ,ni da ya turo ma ciwon hauka da rana tsaka duk da na ƴan mintina ne amman ai na wahala'
Fatimah wacce ke waje duk ta ji hirar da suka zanta,cike da murna ta cika bokiti da ruwa ta kai ma Innaro banɗaki kafin ta ɗaga labule tace "ki tasho kiyi wanka na kai maki ruwa"kai ta gyaɗa mata alamar toh kafin a zuci tace 'muguwa ai doli ki kai min ruwa tunda kin kwaso mana masifa mu na zaman-zamanmu'Innaro na shiga bayi Fatimah ta arce ba ta zame ko ina ba sai gidansu Amadi.
Da sallama a bakinta sai dai babu kowa sai kukan wani maras lafiya mai cutar Jinnu da aka kawo ma malam,har za ta fito sai ta tsinkayi riga da wando rataye a katangar banɗaki.
Fatimah ta saki murmushi ta nufi ɗakin Amadi domin jiransa,ba ta wani daɗe da zama ba ya shigo.Kanta sunne a ƙasa ba tare da gaisuwa ba tace "Innaro ta amince da aurenmu shine nace bari na zo na faɗa ma"
Amadi yayi murmushi yace "ai na sani,yanzu haka wankan zuwa gidan ku ne na yi amman tunda ga ki kin zo mu je kawai gaɓar ruwa"
Babu wani muso ta miƙe tsaye ta bi bayansa,su na tafe su na hirar soyayya har suka kawo gaɓar ruwa.
Amadi ya ɗauki ƙanƙara ya jefa a ciki ta bada sautin "tsulum"can sai ga kifi ya fito daidai inda babu ruwa ya na motsi,Amadi ya duƙa ya ɗauki ƙaton kifin kafin ya koma gefe ya cire masa wuya.Wuta ya hura ya fara gasa kifin,ita dai Fatimah na gefe ta na kallon siddabarun Amadi kala-kala.
Cike da burgewa ta ƙaraso gun sa,cikin muryata ta Fulani tace "yanzu in nace sai ka mayar da kifin nan ɗanye ya za ka yi?"Amadi wanda ke ƙoƙarin juya kifin dan ya fara gasuwa ya ɗago ya dubeta yace "tsaf zan maidosa ɗanye kuma da ransa"Fatimah ta waro ido tace "da gaske?"ya jinjina mata kai.Ta rufe baki da dukan hannuwanta kafin tace "to mayar na gani"wata formula Amadi ya faɗa nan take kifin da ke kan wuta yayi tsul ya faɗi a ƙasa ya dawo ɗanye har ya na motsi.Fatimah ta waro ido tace "to mayar da shi gasashe"ko ida rufe bakinta ba ta yi ba kifin ya koma yadda ya ke a gashe bisa garwashi.
Ganin yadda Fatimah ta shiga nishaɗi yasa Amadi mayar da abun wasa sai kifin ya gasu sai kuma ya mayar da shi ɗanye ita kuwa wawiya sai dariya ta ke saboda ita ba ta ganin dogon hannun da ke yin masanyar kifin balle ta farga da rufa ido ake yi mata.
★★★ MARADI
"Ta ya aka yi kika shigo rayuwata ba tare da na shirya ba?"Yarima ya tambaya bayan ya hau kan gadon da Saffa take zaune a tsakiya.
"Ta yadda ka yaudare ni kace za ka sa Prince Khalid ya so ni bayan na ci amanar ƴar uwata"Saffa ta basa amsa
"Ban yaudare ki ba,akasi aka samu ko da na farka ban ga Marwa ba sannan sai naji wai an shirya hidimar auren mu"Yarima ya faɗa,Saffa ta taɓe baki tace "dama ranar da Amma ta zo sashen mu na yi mafarkin haka,ƙaddara za ta raba mu kuma za mu sake kasancewa a tare sai dai ban san tsawon wane lokaci hakan za ta faru ba"
"Ko da ta dawo nan to za ta zo ne a ƙuraren lokaci,saboda sai bayan Yarima ya hau karagar mulkin da ta ke tamaƙa za ta ɗora wanin Yarima"murya Amma ta daki kunnuwansu duk sai suka waigowa su na kallonta cike da mamaki saboda sun kulle ƙofa ta yaya ta shigo kenan?
Amma ta saki murmushi tace "da zarar kun raya daren farkon ku to wannan tsohon banzar zai sabka daga karagar mulki kai kuma Yarima ka hau"a zafafe Yarima ya yo kan Amma ya ɗaga hannu zai sharara mata mari ta riƙe hannunsa ta na "kul!kul!Kar ka soma taɓa fuskar nan yin haka zai sa ka samu tsinuwar Mala'iku saboda wannan fuskar ta mahaifiyar ka ce"
"Mahaifiya?"Yarima ya maimaita kalmar ,Amma ta juya baya tace "tabbas Yarima kai Ɗana ne,na jima ina jiran wannan ranar wacce za ta zo na fasa ƙwan" sam Yarima bai samu bakin magana ba sai Saffa ce ta tambayi Amma "ta yaya kika zamo mahaifiyarsa?sannan shi kuma Prince Khalid fah?"
Amma tace "labari ne mai tsayi,yanzu dai zan barku domin raya wannan daren zan koma sashena jiran har izuwa lokacin da zan ji an buga tamburan juyin mulki"ta na gama faɗa ta fice ba tare da ta jira cewar su ba.
Saffa ta dafa Yarima tace "tabbas biri yayi kama da mutum,sai yanzu na ida fahimtar mi yasa Amma ba ta son Prince Khalid ya auri Marwa" Yarima ya dubeta yace "mi kika gane?"ba ta basa amsa ba ta fara tura masa saƙon da ya zautar shi izuwa raya daren farkon su.