Sashe 8
Masarautar Gobir Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ya kamata ka koma kar Sarki yayi neman ka"Maa ta faɗa ta na mai kawar da kai,Maheer yace "kin matsu na tafi ne dan kar na rinjaye ta ko kuwa?"
Maa tace "ai ko yanzu ta na yin sallah da sauran ibadun ta, wannan dalili ya sa mu ka tsaya bakin gari saboda isar ta can da matsala ka san tsakanin sihiri da Alkur'ani kamar wuta ce da karmami"
Maheer ya ƙanƙance ido yace "Maa kenan kin san alƙur'ani jagaba ne akan komi na duniya?amman miyasa ba za ki aje bokanci ki tuba ga Allah ba?"
Maa ta dube sa tace "a'a kudin ƙaddara ya tsara min haka"ganin dai Maa ba za ta fahimta ba yasa Maheer yi masu sallama ya fara tafiya bai yi nisa ba ya ɓace a idon Marwa.
Ta sauke ajiyar zuciya "Maa miyasa ya ke zuwa nan alhalin shi ya kasance Musulmi kuma kin ce sai Ifiritu da masu aiki da su kawai ke wannan Nahiyar?"Marwa ta yi wannan tambayar ta na mai maida dukan hankalinta ga Maa.
"Shi ɗin zuciyarsa tsarkaka ce,a kullum burinsa bai wuce ya mayar da wannan Nahiyar ba yankin Musulmi.A lokacin baya duk ranar juma'a ya ke ziyartar mu,zai zo yayi wa'azi wani sa'in kafin ya gusa sai ya rinjayi wasu sun shiriya kama daga bil'adama zuwa Jinnu " Maa ta bata amsa ta na mai sunkuyawa ta ɗauki wata sarƙa.
★★★ MADARUMFA
Yamma lis su Amadi suka dawo gida ,a bakin ƙofar gidan su Fatimah suka tsaya su na hira.
Abdu ya zo suka gaisa da Amadi sannan ya shaida masa saƙon Innaro,kamar wani mutumen kirki haka Amadi ya shiga godiya.
"Ki shiga ciki amaryar Amadi magrib ta gabato zan je na yi sallah na je bakin gulbi yau aikin dare zan yi"
Fatimah ta ɓata fuska tace "Ni dai gaskiya ka canza sana'a dan ba zan lamunci wannan ba"
Amadi yace "mi kenan?"ta bashi amsa da "fitar dare mana"
"Kar ki damu in dai wannan ne,ina ce ma dai gulbin ya kusa tafiya sai kuma wata shekara.Am...ki shiga gida sai gobe da safe zan zo nan kafin na wuce aiki"
"To ya maganar turo da magabatan naka ko har ka manta?"Fatimah ta tambaya
"Ta ya zan manta ke ma,ai sai in babu rai a gangar jikina dan na tabbata ko haukacewa na yi ba zan manta wannan babban abun farin cikin ba.In shaa Allah gobe zan turo da komi kin ji amarya ta?"da sauri Fatimah ta rufe ido dan kunya gami da rugawa cikin gida shi kuwa Amadi ya na dariya ya nufi na su gidan.
Washegari
Sai da amadi ya cika alƙawarin sa na zuwa ya ga Fatimah kafin ya wuce bakin rafi.
Duk wunin ranar Fatimah cikin murna ta yi sa ganin dangin mahaifanta tuni sun hallara domin tarbar bakinta.
Lauriya da sauran ƙawaye sai murna suke taya Fatimah yayinda tuni dangi Amadi sun hallara sai buɗa ke tashi,bayan an karɓi sadaki aka ɗaura aure kamar yadda al'adar garin ta ke.An tsayar da sati biyu ranar da za'a yi walima kafin amarya ta tare gidan mijinta.
Ana shirin magrib Amadi ya shigo gida kamar kullum,bayan sun gaisa da Inna ne ta ke shaida masa an tsayar da bikin su sati biyu masu zuwa.Babu kunya Amadi ya fara taka rawa kafin ya wuce cikin ɗakinsa,ƙwarya da ke ƙarƙashin gadonsa ya ɗauko ya duba ya gani ruwan cikinta sun yi ƙasa hakan na nuni da gulbi ya kusa ƙwafewa.Ya mayar sannan ya fito yayi wanka ya tafi masallaci,ya na dawowa Inna tace "Amadi ga abincin ka nan rufe da faifai"ya girgiza kai yace "ai yau ba zan ci komi ba saboda murna,amman ina son na je wajen Ɗan Ladi mai balangu na saya mana mu ci ni da Fatimah kin ga sai mu taya junan mu farin ciki.Ke ma kin faɗan abinda kike so sai na biyo maki da shi"
Inna tace "a'a ni kam ba zan ci komi ba amman in ka fita ka biyo ma malam da fura sai na dama masa "da "toh"Amadi ya amsa kafin ya fice.
Direct wajen mai balangun ya nufa ,bayan ya saya sai ya wuce gidan su Fatimah.Har ciki ya shiga yayi sallama jin ta amsa masa yasa shi fitowa waje ya zauna kan dakali zaman jiranta,ba'a jima ba can sai gata ta fito cikin shigar atamfa da zane ta ɗaura kallabin wani yadi daban.
A kunyace ta zo ta zauna kafin ta gaishe sa,ya amsa ya na mai tambayarta mutan gida ta amsa masa da "alhamdullah,ya naku gidan fatan su Inna na lafiya?"
"Lafiyarta lau tace na gaishe ki sannan na kawo maki balangu"Amadi ya faɗa ya na mai buɗe ledar ya aje a tsakiyar su yace "Bismillah mu ci"a al'adar Fulani budurwa ba ta iya cin abinci a gaban namiji,amman kasancewar Amadi ya gama sihirce Fatimah haka ta saka hannunta suka cinye bulangun nan tas har da shiga gida ta ɗebo masu ruwa.
Hira suka yi sosai game da kawo lefen da aka yi da kuma yadda bikin su zai kasance,a ƙarshe suka yi ma juna sallama.
Bayan sati biyu aka yi walimar bikin su Amadi,dangi da ƙawaye suka rako amarya ɗakinta wanda ya kasance gidan iyayen Amadi a nan cikin ɗakinsa wanda ya sha gyara.
Bayan kowa ya watse Amadi ya shigo ɗakin amarya shi ɗaya, kasancewar duk garin Madarumfa ba za'a nuna wani ba a matsayin abokinsa.
Cike da bege da shauƙi irin na amare Amadi ya yaye maluluɓin da aka rufeta,a kunyace ta so ƙwace darar sai dai tuni Amadi yayi mata dirar mikiya.Duk yadda Fatimah ta so ƙwatar kanta abu ya cuttura saboda da dukan alamu shi Amadi so ya ke kawai ya cimma burinsa wanda kuma kusan agonye ne ne haka.
Ƙarar da Fatimah ta yi yayi daidai da faɗuwar Malam wanda shi kuma shigowar sa kenan,da sauri Inna tayi kansa ta na "Innalillahi wa'inna iley raji'un"ruwa ta yi ta zuba masa amman shiru.
Tsawon lokaci sosai Amadi ya fito daga ɗaki jin kukan mahaifiyarsa ya ƙi tsayawa,da sauri shi ma ya nufi malam ɗin kafin ya koma ɗaki ya ɗauko fitila ya haska malam.
Da sauri ya saki fitilar ya na mai furta" Innalillahi wa'inna iley raji'un" yayinda ita kuma Inna ta faɗi a sume.....
[08/09 à 08:24] MRS SADAUKI 👑M~SHURAIM🤍: *MASARAUTAR GOBIR*
LoVe and HoRoR StOrY
*Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo
(MRS SADAUKI💫✍️)
*Lambar waya:* +22795045822
*FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️*
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation.
*Sadaukar wa:* Ga duk Gobirawan duniya.
_____________________
9-10
Jini ne ke fita a duk wasu ƙofofin fuskar malam,hanci,ido, kunnuwa da kuma baki.
Amadi ya saki fitilar zuciyarsa na bugun tara-tara,a doli ya fita ya nemo mai mota aka kai shi asibiti sai dai daga zuwansu aka tabbatar masu da rai ya riga da yayi halinsa.
Inna ta turje ta ƙi baro asibiti,Amadi ya dawo gida ya taimaka ma Fatimah ta gyara jikinta sannan ya canza zanen gadon.
Ya rungume Fatimah a jikinsa ko zai ji sassauci,ita kuwa ta na son tambayar shi lafiya don kuwa duk ta ji koke-koken Inna sai dai yanayinsa da kuma rashin jin ƙwarin jikinta yasa ta share zancen.
Washegari duk garin Madarumfa ya ɗauka malam ya rasu,sosai Fatimah ta yi kuka musamman da ta ji an fara yada mata magana ana cewa "Amadi ya auro mai farar ƙafa,yo wa ya sani ma ko mayya ce".
Tunda aka yi rasuwar yanzu tsawon kwana uku kenan in Fatimah ta gaishe da Inna ba ta amsawa,wannan abu na damunta duk da a ɓangaren Amadi bai nuna mata canji ba sai ma ƙara nuna mata ƙauna da yake.
"Ina kwana Innarmu ya kwanan kewa?"Fatimah ta faɗa ta na mai zama kan tabarmar da Inna ke zaune a kai.Da sauri Inna ta tashi ta na cewa "tambayar mi za ki yi min bayan kin lashe kurwa mijina?Ko kuwa ni ma zowa kika yi ki lashe ni ?"Fatimah ta fashe da kuka ta na cewa "haba Inna ke ma yadda mutanen gari suka laƙa min sharri..."ko kafin ta ida Inna ta shige ɗaki ta barta nan zaune.
Jiki babu ƙwari Fatimah ta miƙe,ta saka takalmi ta nufi ƙofar fita suka yi kiciɓus da Amadi "ina za ki je?"ya tambaye ta ya na kallonta,kai tsaye tace "gidanmu, Amadi na gaji da zaman ƙunci yau kimanin sati biyu da rasuwar Baba malam amman har yanzu Inna ta ƙi fahimta ta da ba ni ce silar mutuwar sa ba,mutanen gari in sun ce yanzu ita Inna ya kamata yayi ita ma ta faɗa?"duk tana kuka ta ke yi masa wannan jawabin.
Amadi ya kama hannunta ya ja ta zuwa ɗakin Inna ,da sallama ya shiga kafin yace "Inna wannan matata ce,in har ke baki yi shedar ta ba ta yaya sauran al'umma za su yi? Sanin kan ki ne Fatimah ba wani sona ta ke ba amman nayi shige da fice har na same ta.Inna duk ɗan Adam ba zai wuce lokacinsa ba,mu ma in lokacin mu yayi doli mu tafi.Ki sa a ran ki malam ya mutu ne saboda lokacinsa da yayi sannan dan Allah ki zauna da Fatimah lafiya na roƙe ki,ita ce farin cikina,sirrina in babu ita rayuwata ragaga ce"
Tunda ya fara maganar Inna ke kuka ba tace komi ba,Amadi ya ci gaba da cewa "haba Uwata!kar fah ki manta a kullum ke ce ke faɗa min قُل لَّن يُصِيبَنَآ إِلَّا مَا كَتَبَ ٱللَّهُ لَنَا هُوَ مَوۡلَىٰنَاۚ babu abinda zai samu bawa baya ga abinda ga Ubangijinsa ya rubuta zai same sa,sannan وَعَلَى ٱللَّهِ فَلۡيَتَوَكَّلِ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ gare shi masu Imani ya kamata su mayar da yardarsu kenan yanzu ki na nufin ba ki yarda da Ayar ba komi?"cikin kuka Inna tace "na yarda Amadi Allah jiƙansa da rahama,Ƴata Fatimah ki yi haƙuri ruɗin sheɗan ne shiyasa sam na kasa fahimta"Fatimah ta faɗa jikin Inna ta na kuka.
Maa tace "ai ko yanzu ta na yin sallah da sauran ibadun ta, wannan dalili ya sa mu ka tsaya bakin gari saboda isar ta can da matsala ka san tsakanin sihiri da Alkur'ani kamar wuta ce da karmami"
Maheer ya ƙanƙance ido yace "Maa kenan kin san alƙur'ani jagaba ne akan komi na duniya?amman miyasa ba za ki aje bokanci ki tuba ga Allah ba?"
Maa ta dube sa tace "a'a kudin ƙaddara ya tsara min haka"ganin dai Maa ba za ta fahimta ba yasa Maheer yi masu sallama ya fara tafiya bai yi nisa ba ya ɓace a idon Marwa.
Ta sauke ajiyar zuciya "Maa miyasa ya ke zuwa nan alhalin shi ya kasance Musulmi kuma kin ce sai Ifiritu da masu aiki da su kawai ke wannan Nahiyar?"Marwa ta yi wannan tambayar ta na mai maida dukan hankalinta ga Maa.
"Shi ɗin zuciyarsa tsarkaka ce,a kullum burinsa bai wuce ya mayar da wannan Nahiyar ba yankin Musulmi.A lokacin baya duk ranar juma'a ya ke ziyartar mu,zai zo yayi wa'azi wani sa'in kafin ya gusa sai ya rinjayi wasu sun shiriya kama daga bil'adama zuwa Jinnu " Maa ta bata amsa ta na mai sunkuyawa ta ɗauki wata sarƙa.
★★★ MADARUMFA
Yamma lis su Amadi suka dawo gida ,a bakin ƙofar gidan su Fatimah suka tsaya su na hira.
Abdu ya zo suka gaisa da Amadi sannan ya shaida masa saƙon Innaro,kamar wani mutumen kirki haka Amadi ya shiga godiya.
"Ki shiga ciki amaryar Amadi magrib ta gabato zan je na yi sallah na je bakin gulbi yau aikin dare zan yi"
Fatimah ta ɓata fuska tace "Ni dai gaskiya ka canza sana'a dan ba zan lamunci wannan ba"
Amadi yace "mi kenan?"ta bashi amsa da "fitar dare mana"
"Kar ki damu in dai wannan ne,ina ce ma dai gulbin ya kusa tafiya sai kuma wata shekara.Am...ki shiga gida sai gobe da safe zan zo nan kafin na wuce aiki"
"To ya maganar turo da magabatan naka ko har ka manta?"Fatimah ta tambaya
"Ta ya zan manta ke ma,ai sai in babu rai a gangar jikina dan na tabbata ko haukacewa na yi ba zan manta wannan babban abun farin cikin ba.In shaa Allah gobe zan turo da komi kin ji amarya ta?"da sauri Fatimah ta rufe ido dan kunya gami da rugawa cikin gida shi kuwa Amadi ya na dariya ya nufi na su gidan.
Washegari
Sai da amadi ya cika alƙawarin sa na zuwa ya ga Fatimah kafin ya wuce bakin rafi.
Duk wunin ranar Fatimah cikin murna ta yi sa ganin dangin mahaifanta tuni sun hallara domin tarbar bakinta.
Lauriya da sauran ƙawaye sai murna suke taya Fatimah yayinda tuni dangi Amadi sun hallara sai buɗa ke tashi,bayan an karɓi sadaki aka ɗaura aure kamar yadda al'adar garin ta ke.An tsayar da sati biyu ranar da za'a yi walima kafin amarya ta tare gidan mijinta.
Ana shirin magrib Amadi ya shigo gida kamar kullum,bayan sun gaisa da Inna ne ta ke shaida masa an tsayar da bikin su sati biyu masu zuwa.Babu kunya Amadi ya fara taka rawa kafin ya wuce cikin ɗakinsa,ƙwarya da ke ƙarƙashin gadonsa ya ɗauko ya duba ya gani ruwan cikinta sun yi ƙasa hakan na nuni da gulbi ya kusa ƙwafewa.Ya mayar sannan ya fito yayi wanka ya tafi masallaci,ya na dawowa Inna tace "Amadi ga abincin ka nan rufe da faifai"ya girgiza kai yace "ai yau ba zan ci komi ba saboda murna,amman ina son na je wajen Ɗan Ladi mai balangu na saya mana mu ci ni da Fatimah kin ga sai mu taya junan mu farin ciki.Ke ma kin faɗan abinda kike so sai na biyo maki da shi"
Inna tace "a'a ni kam ba zan ci komi ba amman in ka fita ka biyo ma malam da fura sai na dama masa "da "toh"Amadi ya amsa kafin ya fice.
Direct wajen mai balangun ya nufa ,bayan ya saya sai ya wuce gidan su Fatimah.Har ciki ya shiga yayi sallama jin ta amsa masa yasa shi fitowa waje ya zauna kan dakali zaman jiranta,ba'a jima ba can sai gata ta fito cikin shigar atamfa da zane ta ɗaura kallabin wani yadi daban.
A kunyace ta zo ta zauna kafin ta gaishe sa,ya amsa ya na mai tambayarta mutan gida ta amsa masa da "alhamdullah,ya naku gidan fatan su Inna na lafiya?"
"Lafiyarta lau tace na gaishe ki sannan na kawo maki balangu"Amadi ya faɗa ya na mai buɗe ledar ya aje a tsakiyar su yace "Bismillah mu ci"a al'adar Fulani budurwa ba ta iya cin abinci a gaban namiji,amman kasancewar Amadi ya gama sihirce Fatimah haka ta saka hannunta suka cinye bulangun nan tas har da shiga gida ta ɗebo masu ruwa.
Hira suka yi sosai game da kawo lefen da aka yi da kuma yadda bikin su zai kasance,a ƙarshe suka yi ma juna sallama.
Bayan sati biyu aka yi walimar bikin su Amadi,dangi da ƙawaye suka rako amarya ɗakinta wanda ya kasance gidan iyayen Amadi a nan cikin ɗakinsa wanda ya sha gyara.
Bayan kowa ya watse Amadi ya shigo ɗakin amarya shi ɗaya, kasancewar duk garin Madarumfa ba za'a nuna wani ba a matsayin abokinsa.
Cike da bege da shauƙi irin na amare Amadi ya yaye maluluɓin da aka rufeta,a kunyace ta so ƙwace darar sai dai tuni Amadi yayi mata dirar mikiya.Duk yadda Fatimah ta so ƙwatar kanta abu ya cuttura saboda da dukan alamu shi Amadi so ya ke kawai ya cimma burinsa wanda kuma kusan agonye ne ne haka.
Ƙarar da Fatimah ta yi yayi daidai da faɗuwar Malam wanda shi kuma shigowar sa kenan,da sauri Inna tayi kansa ta na "Innalillahi wa'inna iley raji'un"ruwa ta yi ta zuba masa amman shiru.
Tsawon lokaci sosai Amadi ya fito daga ɗaki jin kukan mahaifiyarsa ya ƙi tsayawa,da sauri shi ma ya nufi malam ɗin kafin ya koma ɗaki ya ɗauko fitila ya haska malam.
Da sauri ya saki fitilar ya na mai furta" Innalillahi wa'inna iley raji'un" yayinda ita kuma Inna ta faɗi a sume.....
[08/09 à 08:24] MRS SADAUKI 👑M~SHURAIM🤍: *MASARAUTAR GOBIR*
LoVe and HoRoR StOrY
*Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo
(MRS SADAUKI💫✍️)
*Lambar waya:* +22795045822
*FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️*
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation.
*Sadaukar wa:* Ga duk Gobirawan duniya.
_____________________
9-10
Jini ne ke fita a duk wasu ƙofofin fuskar malam,hanci,ido, kunnuwa da kuma baki.
Amadi ya saki fitilar zuciyarsa na bugun tara-tara,a doli ya fita ya nemo mai mota aka kai shi asibiti sai dai daga zuwansu aka tabbatar masu da rai ya riga da yayi halinsa.
Inna ta turje ta ƙi baro asibiti,Amadi ya dawo gida ya taimaka ma Fatimah ta gyara jikinta sannan ya canza zanen gadon.
Ya rungume Fatimah a jikinsa ko zai ji sassauci,ita kuwa ta na son tambayar shi lafiya don kuwa duk ta ji koke-koken Inna sai dai yanayinsa da kuma rashin jin ƙwarin jikinta yasa ta share zancen.
Washegari duk garin Madarumfa ya ɗauka malam ya rasu,sosai Fatimah ta yi kuka musamman da ta ji an fara yada mata magana ana cewa "Amadi ya auro mai farar ƙafa,yo wa ya sani ma ko mayya ce".
Tunda aka yi rasuwar yanzu tsawon kwana uku kenan in Fatimah ta gaishe da Inna ba ta amsawa,wannan abu na damunta duk da a ɓangaren Amadi bai nuna mata canji ba sai ma ƙara nuna mata ƙauna da yake.
"Ina kwana Innarmu ya kwanan kewa?"Fatimah ta faɗa ta na mai zama kan tabarmar da Inna ke zaune a kai.Da sauri Inna ta tashi ta na cewa "tambayar mi za ki yi min bayan kin lashe kurwa mijina?Ko kuwa ni ma zowa kika yi ki lashe ni ?"Fatimah ta fashe da kuka ta na cewa "haba Inna ke ma yadda mutanen gari suka laƙa min sharri..."ko kafin ta ida Inna ta shige ɗaki ta barta nan zaune.
Jiki babu ƙwari Fatimah ta miƙe,ta saka takalmi ta nufi ƙofar fita suka yi kiciɓus da Amadi "ina za ki je?"ya tambaye ta ya na kallonta,kai tsaye tace "gidanmu, Amadi na gaji da zaman ƙunci yau kimanin sati biyu da rasuwar Baba malam amman har yanzu Inna ta ƙi fahimta ta da ba ni ce silar mutuwar sa ba,mutanen gari in sun ce yanzu ita Inna ya kamata yayi ita ma ta faɗa?"duk tana kuka ta ke yi masa wannan jawabin.
Amadi ya kama hannunta ya ja ta zuwa ɗakin Inna ,da sallama ya shiga kafin yace "Inna wannan matata ce,in har ke baki yi shedar ta ba ta yaya sauran al'umma za su yi? Sanin kan ki ne Fatimah ba wani sona ta ke ba amman nayi shige da fice har na same ta.Inna duk ɗan Adam ba zai wuce lokacinsa ba,mu ma in lokacin mu yayi doli mu tafi.Ki sa a ran ki malam ya mutu ne saboda lokacinsa da yayi sannan dan Allah ki zauna da Fatimah lafiya na roƙe ki,ita ce farin cikina,sirrina in babu ita rayuwata ragaga ce"
Tunda ya fara maganar Inna ke kuka ba tace komi ba,Amadi ya ci gaba da cewa "haba Uwata!kar fah ki manta a kullum ke ce ke faɗa min قُل لَّن يُصِيبَنَآ إِلَّا مَا كَتَبَ ٱللَّهُ لَنَا هُوَ مَوۡلَىٰنَاۚ babu abinda zai samu bawa baya ga abinda ga Ubangijinsa ya rubuta zai same sa,sannan وَعَلَى ٱللَّهِ فَلۡيَتَوَكَّلِ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ gare shi masu Imani ya kamata su mayar da yardarsu kenan yanzu ki na nufin ba ki yarda da Ayar ba komi?"cikin kuka Inna tace "na yarda Amadi Allah jiƙansa da rahama,Ƴata Fatimah ki yi haƙuri ruɗin sheɗan ne shiyasa sam na kasa fahimta"Fatimah ta faɗa jikin Inna ta na kuka.