Sashe 14
Kawar Zuciya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Cikin Safiyyah ya shiga watanni na bakwai, karkashin kyakkyawar kulawar likitocin ta, kulawarsu, tattalinsu da burinsu duka ya koma kan cikin. Wani abun mamaki Zayyan din da a baya yake cewa bai damu da haihuwa ba blah blah blah… sai gashi da akayi wa Sophie dashen Dan, sai yazo yafi kowa son shi, da dokin a haifa masa shi ya dauka.
Har dakin da Babyn zai rayu bayan an yaye shi daga nono Zayyan ya ware a kusa da nasu shi da Safiyyah.
Ya zuba komai na bukatar yara ‘toddlers’. Mama Fatu dai ko me yasa? Daga baya bakinta ya mutu akan batun cikin, bata kara aibatawa ba, bayan wancan wankin babban bargon data yi musu. Ganin dukkansu sun dauke mata kafa.
Wannan ya biyo bayan ranar da tayi arba da Safiyyah da tirtsetsen cikinta a gabanta, aka ce Uwa-Uwa ce ba’a sake ki saidai uwardaki, shi da kansa ya hakura da abinda Mama tayi masa ya dauko Safiyyah da tsohon cikinta musamman ya kawo ta don ta gaida Mama, daga ranar bakin Mama dana ‘ya’yanta yayi la’asar daga gorin Sophie ta kasa haihuwa, sun yarda ko yaya ne dai ashe akwai kwan haihuwa irinna kowacce ‘ya mace a jikinta, suka gasgata jita-jitan da suke ji din, na cewa tabbas ta samu ciki daga bakin Zubaina, wanda a da suka kasa yarda da gangan.
Saboda a ranar ta same su bakidaya a gidan mahaifan nasu (banda Zubaina), suna tsaka da family meeting kamar yadda suka saba tare da Baba Murtala akan habakar Estates dinsu na nan Katsina, da sauran fannoni na cigaban rayuwarsu data ‘ya’yansu masu tasowa.
Baba Murtala wanda shine makwafin Ubansu a halin yanzu, duk meetings din da suke yi a karshen kowanne wata in dai yana gari da shi a ciki, akan rayuwarsu data ‘ya’yansu data Estate din ‘ya’yan Mama ake meeting din, a kowacce asabar din karshen wata, inda Baba Murtala yake shige musu gaba a komai, don kula da habakar dukiyarsu da cigaban rayuwarsu.
Duk da Mama ta amsa gaisuwarta, ta kuma ganta da tirtsetsen ciki ta kasa cewa a ranta “Alhamdulillah Baffa zai haihu”, haka ta kasa cewa “Allah ya raba lafiya” saboda can a kasan ranta tana jin wani iri babu dadi, saboda tuntuni ta riga ta sakawa kanta wani negative thought haka (gurbataccen tunani) akan ‘In-vitro Fertilization’.
Mama in ta tuna dan Zayyan dinta na farko a duniya, haihuwar Baffanta na fari dan dashe ne (IVF Baby) ne sai taji gara ma bai haifa ba.
Yawan korafin Mama akan rashin halaccin IVF yasa Zayyan ya sake bazama neman fatawar Malamai mabambanta, amma kamar can baya, har yau bai ji fatawa sahihiyar da ta haramtashi ba. Saidai malamai suce surrogacy shine haramun (wata ta daukar ma mace cikin da sperm din mijinta ta haifar mata dan saboda ita bazata iya haihuwa ba).
Amma a duka binciken da yayi na addini akan In-Vitro Fertilization, amsar da yake samu shine;
“IVF is permissible in ISLAM with the condition that it involves the gametes of the married couple and adheres to the sanctity of the marital union, aligning with Islamic principles of lineage preservation”.
Ma’ana; Dashen haihuwa ya halatta a muulunci bisa sharadin cewa kwayayen haihuwar da za’ayi amfani dasu su kasance na ma’auratan ne, don a kare martabar aure da samar da zuri’a tsarkakakkiya kamar yadda dokokin musulunci suka tanada”.
***** **** ****
“The IVF Mother”
A wannan lokacin da cikin ta ya shiga watanni na takwas Zayyan baya nisa da gidansa. Haka duk inda yaje Safiyyah na ransa, baya awa biyu bai kirata a waya don tabbatar da lafiyarta ba.
Tun cikin nada wata bakwai Zayyan da Safiyyah da taimakon Yayarsa Zubaina sun gama tanadar duk wani abinda jaririn zai bukata, shi da Yaya Zubaina suke shirye-shiryensu ba tareda sun saka Zubaidah ba, har feeder da gadon baccin jariri yana nan sun ajiye a cikin dakin sa. Kuma komai suka tashi saya sai sun zabo ajin farko na ‘yan gatan jarirai.
A ranar da cikin Safiyya ya shiga watan haihuwa ba yadda Safiyyyah bata yi da Zayyan ya maidata Dandume ta haihu a can ba, ya kafe yaki amincewa.
Yace “kina wasa ne kema yarinya.
Ya kamata ki san cewa we have to take extra care of this Baby, tunda dai kin ga da yadda Allah yasa aka sameshi. Bazan barki ki koma Dandume haka kawai inje kiyi haihuwar gida ba, lallai sai a asibitin da ake kula daku anan tun farko zan bari ki haihu, in yaso Ammi ta kawo wadda zata kula da ke gidannan, to wannan kuwa, bazan ki amincewa ba, hankalina ma zai fi kwanciya in ya kasance muna tare koyaushe, fiyeda ina nan nesa, ku kuna can Dandume”.
A can gidan su Safiyyah Ammi tuni ta soma hada kayan haihuwa, su yajin jego, garin yin kunun kanwa da kanwar kanta duk ta tanada da sauransu, haka ta hada su rankatakaf ta daure jiran haihuwa kawai ake.
Da EDD dinta ya rage saura sati biyu shida kansa ya roko Ammi ta basu mai zaman jego. Sai Ammi tace Sabah da Rayyah su shirya su koma Abuja su taimakawa Yayarsu, don masha Allah ‘yan matan Ammi sun horu, ba abunda basu iya ba na manya kasancewar su rainon Tsoffi.
Har Rayha autar su ta girma Ammi bata san komai na hidimarta da rainonta ba, Sabah da Rayyah ne suka yi raino da hidimarta. Haka in Anti Dije ta haihu su suke mata komai da babba ke yiwa Maijego harda saka ruwan wanka.
Haihuwar Safiyyah daban ce da sauran haihuwa shiyasa iyayenta basu takura ta dawo gida ta haihu a gabansu ba.
Zayyan daga baya ya yiwa su malam bayanin IVF na asibiti aka yi mata, kuma malam a matsayin shi na babban malami bai yi challenging IVF ba, ya dubeshi ta kowacce fuska ta addini bai ga inda ya zama haramtacce ba.
Don haka ya bisu da addu’a da fatan Allah ya sauki Safiyyah lafiya.
Yanzunma Sabah da Rayyah data turawa Safiyya tana da tabbacin zasu iya, shiyasa ta turo su tunda Anti Dije bazata bar gidanta taje jegonta ba, amma hankalinta bakidaya yana kan babbar ‘yarta mafi soyuwa a ranta “Nana Safiyyah”. Dare da rana tana yi mata addu’ar sauka lafiya da samun saukin nakuda a kowacce sallahr farillarta.
Da murna da doki sosai su Sabah suke shirin tafiya Abuja, don kwatakwata tun komawarsu Safiyyah can bai fi sau biyu suka taba zuwa gidan Yayar tasu ba, shima dubiyarta suka je da bata da lafiya, na farkon kuma sun je ganin gidan ne sanda zasu koma can da zama, malam baya barinsu sam, don kowacce da maganar aurenta a kanta in ka dauke Rayha autar Ammi.
A motar haya su Rayyah suka tafi Abuja su biyu. Tun kafin su iso Safiyyah ta ware musu dakin da zasu sauka cike da dokin ganin kannen nata, ta aje masu duk abinda ta san zasu bukata, wannan shine zuwansu Abuja karo na biyu tun dawowarsu Safiyya nan daga Zaria.
Sabah dama tafi Rayyah baki, kuma tafi duk sauran kannenta faram-faram da jama’ah. Tunda Zayyan ya je dauko su a tashar Jabi tana gidan gaba Rayyah na baya, shida ita suke hirar tsokanar juna a cikin motar. Zayyan yana tsokanarta da amaryar robarshi, tazo bikon shi, taga baya zuwa zance yanzu, Sabah tace “haba dai inzo bikon ka, na dai zo taron Da na wallahi, kaima kasan kayi min tsufa Yaya Zayyan”, Zayyan yak ama baki ciki dariya da mamaki yace “really? Rayyah, yaushe ‘yar kauyen matar nan ta kile haka?”
Rayyah dai dariya take tana jinsu. Sabah ta kara cewa “Saboda Allah Rayyah nida nake da sarbadeden saurayi irin Jabir a gefe, yaro matashi me jini a jika, dan late twenties, me zan yi da Yaya Zayyan? Wannan kayan tsufan ai sai Nana Safiyyah”.
Zayyan ya tuntsure da dariya harda bugun sityari yace “amma kin yankeni! Saina gayawa Sophie, kina kira ma darling dinta tsufa tun yanzu”.
Tunda su Sabah suka zo gidan suke wani irin kula da Safiyyah da komai na kulawar gidan ya koma wuyansu, ko tsinke basa bari ta kawar, ko abinci taci nan zasu kawo mata ruwa ta wanke hannu daga zaune. Zayyan kuma ya wadatasu da kayan dadi suke ta fama, duk fitar da yayi ya dawo sai ya riko musu abinmotsa baki, musamman Rufaida Yughurt da Rufaidah Shawarma da Pizza din Dominos da suke matukar so.
Yanzu kam kowa yaga Sophie ya san dan cikin ta ya gama duk wani shirye-shiryensa na isowa duniya. Tashi sai da dabara kwanciya ma haka.
**** ***** ****
Har dakin da Babyn zai rayu bayan an yaye shi daga nono Zayyan ya ware a kusa da nasu shi da Safiyyah.
Ya zuba komai na bukatar yara ‘toddlers’. Mama Fatu dai ko me yasa? Daga baya bakinta ya mutu akan batun cikin, bata kara aibatawa ba, bayan wancan wankin babban bargon data yi musu. Ganin dukkansu sun dauke mata kafa.
Wannan ya biyo bayan ranar da tayi arba da Safiyyah da tirtsetsen cikinta a gabanta, aka ce Uwa-Uwa ce ba’a sake ki saidai uwardaki, shi da kansa ya hakura da abinda Mama tayi masa ya dauko Safiyyah da tsohon cikinta musamman ya kawo ta don ta gaida Mama, daga ranar bakin Mama dana ‘ya’yanta yayi la’asar daga gorin Sophie ta kasa haihuwa, sun yarda ko yaya ne dai ashe akwai kwan haihuwa irinna kowacce ‘ya mace a jikinta, suka gasgata jita-jitan da suke ji din, na cewa tabbas ta samu ciki daga bakin Zubaina, wanda a da suka kasa yarda da gangan.
Saboda a ranar ta same su bakidaya a gidan mahaifan nasu (banda Zubaina), suna tsaka da family meeting kamar yadda suka saba tare da Baba Murtala akan habakar Estates dinsu na nan Katsina, da sauran fannoni na cigaban rayuwarsu data ‘ya’yansu masu tasowa.
Baba Murtala wanda shine makwafin Ubansu a halin yanzu, duk meetings din da suke yi a karshen kowanne wata in dai yana gari da shi a ciki, akan rayuwarsu data ‘ya’yansu data Estate din ‘ya’yan Mama ake meeting din, a kowacce asabar din karshen wata, inda Baba Murtala yake shige musu gaba a komai, don kula da habakar dukiyarsu da cigaban rayuwarsu.
Duk da Mama ta amsa gaisuwarta, ta kuma ganta da tirtsetsen ciki ta kasa cewa a ranta “Alhamdulillah Baffa zai haihu”, haka ta kasa cewa “Allah ya raba lafiya” saboda can a kasan ranta tana jin wani iri babu dadi, saboda tuntuni ta riga ta sakawa kanta wani negative thought haka (gurbataccen tunani) akan ‘In-vitro Fertilization’.
Mama in ta tuna dan Zayyan dinta na farko a duniya, haihuwar Baffanta na fari dan dashe ne (IVF Baby) ne sai taji gara ma bai haifa ba.
Yawan korafin Mama akan rashin halaccin IVF yasa Zayyan ya sake bazama neman fatawar Malamai mabambanta, amma kamar can baya, har yau bai ji fatawa sahihiyar da ta haramtashi ba. Saidai malamai suce surrogacy shine haramun (wata ta daukar ma mace cikin da sperm din mijinta ta haifar mata dan saboda ita bazata iya haihuwa ba).
Amma a duka binciken da yayi na addini akan In-Vitro Fertilization, amsar da yake samu shine;
“IVF is permissible in ISLAM with the condition that it involves the gametes of the married couple and adheres to the sanctity of the marital union, aligning with Islamic principles of lineage preservation”.
Ma’ana; Dashen haihuwa ya halatta a muulunci bisa sharadin cewa kwayayen haihuwar da za’ayi amfani dasu su kasance na ma’auratan ne, don a kare martabar aure da samar da zuri’a tsarkakakkiya kamar yadda dokokin musulunci suka tanada”.
***** **** ****
“The IVF Mother”
A wannan lokacin da cikin ta ya shiga watanni na takwas Zayyan baya nisa da gidansa. Haka duk inda yaje Safiyyah na ransa, baya awa biyu bai kirata a waya don tabbatar da lafiyarta ba.
Tun cikin nada wata bakwai Zayyan da Safiyyah da taimakon Yayarsa Zubaina sun gama tanadar duk wani abinda jaririn zai bukata, shi da Yaya Zubaina suke shirye-shiryensu ba tareda sun saka Zubaidah ba, har feeder da gadon baccin jariri yana nan sun ajiye a cikin dakin sa. Kuma komai suka tashi saya sai sun zabo ajin farko na ‘yan gatan jarirai.
A ranar da cikin Safiyya ya shiga watan haihuwa ba yadda Safiyyyah bata yi da Zayyan ya maidata Dandume ta haihu a can ba, ya kafe yaki amincewa.
Yace “kina wasa ne kema yarinya.
Ya kamata ki san cewa we have to take extra care of this Baby, tunda dai kin ga da yadda Allah yasa aka sameshi. Bazan barki ki koma Dandume haka kawai inje kiyi haihuwar gida ba, lallai sai a asibitin da ake kula daku anan tun farko zan bari ki haihu, in yaso Ammi ta kawo wadda zata kula da ke gidannan, to wannan kuwa, bazan ki amincewa ba, hankalina ma zai fi kwanciya in ya kasance muna tare koyaushe, fiyeda ina nan nesa, ku kuna can Dandume”.
A can gidan su Safiyyah Ammi tuni ta soma hada kayan haihuwa, su yajin jego, garin yin kunun kanwa da kanwar kanta duk ta tanada da sauransu, haka ta hada su rankatakaf ta daure jiran haihuwa kawai ake.
Da EDD dinta ya rage saura sati biyu shida kansa ya roko Ammi ta basu mai zaman jego. Sai Ammi tace Sabah da Rayyah su shirya su koma Abuja su taimakawa Yayarsu, don masha Allah ‘yan matan Ammi sun horu, ba abunda basu iya ba na manya kasancewar su rainon Tsoffi.
Har Rayha autar su ta girma Ammi bata san komai na hidimarta da rainonta ba, Sabah da Rayyah ne suka yi raino da hidimarta. Haka in Anti Dije ta haihu su suke mata komai da babba ke yiwa Maijego harda saka ruwan wanka.
Haihuwar Safiyyah daban ce da sauran haihuwa shiyasa iyayenta basu takura ta dawo gida ta haihu a gabansu ba.
Zayyan daga baya ya yiwa su malam bayanin IVF na asibiti aka yi mata, kuma malam a matsayin shi na babban malami bai yi challenging IVF ba, ya dubeshi ta kowacce fuska ta addini bai ga inda ya zama haramtacce ba.
Don haka ya bisu da addu’a da fatan Allah ya sauki Safiyyah lafiya.
Yanzunma Sabah da Rayyah data turawa Safiyya tana da tabbacin zasu iya, shiyasa ta turo su tunda Anti Dije bazata bar gidanta taje jegonta ba, amma hankalinta bakidaya yana kan babbar ‘yarta mafi soyuwa a ranta “Nana Safiyyah”. Dare da rana tana yi mata addu’ar sauka lafiya da samun saukin nakuda a kowacce sallahr farillarta.
Da murna da doki sosai su Sabah suke shirin tafiya Abuja, don kwatakwata tun komawarsu Safiyyah can bai fi sau biyu suka taba zuwa gidan Yayar tasu ba, shima dubiyarta suka je da bata da lafiya, na farkon kuma sun je ganin gidan ne sanda zasu koma can da zama, malam baya barinsu sam, don kowacce da maganar aurenta a kanta in ka dauke Rayha autar Ammi.
A motar haya su Rayyah suka tafi Abuja su biyu. Tun kafin su iso Safiyyah ta ware musu dakin da zasu sauka cike da dokin ganin kannen nata, ta aje masu duk abinda ta san zasu bukata, wannan shine zuwansu Abuja karo na biyu tun dawowarsu Safiyya nan daga Zaria.
Sabah dama tafi Rayyah baki, kuma tafi duk sauran kannenta faram-faram da jama’ah. Tunda Zayyan ya je dauko su a tashar Jabi tana gidan gaba Rayyah na baya, shida ita suke hirar tsokanar juna a cikin motar. Zayyan yana tsokanarta da amaryar robarshi, tazo bikon shi, taga baya zuwa zance yanzu, Sabah tace “haba dai inzo bikon ka, na dai zo taron Da na wallahi, kaima kasan kayi min tsufa Yaya Zayyan”, Zayyan yak ama baki ciki dariya da mamaki yace “really? Rayyah, yaushe ‘yar kauyen matar nan ta kile haka?”
Rayyah dai dariya take tana jinsu. Sabah ta kara cewa “Saboda Allah Rayyah nida nake da sarbadeden saurayi irin Jabir a gefe, yaro matashi me jini a jika, dan late twenties, me zan yi da Yaya Zayyan? Wannan kayan tsufan ai sai Nana Safiyyah”.
Zayyan ya tuntsure da dariya harda bugun sityari yace “amma kin yankeni! Saina gayawa Sophie, kina kira ma darling dinta tsufa tun yanzu”.
Tunda su Sabah suka zo gidan suke wani irin kula da Safiyyah da komai na kulawar gidan ya koma wuyansu, ko tsinke basa bari ta kawar, ko abinci taci nan zasu kawo mata ruwa ta wanke hannu daga zaune. Zayyan kuma ya wadatasu da kayan dadi suke ta fama, duk fitar da yayi ya dawo sai ya riko musu abinmotsa baki, musamman Rufaida Yughurt da Rufaidah Shawarma da Pizza din Dominos da suke matukar so.
Yanzu kam kowa yaga Sophie ya san dan cikin ta ya gama duk wani shirye-shiryensa na isowa duniya. Tashi sai da dabara kwanciya ma haka.
**** ***** ****