Sashe 14
Kasaita Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sama da mintuna ashirin ina haka wanda tuni har tunanina ya bani in bugawa Aunty waya in ce a zo a tafi da mu. Hannu na ji an sa an shafi gashin kaina ɗan motsi da numfashi su suka sa na yi saurin ɗaga kaina saboda in ga mai taɓa mini gashina. Yarima ne ke kallona yana murmushi, na yi wata sassanyar ajiyar zuciya na dinga murmushin daɗi don ma ina jin kunyarsa da tuni na yi tsalle.
Na tashi da sauri na dawo saman gadon na faɗa jikinsa ya mayar da hannuwansa ya rungume ni ina jin shi yana ta shafa gashin kaina, alamar lallashi ina jinsa yana ƙoƙarin ya ɗago ni amma na rungume shi tamau, ina jinsa ya faɗi kalmomin nan da harshen Turanci.
"Yasmin do you love me now? Zaki iya sakin jiki da ni?"
Na ɗaga kaina wanda ke ƙwance a tsokar naman kafaɗarsa.
Tabbas murnar Yarima ta fito fili,dana amsa masa ina son shi, ya ɗauke ni baki ɗaya ya ɗora ni a gadon da yake ƙwance, ya mayar da ni ya ƙwantar a ƙirjinsa ya janyo bargo ya lulluɓe mu a ciki, fuskokinmu kawai ke waje, na ɗago na ce masa.
"Ka samu sauƙi?"
Ya yi murmushin da yasa na ji sabuwar kunyarsa ta dirar mini sannan ya ɗaga kai alamar eh, wanda jin ɗaga kan kawai nayi saboda ni tuni na mayar da kaina a ƙirjinsa na ƙwantar.
Lallai yanzu zuciyata da gangar jikina sun amince mini da ina son Yarima,su ma kansu son Yarima ya cika su dama. Na yi sauri na ɗan yi alamar zan tashi ya ruƙo gashina ta bayana, na juyo da sauri har da ƴar ƙara da ido da kai ya tambaye ni ina zani? Na sunkuyar da kaina ina murmushin da yake fita tare da ƴan ragowar hawayen idanuwana.
"Magani zan É—auko maka, likita ne ya ce da ka tashi na baka."
Da kai ya nuna mini cewa inje na ɗauko, ina murmushin mamaki na cikin zuciya kenan bai fito fili ba, saboda mamakin yanda Yarima ya ƙware da maganar kai ko da yake ba mamaki idan na yi la'akari da farkon haɗuwata da shi yanda ya yi wa dogarawansa magana da gilashin hannunsa.
Bayan na kama shi ya tashi zaune na taimaka masa na jingina shi jikin kan gado wanda nasa filo a bayansa sannan na zauna kusa da shi na miƙa masa maganin da ruwa a kofi, maganin ƙwaya ɗaya ne ɗan ƙarami, sannan na ƙara janyo kujerar da na ɗora ɗan farantin da kofin maganin na ajiye kofin sannan na miƙa masa kofin ruwan madara ya shanye.
Saboda magriba ta kawo jiki,in na yi la'akari kamar a ce ƙarfe shida na Nigeriya kenan, wannan yasa na ce ya yi ƙoƙari ya je ya shiga ruwan ɗumi a banɗaki ko ya samu ƙarfin jikinsa sosai,bai yi mini gardama ba ya miƙe abinka ga namiji sai na ga baya ko irin ɗan tangaɗin nan na marasa lafiya.
Ina zaune ni kuwa na rabka uban tagumi a gefen gado ina jiran ya fito, wanda tuni na tafi duniyar tunanina, na da Yarima ya mutu da ya zan yi? Ba don komai ba sai don yanda zuciyata ta fara nutsuwa wajen son zama da shi a matsayin mijin aurena,wai don shirme sai na ji hawaye sun taho na samu na lumshe idanuwana su kuwa suka ci gaba da gangarowa.
Ban ji fitowarsa ba, saboda idanuwana a lumshe suke, kuma linzamin tunanina ya canja salo ya koma tunanin abubuwan son da Yarima ya nuna min a fili, na tuna ranar da ya mallake ni a matsayin matarsa irin nuna so da ƙaunar da ya yi mini a wannan daren ƙwaya ɗaya cal.
Jin an sumbaci laɓɓan bakina shi yasa na dawo daga duniyar tunanin da na tafi, na buɗe lumsassun idanuwana sai na ga Yarima tsaye a kaina, na yi saurin ƙwantar da kaina a cinyata na ce, "Kai Yarima."
Cikin kunnena ya ce, "Ke Yasmin me ye.?"
Na ɗaga ɗanyatsa na nuna shi, "Me ye,tawul, Yasmin sai in ƙi ɗauro tawul ni da matata ni ne fa kawai a ɗakin"
Da jin yanda sautin maganar ke fita ka san Yarima bai saba da yawan magana ba, saboda cikin nutsuwa yake yin ta.
"Ki É—ago Yasmin na zama naki fa."
Na girgiza kaina.
"Sai kasa riga."
Ina jin sa ya zauna dab da ni tabbas na ji sunkuyowarsa daidai da kunnena, saboda jin hucin numfashinsa, madadin ya yi magana sai dai kawai na ji ya hura kunnena,tsigar naman jikina na ji ta yamutsa, na rasa ya zan yi sai dai kawai na koma gado na ƙwanta a ƙudundune.
Haɗani ya yi ya rungume a ƙirjinsa, amma ta bayana, kalaman da suke fita daga bakinsa su suka sakani na ji ɗakin na juyawa da gadon da nake ƙwance, jin ya ƙara hura mini saitin ƙofar kunnena yasa na mirgina ɗaya kusa da shi na samu na miƙe na gudu, na shiga banɗaki, saboda na san nan kaɗai ne in na shiga na tsira, shi ma idan na kulle saboda ƙaton falo ne da ɗaki ɗaya kawai su ne ɗakunan hotel ɗin.
Na kulle ƙofar, amma sai na ji na jingina da ita tare da sulalewa ƙasa na zauna, kai sai na ji ina jin kunya ni kaɗai a banɗaki, na ƙudundune kaina jikin cinyata, na dinga murmushin da zan iya kiranshi na daɗi,wai don tsananin shirme irin nawa da na ɗaga fuskata sai in mayar wai kunya nake ji.
Sai da na ƙwashi wajen mintuna sha uku a haka, sannan na yi sauri na miƙe tsaye saboda tunanin da na ji ya faɗo mini a take,shi ne sallah na san bai fi sauran mintuna a kira sallah ba,ko kuwa in ce lokacin sallah ya yi tun da garin arnaku muke balle mu samu kunnuwanmu da jin kiran Sallah.
Na saɓule kayan dukkansu a gaban ƙaton madubinsu na banɗaki na kalli kaina tas na yi murmushi ganin ba ni da ko ƙwantalan ƙurji a dukkan jikina ballantana tabo, sannan ko'ina na jikina farinsu ɗaya,in an ɗauke saman tsokar ƙirjina.
Na shige ƙwami na zauna dirshen sannan na saki famfunan dukkan biyun ɗaya na zubo da ruwan zafi ɗayan kuwa na sanyi yake ƙwararo min, cikin ɗan gaggawa na gama wankana,gudun kada Yarima ya jira ni da yawa, saboda na san shi mutum ne mai son jam'i. Ina fita sanye da rigar wanka,shi kuma yana sallame sallah.
A zuciyata na ce har ya ƙagara. Na ɗauki kayana riga da wando,wandon ruwan baƙi ne rigar kuwa mai dogon hannu ce ruwan madara, sannan rigar ba ta wuce ƙugu ba, na fito na zauna gaban madubi na yi gaggawar shafa ɗan Wetlips kawai nasa a laɓɓana, na taje gashin kaina na ɗaure shi na sakeshi a baya, sai kuwa turaran da na feshe jikina da shi.
Alkyabbata na zura domin gabatar da sallah, ina isa wajen da na keɓe mana domin sallah na ga Yarima ya miƙe, sannan ya ce mini "Bismillah." Sai wannan lokacin tunani ya faɗo mini cewa nafila ce Yarima ya yi irin waɗannan halayyar ta son Addininsa yana ba ni mamaki, saboda ban taɓa tunanin yana ma sallah ba, ballantana ya iya riƙe Addininsa da hannu bibbiyu, balle da na je gidan yari na ga irin yanda yake baiwa jama'a wahala, ga mulki har na fitar hankali.
Bayan mun gama ne na ji ya ɗaga hannu sama yana jero sunayen Allah gaba ɗayansu daga nan kuwa na ji ya faɗa ga addu'ar Allahumma izzal Islama wal Muslimin har ƙarshenta, sannan ya rufe da wata addu'a wacce tun ina yarinya na ji ana yi mana ita, abin da ya bani mamaki kuma sai na ji ya rufe da ɗayar ma wacce zan ce kowa tun yana yaro ma ya iya ta.
_Rabbana atina fidduniya hasanatan wafil alkhirati hasanatan waƙina azaban nari._ _Rabbana latuziƙ ƙulubana ba ada izhadaitana wahablana min ladin ka rahamatan innaka antal wahab._
A take na tuna da malamin islamiyyarmu da yake ce mana ana son duk sallah a dinga karanta ta,falalarta Allah kaɗai ya san yawansa, sai dai yawan yin ta na kawo arziƙi duniya da lahira.
Hankalina na ji ya ƙara nutsuwa a kan Yarima,ganinsa yanda yake kula da Addininsa. Muna kammalawa ya miƙe ya gabatar mana da sallar isha'i ni dai gaskiya na ji mamaki matuƙa a kan yanda na ga Yarima na tafiyar da rayuwarsa,in na yi la'akari da yanda yake a baya, mutumin da ko motsi ma baya iya yi sai dai a yi masa.
Bayan kammala addu'armu ne na ga ya tashi ya buɗe aƙwatinsa ni kuwa sai bin shi nake da kallon mamaki, wasu kaya na ga ya ɗauko da alama dai na mata ne, ya zauna saman gado sannan na ji ya kira ni na tashi na je inda yake, nima na zauna a gefensa.
"WaÉ—annan kayan nake son ki saka mini su yanzu,zamu fita mu ci abinci a can."
Riga ce doguwa har ƙasa take, amma sai ɗan siririn hannunta, sai kuwa ƴar samanta mai dogon hannu har izuwa wuyan hannunta, dole ta sa na tattare su na matse a tsakanin cinyata,gudun kada su ja ƙasa,a cikin banɗaki na isa gaban madubin banɗakin na tare gashin kaina na ɗaure shi da ɗan mayafin da na gani maƙale a jikin kayan, na yi murmushi ganin na yi mugun ƙyau, abin ka ga kalar jinin kare, sai kuwa dogayen hannuwan rigar, amma ragowar jikinsu kuwa duk jinin kare ne (Maroon colour).
Na fito ina murmushi, sannan na yi saurin sakin rigar sai na ga take ta saman tsakanina da ɗan leɓunta zai kai taku biyu ta cikin ce kawai ke ƙwance a daidai ƙafafuna. Na isa bakin madubi na zauna domin gyara fuskata, na gyare ta da wata irin hodar da take fitowa da ainihin kalar fatar jikinka,jan baki kuwa kalar kayana na saka, jinin kare kenan,dan in ƙarasa zama su turawan har ma gashin ido na saka, gashin ya yi tsaye abin gwanin ban sha'awa.
Na tashi da sauri na dawo saman gadon na faɗa jikinsa ya mayar da hannuwansa ya rungume ni ina jin shi yana ta shafa gashin kaina, alamar lallashi ina jinsa yana ƙoƙarin ya ɗago ni amma na rungume shi tamau, ina jinsa ya faɗi kalmomin nan da harshen Turanci.
"Yasmin do you love me now? Zaki iya sakin jiki da ni?"
Na ɗaga kaina wanda ke ƙwance a tsokar naman kafaɗarsa.
Tabbas murnar Yarima ta fito fili,dana amsa masa ina son shi, ya ɗauke ni baki ɗaya ya ɗora ni a gadon da yake ƙwance, ya mayar da ni ya ƙwantar a ƙirjinsa ya janyo bargo ya lulluɓe mu a ciki, fuskokinmu kawai ke waje, na ɗago na ce masa.
"Ka samu sauƙi?"
Ya yi murmushin da yasa na ji sabuwar kunyarsa ta dirar mini sannan ya ɗaga kai alamar eh, wanda jin ɗaga kan kawai nayi saboda ni tuni na mayar da kaina a ƙirjinsa na ƙwantar.
Lallai yanzu zuciyata da gangar jikina sun amince mini da ina son Yarima,su ma kansu son Yarima ya cika su dama. Na yi sauri na ɗan yi alamar zan tashi ya ruƙo gashina ta bayana, na juyo da sauri har da ƴar ƙara da ido da kai ya tambaye ni ina zani? Na sunkuyar da kaina ina murmushin da yake fita tare da ƴan ragowar hawayen idanuwana.
"Magani zan É—auko maka, likita ne ya ce da ka tashi na baka."
Da kai ya nuna mini cewa inje na ɗauko, ina murmushin mamaki na cikin zuciya kenan bai fito fili ba, saboda mamakin yanda Yarima ya ƙware da maganar kai ko da yake ba mamaki idan na yi la'akari da farkon haɗuwata da shi yanda ya yi wa dogarawansa magana da gilashin hannunsa.
Bayan na kama shi ya tashi zaune na taimaka masa na jingina shi jikin kan gado wanda nasa filo a bayansa sannan na zauna kusa da shi na miƙa masa maganin da ruwa a kofi, maganin ƙwaya ɗaya ne ɗan ƙarami, sannan na ƙara janyo kujerar da na ɗora ɗan farantin da kofin maganin na ajiye kofin sannan na miƙa masa kofin ruwan madara ya shanye.
Saboda magriba ta kawo jiki,in na yi la'akari kamar a ce ƙarfe shida na Nigeriya kenan, wannan yasa na ce ya yi ƙoƙari ya je ya shiga ruwan ɗumi a banɗaki ko ya samu ƙarfin jikinsa sosai,bai yi mini gardama ba ya miƙe abinka ga namiji sai na ga baya ko irin ɗan tangaɗin nan na marasa lafiya.
Ina zaune ni kuwa na rabka uban tagumi a gefen gado ina jiran ya fito, wanda tuni na tafi duniyar tunanina, na da Yarima ya mutu da ya zan yi? Ba don komai ba sai don yanda zuciyata ta fara nutsuwa wajen son zama da shi a matsayin mijin aurena,wai don shirme sai na ji hawaye sun taho na samu na lumshe idanuwana su kuwa suka ci gaba da gangarowa.
Ban ji fitowarsa ba, saboda idanuwana a lumshe suke, kuma linzamin tunanina ya canja salo ya koma tunanin abubuwan son da Yarima ya nuna min a fili, na tuna ranar da ya mallake ni a matsayin matarsa irin nuna so da ƙaunar da ya yi mini a wannan daren ƙwaya ɗaya cal.
Jin an sumbaci laɓɓan bakina shi yasa na dawo daga duniyar tunanin da na tafi, na buɗe lumsassun idanuwana sai na ga Yarima tsaye a kaina, na yi saurin ƙwantar da kaina a cinyata na ce, "Kai Yarima."
Cikin kunnena ya ce, "Ke Yasmin me ye.?"
Na ɗaga ɗanyatsa na nuna shi, "Me ye,tawul, Yasmin sai in ƙi ɗauro tawul ni da matata ni ne fa kawai a ɗakin"
Da jin yanda sautin maganar ke fita ka san Yarima bai saba da yawan magana ba, saboda cikin nutsuwa yake yin ta.
"Ki É—ago Yasmin na zama naki fa."
Na girgiza kaina.
"Sai kasa riga."
Ina jin sa ya zauna dab da ni tabbas na ji sunkuyowarsa daidai da kunnena, saboda jin hucin numfashinsa, madadin ya yi magana sai dai kawai na ji ya hura kunnena,tsigar naman jikina na ji ta yamutsa, na rasa ya zan yi sai dai kawai na koma gado na ƙwanta a ƙudundune.
Haɗani ya yi ya rungume a ƙirjinsa, amma ta bayana, kalaman da suke fita daga bakinsa su suka sakani na ji ɗakin na juyawa da gadon da nake ƙwance, jin ya ƙara hura mini saitin ƙofar kunnena yasa na mirgina ɗaya kusa da shi na samu na miƙe na gudu, na shiga banɗaki, saboda na san nan kaɗai ne in na shiga na tsira, shi ma idan na kulle saboda ƙaton falo ne da ɗaki ɗaya kawai su ne ɗakunan hotel ɗin.
Na kulle ƙofar, amma sai na ji na jingina da ita tare da sulalewa ƙasa na zauna, kai sai na ji ina jin kunya ni kaɗai a banɗaki, na ƙudundune kaina jikin cinyata, na dinga murmushin da zan iya kiranshi na daɗi,wai don tsananin shirme irin nawa da na ɗaga fuskata sai in mayar wai kunya nake ji.
Sai da na ƙwashi wajen mintuna sha uku a haka, sannan na yi sauri na miƙe tsaye saboda tunanin da na ji ya faɗo mini a take,shi ne sallah na san bai fi sauran mintuna a kira sallah ba,ko kuwa in ce lokacin sallah ya yi tun da garin arnaku muke balle mu samu kunnuwanmu da jin kiran Sallah.
Na saɓule kayan dukkansu a gaban ƙaton madubinsu na banɗaki na kalli kaina tas na yi murmushi ganin ba ni da ko ƙwantalan ƙurji a dukkan jikina ballantana tabo, sannan ko'ina na jikina farinsu ɗaya,in an ɗauke saman tsokar ƙirjina.
Na shige ƙwami na zauna dirshen sannan na saki famfunan dukkan biyun ɗaya na zubo da ruwan zafi ɗayan kuwa na sanyi yake ƙwararo min, cikin ɗan gaggawa na gama wankana,gudun kada Yarima ya jira ni da yawa, saboda na san shi mutum ne mai son jam'i. Ina fita sanye da rigar wanka,shi kuma yana sallame sallah.
A zuciyata na ce har ya ƙagara. Na ɗauki kayana riga da wando,wandon ruwan baƙi ne rigar kuwa mai dogon hannu ce ruwan madara, sannan rigar ba ta wuce ƙugu ba, na fito na zauna gaban madubi na yi gaggawar shafa ɗan Wetlips kawai nasa a laɓɓana, na taje gashin kaina na ɗaure shi na sakeshi a baya, sai kuwa turaran da na feshe jikina da shi.
Alkyabbata na zura domin gabatar da sallah, ina isa wajen da na keɓe mana domin sallah na ga Yarima ya miƙe, sannan ya ce mini "Bismillah." Sai wannan lokacin tunani ya faɗo mini cewa nafila ce Yarima ya yi irin waɗannan halayyar ta son Addininsa yana ba ni mamaki, saboda ban taɓa tunanin yana ma sallah ba, ballantana ya iya riƙe Addininsa da hannu bibbiyu, balle da na je gidan yari na ga irin yanda yake baiwa jama'a wahala, ga mulki har na fitar hankali.
Bayan mun gama ne na ji ya ɗaga hannu sama yana jero sunayen Allah gaba ɗayansu daga nan kuwa na ji ya faɗa ga addu'ar Allahumma izzal Islama wal Muslimin har ƙarshenta, sannan ya rufe da wata addu'a wacce tun ina yarinya na ji ana yi mana ita, abin da ya bani mamaki kuma sai na ji ya rufe da ɗayar ma wacce zan ce kowa tun yana yaro ma ya iya ta.
_Rabbana atina fidduniya hasanatan wafil alkhirati hasanatan waƙina azaban nari._ _Rabbana latuziƙ ƙulubana ba ada izhadaitana wahablana min ladin ka rahamatan innaka antal wahab._
A take na tuna da malamin islamiyyarmu da yake ce mana ana son duk sallah a dinga karanta ta,falalarta Allah kaɗai ya san yawansa, sai dai yawan yin ta na kawo arziƙi duniya da lahira.
Hankalina na ji ya ƙara nutsuwa a kan Yarima,ganinsa yanda yake kula da Addininsa. Muna kammalawa ya miƙe ya gabatar mana da sallar isha'i ni dai gaskiya na ji mamaki matuƙa a kan yanda na ga Yarima na tafiyar da rayuwarsa,in na yi la'akari da yanda yake a baya, mutumin da ko motsi ma baya iya yi sai dai a yi masa.
Bayan kammala addu'armu ne na ga ya tashi ya buɗe aƙwatinsa ni kuwa sai bin shi nake da kallon mamaki, wasu kaya na ga ya ɗauko da alama dai na mata ne, ya zauna saman gado sannan na ji ya kira ni na tashi na je inda yake, nima na zauna a gefensa.
"WaÉ—annan kayan nake son ki saka mini su yanzu,zamu fita mu ci abinci a can."
Riga ce doguwa har ƙasa take, amma sai ɗan siririn hannunta, sai kuwa ƴar samanta mai dogon hannu har izuwa wuyan hannunta, dole ta sa na tattare su na matse a tsakanin cinyata,gudun kada su ja ƙasa,a cikin banɗaki na isa gaban madubin banɗakin na tare gashin kaina na ɗaure shi da ɗan mayafin da na gani maƙale a jikin kayan, na yi murmushi ganin na yi mugun ƙyau, abin ka ga kalar jinin kare, sai kuwa dogayen hannuwan rigar, amma ragowar jikinsu kuwa duk jinin kare ne (Maroon colour).
Na fito ina murmushi, sannan na yi saurin sakin rigar sai na ga take ta saman tsakanina da ɗan leɓunta zai kai taku biyu ta cikin ce kawai ke ƙwance a daidai ƙafafuna. Na isa bakin madubi na zauna domin gyara fuskata, na gyare ta da wata irin hodar da take fitowa da ainihin kalar fatar jikinka,jan baki kuwa kalar kayana na saka, jinin kare kenan,dan in ƙarasa zama su turawan har ma gashin ido na saka, gashin ya yi tsaye abin gwanin ban sha'awa.