Sashe 27
Hamshakiya Uwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ni kuwa ina nan , banyi barci ba, inma ya dan sace ni, kadan sai na farka sai na kira sunanta, sai ta amsa. Karshe dai na tashi nayi alwalla zan tada salla sai naji muryar ta tana cewa lokacin salla ya yi ne? Nace a a ina son inyi salla in fadawa Allah ya baki lafiya da nisan kwana. Ta ya fito ni da hannu naje, tace zan sake neman alfarma. Nace To Tace "Dan Allah in Shamaki ya yi miki laifi dan Allah in zaki masa hukunci ki tausaya ki tuna da ni ki yi masa rangwanme. Hawaye suka sakko mata. Na ce Hajiya na fahimci kaunarki da Shamaki insha Allah zai baki sauki. Tace je kiyi salla ki roka min sassauci a gurin Allah. Na juya na tada salla zuwa yanzu bana iya kuka sai dai suyar zuciya. Na kasa ci ko ruwa na kurba sai inji daci.
Lokaci da na idar bacci ya dauketa domin ina jin numfashinta da karfi ya koma. Na ji dadi bacci ya dauke ta. Da safe likita ya shigo, muka gaisa ya tambayi jiki lokacin ya nufi gurinta, sai naga ya firgita, ya dakko jakar da ya zo da ita ya bude ya ciro wata allura ya hada ya yi mata. Ya daga wayar sa ya kira yana Indianci. Ba jimawa kuma sai naji motar Asibiti. Haka muka tafi asibitin ina jin zuciya ta kamar ta fado kasa. Likitoci suna ta kai kawo an hana ni shiga dakin amma ina kallo window. Cikin dare Hajiya rai ya yi halinsa. Ashe bacci da nake zaton ta yi ta shiga doguwar suma ne.
Likitan ya maida ni wannan gidan ya fada min za su adana gawar Hajiya sannan zai kira lambar da Hajiya ta bashi tace ya kira in ta cika a kira a sanar musu.
Cikin wannan jimamin aka kira Shamaki aka sanar da shi rasuwar Hajiya. Ta fiyar ba shiri ta tashi dan haka Shamaki da mazan yayin shi guda biyu suka tafi domin taho da gawar Hajiya.
Gidan likitan ya kai ni domin ba zan iya zama a wannan katon gidan ba, na kasa ci na kasa sha kuma na kasa kuka, ajiyar zuciya kawai nake yi iyalan likitan suna ta faman lallashina. Duk da banajin yarensu. Dole likitan ya daura min ruwa saboda na Ki cin komai. Shamaki kawai nake son gani.....
......
Bacci ya fara fizagata sai naji an dafa goshina, da sauri na bude ido. Shamaki ne, yana tsaye. Na tashi da sauri ina kallon shi kamar wadda na warke makanta duk ya fita a hajjacin shi. Zanyi kuka sai na tuna da muryar Hajiya kamar a lokaci tana fadin na baki amanar Shamaki.
Na bude baki zan yi masa magana, sai kuka ya kufce min. Ya zauna a bakin gadon bai iya furta komai ba. Na ce Shamaki mun rasa Hajiya. Ya daga kai, da kyar ya furta ta so muje. Munyi sallama da iyalan likita ya rakamu har mota. Ashe sunje sun kwaso kayanmu a wannan gida.
Lagos muka sauka, daga nan muka wuce Kano. Naga dauriyar Shamaki duk da ko magana baya iyawa sai dai da kai.
Dama anyo mata wanka tun acan na ba su duk wani abu data bada ayi mata amfani da shi kuma sunyi. Gidan ya yi cikar kwari dam da Jama'a haka muka iso Muna shigowa Falon Hajiya aka aje ta.
Na zauna ina kallon yadda yaranta suke zuwa suna yi mata addu'a, na kara tabbatar wa Duniya zancen banza ne, da kudi ko kauna ko dangata ko sanayya suna hana mutuwa da baza a fita da Hajiya daga wannan Hamshakin falon nata ba.
Haka suka gama yi mata addu'a aka fita da ita. 'Ya'yanta suna ji suna gani, Maman Nana har suma ta yi, Maman Iman ta tada aljanu amma haka aka tafi da ita.
Ummana suna gidan su da su Umman Amina, Abba da Abban Zuhra duk da su aka yi jan iza sun dawo daga makabarta su ka kirani muna gaisawa suna min ta aziyya aka ce ga Shamaki can anyi Asibiti da shi ya ki tasowa daga gaban kabarin Hajiya, da aka kamoshi sai ya zube a sume. Da sauri na ce wane Asibitin aka kai shi, sai aka ce wai inyi hakuri maza suje. Nace a a ni sai naje. Maman Umar ta dauke ni a mota muka tafi.
Yana kwance a gadon tamkar mai bacci, nace Maman Umar ya farfadone? Tace "E bacci yake yi. Nace zan jira ya farka, tace inzo muje akwai su Baban Umar a nan din in ya farka sai a dawo da ni.". Nace kuyi hakuri ba taurin kai zan muku ba kubarni na soma kuka ina fadin Hajiya ta bani amanar shi, ta maimaita min har a kalamanta na karshe tsakanina da ita. Dole suka barni suka tafi.
Kamar awa daya, sai ya yi mika da salati ya farka sai kuma ya mike zaune da sauri yana kallona, ya kalli dakin,yace "Baby da gaske ne Hajiya ta rasu? " Na ce Shamaki muyi hakuri Hajiya ta yi kyakykyawan karshe kuma ta tafi tana sa muku albarka. Ba ta bukatar komai sai addu'armu. Ka kwantar da hankali muna yi mata kyakykyawa zato. Yace nifa Baby abinda ya bani mamaki Hajiya lafiya lau take sai dan zazzabi dama ba ke ta kai ba kamar dai yadda muka zata. Nace haka muke kallo. Ashe Hajiya tana dauke da ciwon Cancer tsawon lokaci. Ta fada min cewa tun a lokacin haihuwar ka, kuma ta fada min shekaru biyar baya likitoci suka gano cewa bazata wuce wannan lokacin ba.
Ya soma girgiza kai hawaye suna zuba, yace "Amma me yasa Hajiya zata boye min wannan maganar. " Nace na gamsu da dalilin Hajiya, tacev in ta rasa muku baza ku rayu cikin farin ciki ba, zaku rayu a cikin damuwa da fargaba da lissafi. Ya sauke ajiyar zuciya ya ce "Allah sarki Hajiyata, shike nan mun rabu, Allah ka sakata a dausayin rahama. Baby ina ganin fa na gama farinciki a Duniya,. " Ya sake fashewa da kuka.
To a haka likita ya same mu. Shamaki yace zamu tafi tunda shi ba wai maganin damuwarshi zai samu a wannan Asibitin ba. Likita ya kada ya raya, aka Shamaki ya kwana a kara duba shi, amma Shamaki ya ki. Gashi ba mota da zamu tafi, ba wanda ya zo da waya cikinmu. Sai likitan ne ya kaimu gida
. Haka aka ci gaba da zaman makoki, na tausayawa, Azima, ga tsohon ciki ga tashin hankalin rashin Hajiya. Aka yi addu'ar uku aka watse, kullum Shamaki a kabarin Hajiya ya ke yini kamar mahaukaci sai an Kamo shi an sako a mota. Abinci kuwa sai na matsawa Shamaki yake iya kurbar dan shayi ko 'yar fura. Yace shifa ba zai iya ci gaba da zama a wannan gidan ba matsawar dai ba Hajiya a cikin shi.
Duk da na sa an dauke kujerar Hajiyar ankai dakinta. A daddafe aka yi bakwai ya sa aka yi feti a wani gidan sa dake Rafin Danana yace can zamu koma. Duk ya birkice kasuwa ma baya fita. Wai in ya dawo wa zai taya shi lissafi nace masa ni ce.
Yace "To ya nake gani game da Azima in zata zauna da mu. Nace kar muyi gaban kanmu ka kira Maman Umar ta kira duk sauran yayinka mu zauna a kira Azima aji ra'ayinta. Yace shikenan tunda Hajiya tace komai inyi shawara dake mu tattauna ai duk yadda ki ka ce haka zanyi.
Aka kira su muka zauna gaba dayanmu aka kirata. Jikinta ya yi sanyi tace tafi son mu zauna tare. Kowa ya ji dadin haka. Maman Iman tace Allah sarki Hajiya ta, yanzu shikenan haka gidan zai ci gaba da zama tarihin gidan ya shafe! "
Shamaki yace "Za a samu ko a dangi a ba wasu aro su zauna matsawar ina gidan nan har in mutu zan rayu a cikin tashin hankali. Aka sa ranar tarewarmu sati biyu da rasuwar Hajiya. Jamila da Zuhra sunzo mana aranar tarewar.
Shima dai gida babbane kowacce da gefenta shima da nasa, a nawa gefen na fidda dakin su Meema da Rahin mai kula da su. Su Tabawa da Juma dakinsu yana kusa da babban kicin. Haka muka dawo wata sabuwar rayuwa mara kan gado, abubuwa duk sun dagule mana sun canza.
Munfi karfin wata biyu ko yatsana Shamaki bai kama ba da sunan auratayya zamu kwanta guri daya muna manne da juna kila kafin muyi bacci sai mun yi maganar Hajiya munsha kuka, ko yaushe maganar shi bata wuce ta Hajiya. Gashi kullum yana hanyar makabarta. Sai da fa Maman Umar ta amso mishi tofi a gurin malamai wandan da suke yi mana saukar kur'ani so biyu a sati.
Sannan aka dan samu ya dangana. Azima ta wayi gari da ciwon nakuda, Shamaki ya kaimu Asibiti, ta sauka lafiya dama tun a hoto ya nuna mace za a haifa. Ita ma dai Zeena ce, amma aka sa mata Safna. Shamaki yace babu taron suna domin shi dai farin cikin shi ya tafi, yanzu kawai yana rayuwa ne kafin tashi mutuwar ta zo. Haka dai ina lallabashi har ya fara fita kasuwa a hankali ya fara warwarewa,
wata safiyar lahadi an tashi da ruwan sama gari ya dauki sanyi ya kara kankame ni muna baccin safe, a kunne ya rada min cewa Baby ina jin kamar shi 'awata ta dawo. Nace to ko zamu gwada mu gani. Yace gaskiya dai. To ranar kwanan Hajiya dari ba uku da rasuwa wata uku da kwana bakwai sannan Shamaki ya iya saduwa. Tun daga ranar kuma sai komai ya soma canzawa. Ina matukar kokarin ganin naji da kowa a cikin dangin nan. Shawara komai Shamaki dani yake yi. Haka nan lissafin dayake ina dan sauraren da Hajiya ina dan fahimta kuma ina taimaka masa a yanzu.
Yara kuwa duk yadda na tsara zan kula da yarana in Allah ya bani haka nake kula da su, Meema ina mu amalantar Azima daidai da yadda nake ganin nayi mata adalci ba nai mata kallon kishiya.haka nan bana bari Shamaki yana hantarar ta kamar da. Ina fada mishi itama amana ce a gurina.
Lokaci da na idar bacci ya dauketa domin ina jin numfashinta da karfi ya koma. Na ji dadi bacci ya dauke ta. Da safe likita ya shigo, muka gaisa ya tambayi jiki lokacin ya nufi gurinta, sai naga ya firgita, ya dakko jakar da ya zo da ita ya bude ya ciro wata allura ya hada ya yi mata. Ya daga wayar sa ya kira yana Indianci. Ba jimawa kuma sai naji motar Asibiti. Haka muka tafi asibitin ina jin zuciya ta kamar ta fado kasa. Likitoci suna ta kai kawo an hana ni shiga dakin amma ina kallo window. Cikin dare Hajiya rai ya yi halinsa. Ashe bacci da nake zaton ta yi ta shiga doguwar suma ne.
Likitan ya maida ni wannan gidan ya fada min za su adana gawar Hajiya sannan zai kira lambar da Hajiya ta bashi tace ya kira in ta cika a kira a sanar musu.
Cikin wannan jimamin aka kira Shamaki aka sanar da shi rasuwar Hajiya. Ta fiyar ba shiri ta tashi dan haka Shamaki da mazan yayin shi guda biyu suka tafi domin taho da gawar Hajiya.
Gidan likitan ya kai ni domin ba zan iya zama a wannan katon gidan ba, na kasa ci na kasa sha kuma na kasa kuka, ajiyar zuciya kawai nake yi iyalan likitan suna ta faman lallashina. Duk da banajin yarensu. Dole likitan ya daura min ruwa saboda na Ki cin komai. Shamaki kawai nake son gani.....
......
Bacci ya fara fizagata sai naji an dafa goshina, da sauri na bude ido. Shamaki ne, yana tsaye. Na tashi da sauri ina kallon shi kamar wadda na warke makanta duk ya fita a hajjacin shi. Zanyi kuka sai na tuna da muryar Hajiya kamar a lokaci tana fadin na baki amanar Shamaki.
Na bude baki zan yi masa magana, sai kuka ya kufce min. Ya zauna a bakin gadon bai iya furta komai ba. Na ce Shamaki mun rasa Hajiya. Ya daga kai, da kyar ya furta ta so muje. Munyi sallama da iyalan likita ya rakamu har mota. Ashe sunje sun kwaso kayanmu a wannan gida.
Lagos muka sauka, daga nan muka wuce Kano. Naga dauriyar Shamaki duk da ko magana baya iyawa sai dai da kai.
Dama anyo mata wanka tun acan na ba su duk wani abu data bada ayi mata amfani da shi kuma sunyi. Gidan ya yi cikar kwari dam da Jama'a haka muka iso Muna shigowa Falon Hajiya aka aje ta.
Na zauna ina kallon yadda yaranta suke zuwa suna yi mata addu'a, na kara tabbatar wa Duniya zancen banza ne, da kudi ko kauna ko dangata ko sanayya suna hana mutuwa da baza a fita da Hajiya daga wannan Hamshakin falon nata ba.
Haka suka gama yi mata addu'a aka fita da ita. 'Ya'yanta suna ji suna gani, Maman Nana har suma ta yi, Maman Iman ta tada aljanu amma haka aka tafi da ita.
Ummana suna gidan su da su Umman Amina, Abba da Abban Zuhra duk da su aka yi jan iza sun dawo daga makabarta su ka kirani muna gaisawa suna min ta aziyya aka ce ga Shamaki can anyi Asibiti da shi ya ki tasowa daga gaban kabarin Hajiya, da aka kamoshi sai ya zube a sume. Da sauri na ce wane Asibitin aka kai shi, sai aka ce wai inyi hakuri maza suje. Nace a a ni sai naje. Maman Umar ta dauke ni a mota muka tafi.
Yana kwance a gadon tamkar mai bacci, nace Maman Umar ya farfadone? Tace "E bacci yake yi. Nace zan jira ya farka, tace inzo muje akwai su Baban Umar a nan din in ya farka sai a dawo da ni.". Nace kuyi hakuri ba taurin kai zan muku ba kubarni na soma kuka ina fadin Hajiya ta bani amanar shi, ta maimaita min har a kalamanta na karshe tsakanina da ita. Dole suka barni suka tafi.
Kamar awa daya, sai ya yi mika da salati ya farka sai kuma ya mike zaune da sauri yana kallona, ya kalli dakin,yace "Baby da gaske ne Hajiya ta rasu? " Na ce Shamaki muyi hakuri Hajiya ta yi kyakykyawan karshe kuma ta tafi tana sa muku albarka. Ba ta bukatar komai sai addu'armu. Ka kwantar da hankali muna yi mata kyakykyawa zato. Yace nifa Baby abinda ya bani mamaki Hajiya lafiya lau take sai dan zazzabi dama ba ke ta kai ba kamar dai yadda muka zata. Nace haka muke kallo. Ashe Hajiya tana dauke da ciwon Cancer tsawon lokaci. Ta fada min cewa tun a lokacin haihuwar ka, kuma ta fada min shekaru biyar baya likitoci suka gano cewa bazata wuce wannan lokacin ba.
Ya soma girgiza kai hawaye suna zuba, yace "Amma me yasa Hajiya zata boye min wannan maganar. " Nace na gamsu da dalilin Hajiya, tacev in ta rasa muku baza ku rayu cikin farin ciki ba, zaku rayu a cikin damuwa da fargaba da lissafi. Ya sauke ajiyar zuciya ya ce "Allah sarki Hajiyata, shike nan mun rabu, Allah ka sakata a dausayin rahama. Baby ina ganin fa na gama farinciki a Duniya,. " Ya sake fashewa da kuka.
To a haka likita ya same mu. Shamaki yace zamu tafi tunda shi ba wai maganin damuwarshi zai samu a wannan Asibitin ba. Likita ya kada ya raya, aka Shamaki ya kwana a kara duba shi, amma Shamaki ya ki. Gashi ba mota da zamu tafi, ba wanda ya zo da waya cikinmu. Sai likitan ne ya kaimu gida
. Haka aka ci gaba da zaman makoki, na tausayawa, Azima, ga tsohon ciki ga tashin hankalin rashin Hajiya. Aka yi addu'ar uku aka watse, kullum Shamaki a kabarin Hajiya ya ke yini kamar mahaukaci sai an Kamo shi an sako a mota. Abinci kuwa sai na matsawa Shamaki yake iya kurbar dan shayi ko 'yar fura. Yace shifa ba zai iya ci gaba da zama a wannan gidan ba matsawar dai ba Hajiya a cikin shi.
Duk da na sa an dauke kujerar Hajiyar ankai dakinta. A daddafe aka yi bakwai ya sa aka yi feti a wani gidan sa dake Rafin Danana yace can zamu koma. Duk ya birkice kasuwa ma baya fita. Wai in ya dawo wa zai taya shi lissafi nace masa ni ce.
Yace "To ya nake gani game da Azima in zata zauna da mu. Nace kar muyi gaban kanmu ka kira Maman Umar ta kira duk sauran yayinka mu zauna a kira Azima aji ra'ayinta. Yace shikenan tunda Hajiya tace komai inyi shawara dake mu tattauna ai duk yadda ki ka ce haka zanyi.
Aka kira su muka zauna gaba dayanmu aka kirata. Jikinta ya yi sanyi tace tafi son mu zauna tare. Kowa ya ji dadin haka. Maman Iman tace Allah sarki Hajiya ta, yanzu shikenan haka gidan zai ci gaba da zama tarihin gidan ya shafe! "
Shamaki yace "Za a samu ko a dangi a ba wasu aro su zauna matsawar ina gidan nan har in mutu zan rayu a cikin tashin hankali. Aka sa ranar tarewarmu sati biyu da rasuwar Hajiya. Jamila da Zuhra sunzo mana aranar tarewar.
Shima dai gida babbane kowacce da gefenta shima da nasa, a nawa gefen na fidda dakin su Meema da Rahin mai kula da su. Su Tabawa da Juma dakinsu yana kusa da babban kicin. Haka muka dawo wata sabuwar rayuwa mara kan gado, abubuwa duk sun dagule mana sun canza.
Munfi karfin wata biyu ko yatsana Shamaki bai kama ba da sunan auratayya zamu kwanta guri daya muna manne da juna kila kafin muyi bacci sai mun yi maganar Hajiya munsha kuka, ko yaushe maganar shi bata wuce ta Hajiya. Gashi kullum yana hanyar makabarta. Sai da fa Maman Umar ta amso mishi tofi a gurin malamai wandan da suke yi mana saukar kur'ani so biyu a sati.
Sannan aka dan samu ya dangana. Azima ta wayi gari da ciwon nakuda, Shamaki ya kaimu Asibiti, ta sauka lafiya dama tun a hoto ya nuna mace za a haifa. Ita ma dai Zeena ce, amma aka sa mata Safna. Shamaki yace babu taron suna domin shi dai farin cikin shi ya tafi, yanzu kawai yana rayuwa ne kafin tashi mutuwar ta zo. Haka dai ina lallabashi har ya fara fita kasuwa a hankali ya fara warwarewa,
wata safiyar lahadi an tashi da ruwan sama gari ya dauki sanyi ya kara kankame ni muna baccin safe, a kunne ya rada min cewa Baby ina jin kamar shi 'awata ta dawo. Nace to ko zamu gwada mu gani. Yace gaskiya dai. To ranar kwanan Hajiya dari ba uku da rasuwa wata uku da kwana bakwai sannan Shamaki ya iya saduwa. Tun daga ranar kuma sai komai ya soma canzawa. Ina matukar kokarin ganin naji da kowa a cikin dangin nan. Shawara komai Shamaki dani yake yi. Haka nan lissafin dayake ina dan sauraren da Hajiya ina dan fahimta kuma ina taimaka masa a yanzu.
Yara kuwa duk yadda na tsara zan kula da yarana in Allah ya bani haka nake kula da su, Meema ina mu amalantar Azima daidai da yadda nake ganin nayi mata adalci ba nai mata kallon kishiya.haka nan bana bari Shamaki yana hantarar ta kamar da. Ina fada mishi itama amana ce a gurina.