Sashe 19
Hamshakiya Uwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka nan su Juma sun na janye su ta hanyar nuna musu cewa duk daya muke da su, da kuma girmama su.Duk ranar da Shamaki ba ya gidan Azima to fa a dakinta na da zata kwana. Tun ina dariya kunsan halin kishi har na zo ina jin tausayin ta. Domin gaba daya Shamaki baya ganin kima ko darajar 'Azima.
Wata ranar lahadi na shigo falon Hajiya dan zuwa kicin muyi aikin abincin rana, sai na sha mamaki ganin Shamaki turus a gaban Hajiya ga Maman Umar zaune. Na gaida Maman Umar sannan nan na kalli Shamaki ransa a bace yake, Nace sannu da zuwa. Hannu kawai ya daga min. Hajiya kuma bata daina maganar da ta ke yi ba wai dan ganina. Na tsinci tana fadin " Na gama magana ya rage naka gidanka ne kuma matar ka ce duk abinda ka ga dama kuma zaka iya yi amma ni a nan na tsaya. " Na nufi kicin cikin faduwar gaba ko a kaina akeyin maganar na fara lissafi yanzu dai watana shidda a gidan Hajiya bare ince ko wa a dina ne ya iso a mugun yanayi, wato banci nasara ba.
Juma wadda na samu suna kuskus da Tabawa ta kalle ni, tace "Yawwa Uwar dakina, dama dai ina ta fatan ki fito domin kiji wani mugun labari, ni dai ina ganin lokacin barin aikina a gidan nan ya zo. na zaro ido cikin fargaba. Me zai sa ki bar inda ki ke samun abinci Baba Juma? Tace wai gidan yarinyar nan za a maida ni wannan marakunyar Azima. Ni kuma da in koma gurinta gara in hakura da aikin kawai gaba daya. " Nace A a Baba Juma, ki fara zuwa ki ga kamun ludayin zaman Idan kinga ba dama to sai ki zo ki fadawa Hajiya . Tace "To kin kawo shawara kema, zan gwada in gani, amma dai na san wajibi ne ta bata min rai Indai wannan yarinyar ce." Nace Ki kwada haka. Juma ta ce wai wani abu ta ke yi wai shi ko tintam irin na wayar nan ana rawa gashinan malamai suna ta wa''azin abin ba kyau ashe yarinyar nan tana yi. Tun a gidan nan. Hajiya bata sani ba. " Nace Tiktok ki ke nufi? Juma ta ce "Yawwa shifa." Na saki baki wai ina kallon Juma. Hajiya dai ta samu kalubale a gidanta. Ya yi da take ganin wasu ba su iya tarbiyya ba sai gashi
A gidanta karkashin tarbiyyar ta Allah ya jarabce ta. Juma tace wai Maman Umarce ta gani a wayar ta, shine ta zo
ta sanar da Hajiya shine mitin din gaggawa ya tashi, aka kira Shamaki yana kasuwa. Nace Allah ya kyau ta.
Ranar a gurina ya ke dan haka Juma ta hada kayanta ta koma gidan, Shamaki ya je ya amshe wayar Azima ya taho da ita. Ni dai naga waya a kan durowar sa ban yi magana ba. Da kanshi yace "Kinsan wannan wayar? Nace bansan ta ba. Yace "Ta Azima ce. " Nace wata ka canza mata ke nan Allah ya sanya alkhari. Yace,, " In canza mata waya saboda itace wa,? Kinsan yarinyar nan wai Tiktok ta ke yi a she?" Nace Haba dai! Kai to kana ina? Yace "Humm na sha mamaki ta jima tana rawa da waka, a Tiktok ba mu sani ba tunda ba mai lokacin kallon shi s ciknmu, na dai sata dai ta goge, sannan na rufe account din, shine kuma na amshe wayar. An tura mata Juma. Nace Aiiah ya basu zaman lafiya amma da ka barta da wayar ta.
Nikam ina kewar Juma aiki zai mana yawa yanzu. Yace "Na san in Hajiya ta lura dole zata samar da mafita. Nace Allah ya sa angane da wuri sai a hanata. Yace "Wannan yarinyar ce zata hanu, nifa in fada miki yarinyar nan tsoro take bani, tunda akayi auren nan kullum cikin nadama nake. " Nace duk kai ka ja wa kanka da baka tabata ba, na tabbatar Hajiya baza tace sai ka aure ta ba in har baka sonta. Ya shafa kai, Baby ke dai ki bar sharrin shedan, kinsan Allah ni bazance miki ga yadda aka yi ba amma ita takawo kanta har dakina. " Nace Sauran fa? " Yace "Su wa? " Nace kana nufin akanta ka fara Newman mata kuma daga ita baka neman wata? Ya dan daburce, sannan yace ni bana neman kowa." Nace Kaima yanzu kana son yin karya wanda kuma kasan ba al'adar gidannan bace.
Ya ce "To Yanzu da ki ka tsara ni me ki ke son in fada miki ne Baby? "Nace Abinda ke birge ka a jikin matan wanda ni bani da shi. Kasan me ke bani mamaki da kai, in na kalle ka sai inga wai ta yaya ka ke gane mace "yar iska kuma har ka tinkare ta gabanka gadi ki yi magana ku yi ciniki sannan ka dauke ta kuje ku kebe, bakasan ta ba, baka san ko tana dauke da wani ciwo ba, yadda tsaftar jikinta ma take duk baka da tabbaci.
Kunya tasa ya kasa kallo na kuma ya kasa magana. Nace to wai Tun tsawo wane lokacin ka fara irin wannan karfin halin? Cikin tsawa ya ce, "Ke! Har sai da na firgita, yace kina da hankali kuwa? Kin dame ni fa, an fada miki mu ne mike zuwa mucewa mata muna son su? Ni nan da kika ganni mace ce tafara lalata ni, ita ce ta kawo min kanta har na san amfanin mace a gurin da namiji. Zuwa yanzu zan iya kirge miki matan da ni na taba cewa ina son su da kaina.
Dan haka ki daina yimin tambayar da bata shafe ki ba. Nace Allah ya baka hakuri, amma zan baka shawara ka bi a sannu, sannan in har da gaske kana daukar Maman Anisa to ka bawa Hajiya hakuri ku maido auren ku. Na fadi haka ne don in latsa inji gaske ne. Sai naga ya zura min ido, "Ina ki ke jin maganganu haka? " Nace Kana mamaki ko? Ka daina mamaki domin cikin mafarki na ina iyaganin duk wani abu da ake boye min. Na daure fuska tamkar gaske. Ya zura min ido kila yana mamaki ko Kuma bai kama ba. Amma dan abar maganar sai yace "Zan fadawa Hajiya gobe a kai ki a yimiki International passport ban sani ba ko Hajiya zata ce a tafi da ke aikin hajji. Na lura baya son maganar nima sai na barta, nace Allah ya sa ina da rabon zuwa amma Hajiya bata ayyana ni a cikin 'yan wannan shekarar ba.
Wani abin mamaki washegari sai Hajiya ke ce min Shamaki ya bada kujeru goma kamar yadda ya saba a rabawa dangi ina son ki duba ki lissafo min mutum takwas ni da Shamaki mu ne cikon goman." Nace Hajiya don Allah ki taimaka domin ni ba kowa na sani a cikn dangin ku ba.
Tace "Mijinki ya bada su, dan haka duk yadda ki ka yi ba mai cewa don me kuma ke ma ai kina da dangi ga iyaye.
Nace Hajiya in muna raye kuma ina gidan nan shekara me zuwa lokacin na kara sanin abubuwa sai in yi wannan aikin amma yanzu ki yafe min ba jayayya zanyi da ke ba. Na fada cikin zanyi jiki da sanyin murya.
Hajiya tace "Shike nan, ashe Maman Mubina ta fiki kokari tunda har ta iya rabawa tsaf a dangi ta, kuma sukaje lafiya suka dawo lafiya. " Nace Ba damuwa wata shekarar sai in yi idan Allah ya sa hakan za a yi.
Haka dai suka shirya tafiya aikin Hajji ciki harda Azima. Ban damu ba domin Hajiya ta ce a tafi da Azima na ayyana cewa domin hankalin dan ta ya kwanta ne cewa tana kusa da su, bazata janyo masa wani ba kamar yadda ya ke fada. Shi da Hajiya kuwa dama duk shekara bata wuce su. Kafin tafiyar su nan ma aka sake wata diramar, an kawo ragunan layya, Hajiya ta ta sani wai in raba raguna, har sai da na kusa kuka ina fada mata bazan iya ba, musamman da na tambaye ta ko wadan da aka baiwa sadakar Azumi za a baiwa tace "A a. Daga baya sai ta ce in zabi na gidan mu. " Nace su kowanne aka ba su, tace lallai saina zaba. Ban ko kalli layin manyan ba na nuna wani dan tsaka tsaki nace to akai musu wannan.
Budar bakinta sai cewa ta yi. "Au ke bazaki zaba ki darje ki zabi narkeke ba irin yadda Maman Meema ta yi ko ki dauki biyu kamar yadda maman Anisa ta yi kuma duk sunci lafiya, iyayen ki
nefa?" Na yi Dan murmushi na kara yadda duk wani motsi mai karfi na gidan Hajiya jarabawa ce. Nace Wannan din ma Allah ya amfana.
Ranar da zasu tafi karfe biyun rana ce zasu wuce, dan bai fita kasuwa ba. Muna kwance a dakinsa ya hanani sakat ina masa mitar me yasa yake yawan damuna. Yace "Baby kullum addu a ta in ganki da ciki ina tsoro kar ki shekara ba ciki Hajiya ta ce kun fadi jarabawa. " Nace dama a cikin gwajin nata harda ciki? Yace "Bansani ba, amma dai ni na zaci haka. Nace duk da bansani ba, amma bana zaton Hajiya zata shiga hurumin Allah domin shine yake da ikon bayarwa kuma bai Bayard ba. Yace "Haka ne, ga shi Azima tana da ciki, Hajiya ta so a barta nace ta yi hakuri mu tasa ta kar ta kama yawonta kafin mudawo. A nan na gane dalilin tafiya da Azima kamar dai yadda na zarge. Wanda da farko har na zarge su da son zuciyar su a farko. Yace zan roko miki Allah ya baki ciki da zarar mundawo." Nace masu albarka zaka rokofa amma, yace "Insha Allahu masu albarka za a samu, na shawo Zam Zam da Laban na ciyo dabinon mai daraja na yo addu'o'i ke kinsan zamu samu 'Dan albarka ko? Nace haka ne. To haka dai suka tafi aka barmin gida amma Juma nan ta dawo saboda aiki harma sai da ta karo mana wasu matan.
Wata ranar lahadi na shigo falon Hajiya dan zuwa kicin muyi aikin abincin rana, sai na sha mamaki ganin Shamaki turus a gaban Hajiya ga Maman Umar zaune. Na gaida Maman Umar sannan nan na kalli Shamaki ransa a bace yake, Nace sannu da zuwa. Hannu kawai ya daga min. Hajiya kuma bata daina maganar da ta ke yi ba wai dan ganina. Na tsinci tana fadin " Na gama magana ya rage naka gidanka ne kuma matar ka ce duk abinda ka ga dama kuma zaka iya yi amma ni a nan na tsaya. " Na nufi kicin cikin faduwar gaba ko a kaina akeyin maganar na fara lissafi yanzu dai watana shidda a gidan Hajiya bare ince ko wa a dina ne ya iso a mugun yanayi, wato banci nasara ba.
Juma wadda na samu suna kuskus da Tabawa ta kalle ni, tace "Yawwa Uwar dakina, dama dai ina ta fatan ki fito domin kiji wani mugun labari, ni dai ina ganin lokacin barin aikina a gidan nan ya zo. na zaro ido cikin fargaba. Me zai sa ki bar inda ki ke samun abinci Baba Juma? Tace wai gidan yarinyar nan za a maida ni wannan marakunyar Azima. Ni kuma da in koma gurinta gara in hakura da aikin kawai gaba daya. " Nace A a Baba Juma, ki fara zuwa ki ga kamun ludayin zaman Idan kinga ba dama to sai ki zo ki fadawa Hajiya . Tace "To kin kawo shawara kema, zan gwada in gani, amma dai na san wajibi ne ta bata min rai Indai wannan yarinyar ce." Nace Ki kwada haka. Juma ta ce wai wani abu ta ke yi wai shi ko tintam irin na wayar nan ana rawa gashinan malamai suna ta wa''azin abin ba kyau ashe yarinyar nan tana yi. Tun a gidan nan. Hajiya bata sani ba. " Nace Tiktok ki ke nufi? Juma ta ce "Yawwa shifa." Na saki baki wai ina kallon Juma. Hajiya dai ta samu kalubale a gidanta. Ya yi da take ganin wasu ba su iya tarbiyya ba sai gashi
A gidanta karkashin tarbiyyar ta Allah ya jarabce ta. Juma tace wai Maman Umarce ta gani a wayar ta, shine ta zo
ta sanar da Hajiya shine mitin din gaggawa ya tashi, aka kira Shamaki yana kasuwa. Nace Allah ya kyau ta.
Ranar a gurina ya ke dan haka Juma ta hada kayanta ta koma gidan, Shamaki ya je ya amshe wayar Azima ya taho da ita. Ni dai naga waya a kan durowar sa ban yi magana ba. Da kanshi yace "Kinsan wannan wayar? Nace bansan ta ba. Yace "Ta Azima ce. " Nace wata ka canza mata ke nan Allah ya sanya alkhari. Yace,, " In canza mata waya saboda itace wa,? Kinsan yarinyar nan wai Tiktok ta ke yi a she?" Nace Haba dai! Kai to kana ina? Yace "Humm na sha mamaki ta jima tana rawa da waka, a Tiktok ba mu sani ba tunda ba mai lokacin kallon shi s ciknmu, na dai sata dai ta goge, sannan na rufe account din, shine kuma na amshe wayar. An tura mata Juma. Nace Aiiah ya basu zaman lafiya amma da ka barta da wayar ta.
Nikam ina kewar Juma aiki zai mana yawa yanzu. Yace "Na san in Hajiya ta lura dole zata samar da mafita. Nace Allah ya sa angane da wuri sai a hanata. Yace "Wannan yarinyar ce zata hanu, nifa in fada miki yarinyar nan tsoro take bani, tunda akayi auren nan kullum cikin nadama nake. " Nace duk kai ka ja wa kanka da baka tabata ba, na tabbatar Hajiya baza tace sai ka aure ta ba in har baka sonta. Ya shafa kai, Baby ke dai ki bar sharrin shedan, kinsan Allah ni bazance miki ga yadda aka yi ba amma ita takawo kanta har dakina. " Nace Sauran fa? " Yace "Su wa? " Nace kana nufin akanta ka fara Newman mata kuma daga ita baka neman wata? Ya dan daburce, sannan yace ni bana neman kowa." Nace Kaima yanzu kana son yin karya wanda kuma kasan ba al'adar gidannan bace.
Ya ce "To Yanzu da ki ka tsara ni me ki ke son in fada miki ne Baby? "Nace Abinda ke birge ka a jikin matan wanda ni bani da shi. Kasan me ke bani mamaki da kai, in na kalle ka sai inga wai ta yaya ka ke gane mace "yar iska kuma har ka tinkare ta gabanka gadi ki yi magana ku yi ciniki sannan ka dauke ta kuje ku kebe, bakasan ta ba, baka san ko tana dauke da wani ciwo ba, yadda tsaftar jikinta ma take duk baka da tabbaci.
Kunya tasa ya kasa kallo na kuma ya kasa magana. Nace to wai Tun tsawo wane lokacin ka fara irin wannan karfin halin? Cikin tsawa ya ce, "Ke! Har sai da na firgita, yace kina da hankali kuwa? Kin dame ni fa, an fada miki mu ne mike zuwa mucewa mata muna son su? Ni nan da kika ganni mace ce tafara lalata ni, ita ce ta kawo min kanta har na san amfanin mace a gurin da namiji. Zuwa yanzu zan iya kirge miki matan da ni na taba cewa ina son su da kaina.
Dan haka ki daina yimin tambayar da bata shafe ki ba. Nace Allah ya baka hakuri, amma zan baka shawara ka bi a sannu, sannan in har da gaske kana daukar Maman Anisa to ka bawa Hajiya hakuri ku maido auren ku. Na fadi haka ne don in latsa inji gaske ne. Sai naga ya zura min ido, "Ina ki ke jin maganganu haka? " Nace Kana mamaki ko? Ka daina mamaki domin cikin mafarki na ina iyaganin duk wani abu da ake boye min. Na daure fuska tamkar gaske. Ya zura min ido kila yana mamaki ko Kuma bai kama ba. Amma dan abar maganar sai yace "Zan fadawa Hajiya gobe a kai ki a yimiki International passport ban sani ba ko Hajiya zata ce a tafi da ke aikin hajji. Na lura baya son maganar nima sai na barta, nace Allah ya sa ina da rabon zuwa amma Hajiya bata ayyana ni a cikin 'yan wannan shekarar ba.
Wani abin mamaki washegari sai Hajiya ke ce min Shamaki ya bada kujeru goma kamar yadda ya saba a rabawa dangi ina son ki duba ki lissafo min mutum takwas ni da Shamaki mu ne cikon goman." Nace Hajiya don Allah ki taimaka domin ni ba kowa na sani a cikn dangin ku ba.
Tace "Mijinki ya bada su, dan haka duk yadda ki ka yi ba mai cewa don me kuma ke ma ai kina da dangi ga iyaye.
Nace Hajiya in muna raye kuma ina gidan nan shekara me zuwa lokacin na kara sanin abubuwa sai in yi wannan aikin amma yanzu ki yafe min ba jayayya zanyi da ke ba. Na fada cikin zanyi jiki da sanyin murya.
Hajiya tace "Shike nan, ashe Maman Mubina ta fiki kokari tunda har ta iya rabawa tsaf a dangi ta, kuma sukaje lafiya suka dawo lafiya. " Nace Ba damuwa wata shekarar sai in yi idan Allah ya sa hakan za a yi.
Haka dai suka shirya tafiya aikin Hajji ciki harda Azima. Ban damu ba domin Hajiya ta ce a tafi da Azima na ayyana cewa domin hankalin dan ta ya kwanta ne cewa tana kusa da su, bazata janyo masa wani ba kamar yadda ya ke fada. Shi da Hajiya kuwa dama duk shekara bata wuce su. Kafin tafiyar su nan ma aka sake wata diramar, an kawo ragunan layya, Hajiya ta ta sani wai in raba raguna, har sai da na kusa kuka ina fada mata bazan iya ba, musamman da na tambaye ta ko wadan da aka baiwa sadakar Azumi za a baiwa tace "A a. Daga baya sai ta ce in zabi na gidan mu. " Nace su kowanne aka ba su, tace lallai saina zaba. Ban ko kalli layin manyan ba na nuna wani dan tsaka tsaki nace to akai musu wannan.
Budar bakinta sai cewa ta yi. "Au ke bazaki zaba ki darje ki zabi narkeke ba irin yadda Maman Meema ta yi ko ki dauki biyu kamar yadda maman Anisa ta yi kuma duk sunci lafiya, iyayen ki
nefa?" Na yi Dan murmushi na kara yadda duk wani motsi mai karfi na gidan Hajiya jarabawa ce. Nace Wannan din ma Allah ya amfana.
Ranar da zasu tafi karfe biyun rana ce zasu wuce, dan bai fita kasuwa ba. Muna kwance a dakinsa ya hanani sakat ina masa mitar me yasa yake yawan damuna. Yace "Baby kullum addu a ta in ganki da ciki ina tsoro kar ki shekara ba ciki Hajiya ta ce kun fadi jarabawa. " Nace dama a cikin gwajin nata harda ciki? Yace "Bansani ba, amma dai ni na zaci haka. Nace duk da bansani ba, amma bana zaton Hajiya zata shiga hurumin Allah domin shine yake da ikon bayarwa kuma bai Bayard ba. Yace "Haka ne, ga shi Azima tana da ciki, Hajiya ta so a barta nace ta yi hakuri mu tasa ta kar ta kama yawonta kafin mudawo. A nan na gane dalilin tafiya da Azima kamar dai yadda na zarge. Wanda da farko har na zarge su da son zuciyar su a farko. Yace zan roko miki Allah ya baki ciki da zarar mundawo." Nace masu albarka zaka rokofa amma, yace "Insha Allahu masu albarka za a samu, na shawo Zam Zam da Laban na ciyo dabinon mai daraja na yo addu'o'i ke kinsan zamu samu 'Dan albarka ko? Nace haka ne. To haka dai suka tafi aka barmin gida amma Juma nan ta dawo saboda aiki harma sai da ta karo mana wasu matan.