Sashe 9
Halittar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bayan sallar magariba Inna na cikin zubowa Halima d'anwaken da tayi dominta sai ga sallamar Baba ya shigo cikin gidan,idansa akan Haliman ya fara sauka ya wani had'e fuska,ko gaisuwar da take mik'o masa bai amsa ba yace tazo ta shige ta koma inda ta fito,tsam ta mik'e tana saka hijabinta a ranta fad'i take."Banda arzik'in mahaifiyarta dake cikin gidan da ko fuskarta baza su k'ara gani ba,har sai sun manta ya kalar fuskar tata take.A kwano mai murfi Inna ta juye mata d'an waken ta k'ulle a leda ta bata."To Inna na gode,idan da sauran canji zan bayar a kawo miki sai ki sayi sauran abinda babu a kayan wainar."
"To na gode Mamana,Allah ya yiwa rayuwa albarka,ki gaishe da mutan gidan."
"Amin Innarmu,zasu ji in sha Allah"
"Yauwa Babansu ga Mubarak can a kwance mashashshara ta kwantar da shi sakamakon dukan da Rahin tayi masa."
Cewar Hajara,bud'ar bakin Inna sai cewa tayi.
"Ke Hajara kiji tsoron Allah,yanzu Mubarak d'in da ke sa'an Rahina,shi za tayiwa dukan da har zai sakashi zazzab'i,bayan ke kanki kinsan k'arfin mace da namiji ba d'aya ba ne,idan har bai saka mata zazzab'i ba ai ba ta saka masa ba."
"To zan mata k'arya,sai an magana ba ke ke daure mata baya ba ki kawowa mutum k'auli da ba'adi."
Baba kuwa inda Rahin ke kwance na sharar bacci ya nufa,tun bayan gama cin abincinta ta b'ingire a gurin,saboda anyi fitina har an gaji...
[9/18, 2:59 PM] Mtn Number: BEBE'ARTH
2023
Wattpad@Rashuna
Mama Jiddah
Heenah
Silar soyayya
Masoya
Rabee'ah
Babbar Cuta
Muguwar surika
K'addarar Rayuwarmu
Cikin Duniyarmu500
Katanga500
Cin Amana500
Wadjda500
Halittar ZUciya500
Compleet guda hud'unnan ga masu buk'ata zan iya baku a 1500 da kuma samun damar karanta HALITTAR ZUCIYA KTAUTA.
Ban yadda a juya mini littafaina ko wata siga ba,duk wanda yaci da gumina idan ban gani ba Allah yana gani.
HALITTAR
ZUCIYA
(3)
Sa k'amshi sa dad'i,hana gafi k'arni no,spices da curry kenan gangariya gurin k'awata girki.
09037093702
Ina macen da girkinta ke k'arni idan tayi amfani da nama,ina macen da ke son amfani karafish tana tsoron k'arni,ina kuma macen da rashin albasa ke hanata soya k'wai,ina macen da take son girkinta ya k'ara dad'i da d'and'ano da kuma k'amshi?maza hanzarta ki nemi spices d'in Rashuna domin kuwa nata ba irin nasu ba ne.09037093702
Mata da dama idan suka soya kifi zubar da man suke saboda gudun k'arni,abinda kuma ba ku sani ba kun zubar da sinadarin ki kelaya abinki Hajiyata,ki kawo curry da spices d'in Rashuna ki zuba,Hmmm na rantse miki da Allah mityarki ba za tayi k'arni ba.
K'afa yasa yakai mata wani irin dukan da ya sanyata farkawar ba shiri had'e da tsanyara wani uban ihu,dukanta ya shiga yi ko ta ina tana ihu tana kwararato shikwa yana fad'in.
"Ai yadda kika saka shi yau zai kwana da zazzab'i wallahi yau kema sai kin kwana da shi,shegiya me siffar aljanu,in baki wasa ba wata rana sai na nakasta ki wallahi."
Ko kallon inda yake dukanta Inna ba tayi ba tai shigewarta d'aki,duk da zuciyarta dake mata suya bama akan dukan nata da yake ba,a'a irin furucin da yake jifanta da shi,duk wanda ya zauna da su na wuni d'aya sai ya fuskanci irin tsanar da yayiwa Rahina wacce ba ya iya b'oyeta ko a gaban waye,ita kuma zuciyarsa na matuk'ar sonsa da k'aunarsa,abu d'aya take jiye masa shine ranar da ZUCIYAR RAHINAN zata fara tsanarsa wacce kuma ta tabbata wannan tsanar mai iya cireta daga zuciyarta sai Allah kuma.
Sai da ya tabbatar ta daku kana ya k'yaleta,band'aki ya shiga ya fito ya d'aura alwala ya fice saboda kiraye kirayen sallar isha da aka fara.Tana zaune tana rusa kuka Sale ya shigo,irin kukan da take ya fara kwaikwaya,aikwa da ta d'auki farantin silbar dake kusa da ita ta lailaya shi ta jefa masa sai kuwa akan goshinsa,wata gigitacciyar k'ara ya saki da ta sanya Hajara saurin fitowa,nufo inda take a zaune yayi yana."Wallahi bazan yadda ba sai na rama." Mik'ewa tayi tana huci tana jiran yazo ayi duk wacce za'ayi,janyeta Inna tayi had'e da fad'in. "Shige kiyi alwala kibar nan gun."
Hajara ce a k'ufule tace."Wannan wani irin zalinci ne?Kibar yaro mana ya rama abinda ta masa zaki wani janyeta tsabar rashin gaskiya." Ci kanki Inna ba tace da ita sai tsaiwarta ta gyara tana jiran Rahin d'in ta fito daga band'akin,tana fitowa kuwa Hajara ta hankad'a Sale had'e da fad'in jeka ka rama dukanka,in kuwa ba haka ba wallahi Babanku ya dawo sai na gaya masa tunda ita aljana ce duka ba ya shiga jikinta,ko kuma nace jaka"
Inda Rahin d'in ke tsugune na alwala Sale ya nufa Inna ta dakatar da shi da fad'in. "Kada ka sake hannunka ya sauka a jikinta,in ba haka ba wallahi sai ranka yayi mugun b'aci,uban waye yace ka tsokaneta?da kaja girmanka zata bi ta taka shine?"
Jaa da baya yayi saboda yana shakkar Innar Rahin d'in,sam bata musu wasa shiyasa suka fi tsoranta ma akan Innarsu,k'wafa kawai yayi,had'e da cewa Rahin d'in. "Shegiya mummuna,duk fad'in garin nan kowa ya shaida Baba baya sonki,kuma wallahi zan kamaki a waje ne inda babu Innar taki sai naga me tare miki."
"Ka nad'a mata na jaki wallahi ni nan na tsaya maka,kuma mahaifinka ma ya tsaya maka,yarinya sai kace iblishiya kuma ana dad'a d'aure mata baya,kai nidai Allah na gode maka da ba ka bani 'ya mace ba,ashe ta bakin baban nasu 'ya mace tarin wahala ce."
"Shige d'aki,kiyi sallar magariba sannan ki isha." Inna tacewa Rahin,sai da taga shigewarta d'akin kana ta juyo kan Hajara dan mayar da martani. "A gurin kune 'ya mace tarin wahala,anman a gurina ni'ima ce kuma sanyin idaniya,da ace zan k'ara haihuwa dubu,kuma Allah du ya bani 'ya'ya mata da zanyi matuk'ar farin ciki,abinda Rahin kuwa keyi k'utuciya ce kuma kowa da kalar tasa k'uruciyar,wata rana baza kice tayi haka ba,kuma ina ji a jikina wata rana sai kin shiga inuwarta 'ya'ya mazan da kike ganin mafaka ne a gareki sai tawa macen ta zane miiki mafaka kafin su,da kina da hankali da tunani ko akan Halima zaki fahimci falala da ni'imar da yayi mini da ya azurta ni da samunta."
Tana kawowa nan tayi shigewarta d'aki ba ta tsaya saurarar kunfar bakin da Inna Hajara ke yi ba ta dai jiyota tana Allah ya sawak'e ta shiga inuwar Rahin d'in ba taga abinda zata tsinana mata ba ita da Allah ya azurtata da samun mazaje har guda biyar ba taga wani abu da wannan iblishiyar za tayi mata ba. A k'udun dine ta samu Rahin d'in tana ta rawar d'ari,alamun zazzab'i ne yake shigarta,paracetamol ta d'auko ta bata tasha,kana tace ta shige cikin gidan sauro ta kwanta ita kuma ta tayar da sallar isha'i. Rantsuwar Baba taci Rahin,dan kwa kwana tayi da azababban zazzab'i,gashi in tana zazzab'i sai tai ta firgita,washe gari da safe kuwa ko makaranta ba taje ba su Fad'ime da suka,biyo mata suka tarar bata da lafiya sai kwa bulki cewa tayi. "Alqur'anin Allah yau nima kwa baza ni ba,komawa zanyi nacewa Innata ba'a yi." cikin marai raita Fad'ime tace.
"Kekwa dan Allah Bulki kizo muje,yau ni kad'ai kuke so ku bari,makarantar baza tamini dad'i ba,gashi in naje na yiwa Innata k'arya baza ta yadda ba." "Ai yau ko me zaki Fad'ime ba zanje makarantar nan ba,kin manta jiya na tsokano kin manta jiya na tsokano Abun gidan Bawa me jakai,tace sai mun had'u a makaranta zata ci ubana,kuma me tare mini ba lafiya in ba so kike tayi k'uli k'ulin Kubra da ni ba." Ba yadda Fad'ime ta iya haka ta bar Bulki ta juya gida ita kuma ta nufi makarantar bokon nasu da ke da d'an tazara sosai da su,ajinsu uku a yanzu,kuma ajinsu d'aya duka su ukun,k'awaye ne tun daga yarinta,Bulki tsinanniyar tsokana ce da ita wacce ta dame ta Rahin ta shanye ga tsoro fal ciki,idan tayo tsokanar Rahin ke uwa ke makarb'iya,ita Rahin fitina tafi yawa a cikinta,Fad'ime ce me sanyin hali kawai a cikinsu anman itama idan ana fad'a da d'aya a cikinsu haka zata zage ayi da ita duk da ba ta kasance me son fad'a ba.
"To na gode Mamana,Allah ya yiwa rayuwa albarka,ki gaishe da mutan gidan."
"Amin Innarmu,zasu ji in sha Allah"
"Yauwa Babansu ga Mubarak can a kwance mashashshara ta kwantar da shi sakamakon dukan da Rahin tayi masa."
Cewar Hajara,bud'ar bakin Inna sai cewa tayi.
"Ke Hajara kiji tsoron Allah,yanzu Mubarak d'in da ke sa'an Rahina,shi za tayiwa dukan da har zai sakashi zazzab'i,bayan ke kanki kinsan k'arfin mace da namiji ba d'aya ba ne,idan har bai saka mata zazzab'i ba ai ba ta saka masa ba."
"To zan mata k'arya,sai an magana ba ke ke daure mata baya ba ki kawowa mutum k'auli da ba'adi."
Baba kuwa inda Rahin ke kwance na sharar bacci ya nufa,tun bayan gama cin abincinta ta b'ingire a gurin,saboda anyi fitina har an gaji...
[9/18, 2:59 PM] Mtn Number: BEBE'ARTH
2023
Wattpad@Rashuna
Mama Jiddah
Heenah
Silar soyayya
Masoya
Rabee'ah
Babbar Cuta
Muguwar surika
K'addarar Rayuwarmu
Cikin Duniyarmu500
Katanga500
Cin Amana500
Wadjda500
Halittar ZUciya500
Compleet guda hud'unnan ga masu buk'ata zan iya baku a 1500 da kuma samun damar karanta HALITTAR ZUCIYA KTAUTA.
Ban yadda a juya mini littafaina ko wata siga ba,duk wanda yaci da gumina idan ban gani ba Allah yana gani.
HALITTAR
ZUCIYA
(3)
Sa k'amshi sa dad'i,hana gafi k'arni no,spices da curry kenan gangariya gurin k'awata girki.
09037093702
Ina macen da girkinta ke k'arni idan tayi amfani da nama,ina macen da ke son amfani karafish tana tsoron k'arni,ina kuma macen da rashin albasa ke hanata soya k'wai,ina macen da take son girkinta ya k'ara dad'i da d'and'ano da kuma k'amshi?maza hanzarta ki nemi spices d'in Rashuna domin kuwa nata ba irin nasu ba ne.09037093702
Mata da dama idan suka soya kifi zubar da man suke saboda gudun k'arni,abinda kuma ba ku sani ba kun zubar da sinadarin ki kelaya abinki Hajiyata,ki kawo curry da spices d'in Rashuna ki zuba,Hmmm na rantse miki da Allah mityarki ba za tayi k'arni ba.
K'afa yasa yakai mata wani irin dukan da ya sanyata farkawar ba shiri had'e da tsanyara wani uban ihu,dukanta ya shiga yi ko ta ina tana ihu tana kwararato shikwa yana fad'in.
"Ai yadda kika saka shi yau zai kwana da zazzab'i wallahi yau kema sai kin kwana da shi,shegiya me siffar aljanu,in baki wasa ba wata rana sai na nakasta ki wallahi."
Ko kallon inda yake dukanta Inna ba tayi ba tai shigewarta d'aki,duk da zuciyarta dake mata suya bama akan dukan nata da yake ba,a'a irin furucin da yake jifanta da shi,duk wanda ya zauna da su na wuni d'aya sai ya fuskanci irin tsanar da yayiwa Rahina wacce ba ya iya b'oyeta ko a gaban waye,ita kuma zuciyarsa na matuk'ar sonsa da k'aunarsa,abu d'aya take jiye masa shine ranar da ZUCIYAR RAHINAN zata fara tsanarsa wacce kuma ta tabbata wannan tsanar mai iya cireta daga zuciyarta sai Allah kuma.
Sai da ya tabbatar ta daku kana ya k'yaleta,band'aki ya shiga ya fito ya d'aura alwala ya fice saboda kiraye kirayen sallar isha da aka fara.Tana zaune tana rusa kuka Sale ya shigo,irin kukan da take ya fara kwaikwaya,aikwa da ta d'auki farantin silbar dake kusa da ita ta lailaya shi ta jefa masa sai kuwa akan goshinsa,wata gigitacciyar k'ara ya saki da ta sanya Hajara saurin fitowa,nufo inda take a zaune yayi yana."Wallahi bazan yadda ba sai na rama." Mik'ewa tayi tana huci tana jiran yazo ayi duk wacce za'ayi,janyeta Inna tayi had'e da fad'in. "Shige kiyi alwala kibar nan gun."
Hajara ce a k'ufule tace."Wannan wani irin zalinci ne?Kibar yaro mana ya rama abinda ta masa zaki wani janyeta tsabar rashin gaskiya." Ci kanki Inna ba tace da ita sai tsaiwarta ta gyara tana jiran Rahin d'in ta fito daga band'akin,tana fitowa kuwa Hajara ta hankad'a Sale had'e da fad'in jeka ka rama dukanka,in kuwa ba haka ba wallahi Babanku ya dawo sai na gaya masa tunda ita aljana ce duka ba ya shiga jikinta,ko kuma nace jaka"
Inda Rahin d'in ke tsugune na alwala Sale ya nufa Inna ta dakatar da shi da fad'in. "Kada ka sake hannunka ya sauka a jikinta,in ba haka ba wallahi sai ranka yayi mugun b'aci,uban waye yace ka tsokaneta?da kaja girmanka zata bi ta taka shine?"
Jaa da baya yayi saboda yana shakkar Innar Rahin d'in,sam bata musu wasa shiyasa suka fi tsoranta ma akan Innarsu,k'wafa kawai yayi,had'e da cewa Rahin d'in. "Shegiya mummuna,duk fad'in garin nan kowa ya shaida Baba baya sonki,kuma wallahi zan kamaki a waje ne inda babu Innar taki sai naga me tare miki."
"Ka nad'a mata na jaki wallahi ni nan na tsaya maka,kuma mahaifinka ma ya tsaya maka,yarinya sai kace iblishiya kuma ana dad'a d'aure mata baya,kai nidai Allah na gode maka da ba ka bani 'ya mace ba,ashe ta bakin baban nasu 'ya mace tarin wahala ce."
"Shige d'aki,kiyi sallar magariba sannan ki isha." Inna tacewa Rahin,sai da taga shigewarta d'akin kana ta juyo kan Hajara dan mayar da martani. "A gurin kune 'ya mace tarin wahala,anman a gurina ni'ima ce kuma sanyin idaniya,da ace zan k'ara haihuwa dubu,kuma Allah du ya bani 'ya'ya mata da zanyi matuk'ar farin ciki,abinda Rahin kuwa keyi k'utuciya ce kuma kowa da kalar tasa k'uruciyar,wata rana baza kice tayi haka ba,kuma ina ji a jikina wata rana sai kin shiga inuwarta 'ya'ya mazan da kike ganin mafaka ne a gareki sai tawa macen ta zane miiki mafaka kafin su,da kina da hankali da tunani ko akan Halima zaki fahimci falala da ni'imar da yayi mini da ya azurta ni da samunta."
Tana kawowa nan tayi shigewarta d'aki ba ta tsaya saurarar kunfar bakin da Inna Hajara ke yi ba ta dai jiyota tana Allah ya sawak'e ta shiga inuwar Rahin d'in ba taga abinda zata tsinana mata ba ita da Allah ya azurtata da samun mazaje har guda biyar ba taga wani abu da wannan iblishiyar za tayi mata ba. A k'udun dine ta samu Rahin d'in tana ta rawar d'ari,alamun zazzab'i ne yake shigarta,paracetamol ta d'auko ta bata tasha,kana tace ta shige cikin gidan sauro ta kwanta ita kuma ta tayar da sallar isha'i. Rantsuwar Baba taci Rahin,dan kwa kwana tayi da azababban zazzab'i,gashi in tana zazzab'i sai tai ta firgita,washe gari da safe kuwa ko makaranta ba taje ba su Fad'ime da suka,biyo mata suka tarar bata da lafiya sai kwa bulki cewa tayi. "Alqur'anin Allah yau nima kwa baza ni ba,komawa zanyi nacewa Innata ba'a yi." cikin marai raita Fad'ime tace.
"Kekwa dan Allah Bulki kizo muje,yau ni kad'ai kuke so ku bari,makarantar baza tamini dad'i ba,gashi in naje na yiwa Innata k'arya baza ta yadda ba." "Ai yau ko me zaki Fad'ime ba zanje makarantar nan ba,kin manta jiya na tsokano kin manta jiya na tsokano Abun gidan Bawa me jakai,tace sai mun had'u a makaranta zata ci ubana,kuma me tare mini ba lafiya in ba so kike tayi k'uli k'ulin Kubra da ni ba." Ba yadda Fad'ime ta iya haka ta bar Bulki ta juya gida ita kuma ta nufi makarantar bokon nasu da ke da d'an tazara sosai da su,ajinsu uku a yanzu,kuma ajinsu d'aya duka su ukun,k'awaye ne tun daga yarinta,Bulki tsinanniyar tsokana ce da ita wacce ta dame ta Rahin ta shanye ga tsoro fal ciki,idan tayo tsokanar Rahin ke uwa ke makarb'iya,ita Rahin fitina tafi yawa a cikinta,Fad'ime ce me sanyin hali kawai a cikinsu anman itama idan ana fad'a da d'aya a cikinsu haka zata zage ayi da ita duk da ba ta kasance me son fad'a ba.