Sashe 7
Halittar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
hayaniya da iho ihon mutane yasa ta farkawa a firgice tana kiran Baba,jin babu alamun Baban kusa da ita sai ihun mutane da take ji yasa ta fashewa da wani irin kuka mai ban tausayi,kukanta ne yasa Hadi da ya lab'e daga bayan katangar da take lek'owa idonsa ya sauka a kanta,wani irin sanyi yaji a ransa,yana ganin kamar wahalarsa ce tazo k'arshe idan ya samu damar k'wamushe wannan yarinyar,da azama ya fito ya ja hannunta ya koma inda ya lab'e,ganin yadda take a firgice tana kiran Baba yasa shi janyo wani hankici daga aljihunsa ya shek'a mata,ba tayi baccin da yake so ba anman jikinta ya saki gaba d'aya ta zube a jikinsa,bayan komai ya lafa ya faki idanuwan mutane ya sakata a bayan motarsa,Allah Allah yake gari ya waye ya fice daga cikin tashar dan ko lodi bazai yi ba tunda ga babban lodi ya samu.
K'arfe bakwai ya fice daga cikin tashar ya fara sharara gudu akan titi Allah Allah yake yaga ya d'auki hanyar barin gari dan yana hango yawan kud'in da zai samu idan ya kaiwa oga wannan yarinyar sai dai kuma kana naka ne Allah yana na shi,nashi kuma shine gaskiya domin kuwa wani k'aton ice da bai kula da shi ba motarshi ta daka a take sitiyarin motar ya kubfce mishi motar ta kife akan titi,mai ya fara zuba a take ta fara hayak'i alamun tana gab da kamawa da huta,mutum biyu Allah ya jeho zasu huce,su suka taimaka suka ciro Rahina daga cikin motar ba su kai ga fito da Hadi ba motar ta kama da huta.
Ko k'warzane babu jikin Rahina,anman a mugun tsorace take,rashin gani babbar illa ce a rayuwa tana jin komai anman bata ganin abinda ke faruwa,kuka take sosai tana kiran sunan Innarta ba ta san ina Baba ya kawota ya ajiye ba ko kuma da had'in bakinsa wannan mutumin yake k'ok'arin sayar da ita,dan taji wayar da yakeyi abinda ya shek'a mata baiyi nasarar sakata bacci ba jininta yana da mugun k'arfi,hankulan mutane na can kan motar da ta kama da huta da kuma k'ok'arin kiran police ta d'auki wata hanya da ban tana tik'ar gudu a ganinta Allah ne ya kub'utar da ita daga hannun azzalumin can dake k'ok'arin sayar da ita,bata da tabbas d'in wanda suka cirota daga motar suma ba azzaluman ba ne,gudu take sosai akan titi wanda ita ba ta san titin bane tunda ba gani take ba,aikam wata mota da ta yanko a guje tai sama da ita ta watsar babu alamun rai a tattare da ita,kifa kai mamallakiyar motar tayi jikin siyiyarin cike da takaici da bak'in cikin wannan mahaukaciyar yarinyar,ba komai take tsoro ba sai azumin da zata janyo mata ba taji ba ba ta gani ba,na Ramadan ma da yaya take sauke shi bare kuma wannan da ya ninka shi,tsaki ta ja kafin ta fito daga motar a ranta tana addu'ar Allah yasa ba ta mutu ba,ko k'warzane babu a jikinta anman da alamun wuya ta saka numfashinta d'aukewa.
D'aukarta tayi ta sanya cikin motarta ta juya zuwa asibitin da ta fito,tana jan tsaki akai akai da addu'ar Allah sa ba ta mutu ba,tsabar zafin da kanta ya d'auka baccin da ke cikin idanuwanta ji tayi ya wartsake gaba d'aya. Sai da aka tabbatar mata yarinyar na da rai ta samu karaya a k'afa da hannu kana ta samu nutsuwar tafiya gida bayan ta bar sallahun a yiwa yarinyar duk abinda ya dace idan taje gida zata turo wanda zai kula da ita.
Sai takwas da rabi ta baro asibitin zuwa gida,tana parking d'in motarta ta hango Fadwa ta nufi sashen FASIHUL LISAN a ranta tace "Wahalalliya." Tana shiga falon,Fadwan ta shigo da tray a hannunta fuskarta d'auke da damuwa,dining ta nufa kai tsaye ta ajiye tray d'in hannunta tana fad'in.
"Ammi sai yanzu?"
"Hmm wata yarinya ta jamin musifa wallahi,ta hau kan tsakiyar titi tana gudu ban aune ba na kad'eta,inda Allah ya tak'aita ba ta mutu ba,kicema Talatu ta shirya Bala ya kaita asibitin ta kula da yarinyar kafin a samu kanta."
"Ayya Allah ya kiyaye gaba,nima zan bisu na duba yarinyar."
Kamar yadda ta tsammata Ammin baza ta tanka ba,ba kwa ta tanka d'in ba sai shigewarta part d'inta tayi dan wanka take buk'ata kafin ta kwanta bacci,kwana tayi ba ta rintsa ba saboda yawaitar marasa lafiya duk rashin kirkinta tsakaninta da Allah take aikinta.
Murmushi Fadwa ta saki,ta d'auko kwaandon saka abinci ta jere break fast d'in da ta hana idonta bacci ta tashi ta tsantsarawa Yaa Fasee duk don ta burgeshi ta kuma karkato da hankalinsa kanta a bisa shawarar aminiyarta Siyama,sai dai kuma da yake Namijin duniya ne haka ya tsallake break d'in ko tab'awa bai yi ba ya fice ya bar mata,yanzu kuwa dole ya ci tunda ta samu hanyar zuwa asibitin sai ta bishi da shi har office d'insa wahalarta baza ta zama a banza ba in sha Allah.
Sai da ta gama jera abincin kana taje ta sanarwa da Talatu sak'on Ammi,ta d'auki d'an abinda zata d'auka suka fito Bala ya jasu zuwa asibitin...
Zan iya cewa a nan free page ya k'are masu buk'atar cigabansa zasu iya samuna kai tsaye a wannan layin 09037093702 na gode.
BEBEE'ARTH RASHUNA[9/18, 2:59 PM] Mtn Number: BEBE'ARTH
2023
Wattpad@Rashuna
Mama Jiddah
Heenah
Silar soyayya
Masoya
Rabee'ah
Babbar Cuta
Muguwar surika
K'addarar Rayuwarmu
Cikin Duniyarmu500
Katanga500
Cin Amana500
Wadjda500
Halittar ZUciya500
Compleet guda hud'unnan ga masu buk'ata zan iya baku a 1500 da kuma samun damar karanta HALITTAR ZUCIYA KYAUTA.
HALITTAR
ZUCIYA
(1)
Shimfid'a
Jajare garin jajaye in kaga bak'i to bak'o ne ya ka zo,wannan inkiya ce ta garin Jajere.Jajere gari ne na fulanin damaturu,Malam Madu yana d'aya daga cikin mutanen garin,haifaffan garinne shi tun iyaye da kakanni,mahaifansa ne suka wanke Mariya suka bashi,Mariya kamar 'ya take a gurinsu saboda su sukayi rik'onta tun tana yarinya,sun tsinceta ne a wani kango da ake gini suka rik'eta ba tare da k'yamata ba,suka kuma d'auketa suka bawa d'ansu duk saboda soyayya,anman Madu sam ba ya k'aunar Mariya,ya karb'i auranta ne saboda biyayya ga iyayansa,suna zaune,lafiya ba mai jin kansu duk da Mariya tana matuk'ar hak'uri da wasu halayen na Madu dan baza ta iya fitowa ta fad'a ba ne ana haka ta samu ciki inda ta haifi 'ya mace,zo kuga ruwan tijara gurin Madu shi ba ya son mace,mace ai k'arin wahala ce babu abinda za ta tsinana maka yak'i yin komai na haihuwa sai iyayansa ne suka yi mata,sunama babansa ne ya rad'a mata Halima,(Sunan mahaifiyar Madun kenan)a haka rayuwa ta gangara Mariya na matuk'ar hak'uri da halayen Madu duk saboda darajar iyayansa wanda su take kallo a matsayin nata iyayan da Allah ya bata sama ta ka,gashi yanzu k'asa ta rufewa Inna Halima idanu wacce ta kasance tana tausayinta da taimaka mata da wasu abubuwan,a haka rayuwa take ta juyawa Madu ya sake auran Hajara, haihuwar fari ta haifo masa namiji zo kuga murna gurin Madu sai a wannan haihuwar Mariya ta san mijin nata ba k'aramin arzik'i ne da shi ba dan sosai ya saki bakin aljihu yana wa Hajara da d'anta hidima har zuwa ranar suna inda yaro yaci sunan mahaifin Madu Idris.
Tun daga haihuwar Halima,Mariya ba ta sake haihuwa ba har sai da Hajara tayi haihuwa uku a jere duk maza wanda suke ganin so da k'auna da gata gurin Madu,Halima kuwa ko kallo ba ta isheshi ba a cewarsa bazai wahalta mata ba,dan su mata sai dai ka wahalta musu a banza ba tare da kaci moriyarsu ba,inda Allah ya taimaki Halima sai ya yota mai sanyin hali,ko kad'an ba ta dosar mahaifin nasu saboda ta san halinsa,abu kad'an za tayi ya mangareta har yanzu kuwa da take da shekaru takwas a duniya.
Hajara da Mariya a lokaci guda suka haihu inda Mariya macen dai ta kuma haifa,inda Hajara ta dinga yadar mata da maganganu shi kwa Madu ba ta isheshi kallo ba daga ita har jinjirar da ta haifa,inda Allah ya taimaketa ta tanadi komai na haihuwarta saboda tana sana'arta ta kayan miya bushashe da kuma wainar gero da k'uli da safe,tunda mai taimakon nata babu ita yanzu a doron k'asa,kamar haihuwar Halima wannan ma mahaifin Madu shi ya nad'awa jaririya suna RAHEENA.
Akwai bam-bamcin halaye k'ara k'ara tsakanin Halima da Raheena,Halima mai shiru shiru ce da sanyin hali,duk inda aka nuna ba'a sonta ba ta dosar gurin,yayin da Raheena ta kasance mai kwaraf niya ga tsokanar tsiya a cikinta kamar me,inda kuma Allah ya d'ora mata k'aunar mahaifinsu Madu duk da kasancewar shi yafi tsanarta ma akan Halima,dan dukan da take sha gurinsa bai daki Halima haka ba ga kyararta da yake anman ba shi zai hana ta koma gurinsa ba,zasu had'u ita da Mubarak tsarar haihuwarta d'an wajan Hajara suyi k'iriniya anman idan Madu ya tashi ko dunguri ba zaiwa Mubarak ba anman in ya kama Raheena da duka kamar Allah ya aikoshi.
Halayen Raheena suna mugun ciwa Mariya tuwo a k'warya anman babu yadda za tayi sai addu'a ta san k'uruciya ce ko wani yaro da kalar k'uruciyarsa nan gaba idan ta san ciwon kanta ba za tayi ba,gashi yanzu ta aurar da Halima tana cikin shekarunta na sha hud'u kenan Raheena kuma shida,komai na auran Halima Baffa Idris mahaifin Malam Madu shi yayi,har yau yana nisar da d'an nasa anma ya kasa ganewa shiyasa ya d'au ido ya zuba masa ya tabbata akwai ranar da zai gane kad'an daga cikin ni'imar da Allah ya yi maka idan ya azurtaka da samun 'ya mace.
Wannan kenan
……
K'arfe bakwai ya fice daga cikin tashar ya fara sharara gudu akan titi Allah Allah yake yaga ya d'auki hanyar barin gari dan yana hango yawan kud'in da zai samu idan ya kaiwa oga wannan yarinyar sai dai kuma kana naka ne Allah yana na shi,nashi kuma shine gaskiya domin kuwa wani k'aton ice da bai kula da shi ba motarshi ta daka a take sitiyarin motar ya kubfce mishi motar ta kife akan titi,mai ya fara zuba a take ta fara hayak'i alamun tana gab da kamawa da huta,mutum biyu Allah ya jeho zasu huce,su suka taimaka suka ciro Rahina daga cikin motar ba su kai ga fito da Hadi ba motar ta kama da huta.
Ko k'warzane babu jikin Rahina,anman a mugun tsorace take,rashin gani babbar illa ce a rayuwa tana jin komai anman bata ganin abinda ke faruwa,kuka take sosai tana kiran sunan Innarta ba ta san ina Baba ya kawota ya ajiye ba ko kuma da had'in bakinsa wannan mutumin yake k'ok'arin sayar da ita,dan taji wayar da yakeyi abinda ya shek'a mata baiyi nasarar sakata bacci ba jininta yana da mugun k'arfi,hankulan mutane na can kan motar da ta kama da huta da kuma k'ok'arin kiran police ta d'auki wata hanya da ban tana tik'ar gudu a ganinta Allah ne ya kub'utar da ita daga hannun azzalumin can dake k'ok'arin sayar da ita,bata da tabbas d'in wanda suka cirota daga motar suma ba azzaluman ba ne,gudu take sosai akan titi wanda ita ba ta san titin bane tunda ba gani take ba,aikam wata mota da ta yanko a guje tai sama da ita ta watsar babu alamun rai a tattare da ita,kifa kai mamallakiyar motar tayi jikin siyiyarin cike da takaici da bak'in cikin wannan mahaukaciyar yarinyar,ba komai take tsoro ba sai azumin da zata janyo mata ba taji ba ba ta gani ba,na Ramadan ma da yaya take sauke shi bare kuma wannan da ya ninka shi,tsaki ta ja kafin ta fito daga motar a ranta tana addu'ar Allah yasa ba ta mutu ba,ko k'warzane babu a jikinta anman da alamun wuya ta saka numfashinta d'aukewa.
D'aukarta tayi ta sanya cikin motarta ta juya zuwa asibitin da ta fito,tana jan tsaki akai akai da addu'ar Allah sa ba ta mutu ba,tsabar zafin da kanta ya d'auka baccin da ke cikin idanuwanta ji tayi ya wartsake gaba d'aya. Sai da aka tabbatar mata yarinyar na da rai ta samu karaya a k'afa da hannu kana ta samu nutsuwar tafiya gida bayan ta bar sallahun a yiwa yarinyar duk abinda ya dace idan taje gida zata turo wanda zai kula da ita.
Sai takwas da rabi ta baro asibitin zuwa gida,tana parking d'in motarta ta hango Fadwa ta nufi sashen FASIHUL LISAN a ranta tace "Wahalalliya." Tana shiga falon,Fadwan ta shigo da tray a hannunta fuskarta d'auke da damuwa,dining ta nufa kai tsaye ta ajiye tray d'in hannunta tana fad'in.
"Ammi sai yanzu?"
"Hmm wata yarinya ta jamin musifa wallahi,ta hau kan tsakiyar titi tana gudu ban aune ba na kad'eta,inda Allah ya tak'aita ba ta mutu ba,kicema Talatu ta shirya Bala ya kaita asibitin ta kula da yarinyar kafin a samu kanta."
"Ayya Allah ya kiyaye gaba,nima zan bisu na duba yarinyar."
Kamar yadda ta tsammata Ammin baza ta tanka ba,ba kwa ta tanka d'in ba sai shigewarta part d'inta tayi dan wanka take buk'ata kafin ta kwanta bacci,kwana tayi ba ta rintsa ba saboda yawaitar marasa lafiya duk rashin kirkinta tsakaninta da Allah take aikinta.
Murmushi Fadwa ta saki,ta d'auko kwaandon saka abinci ta jere break fast d'in da ta hana idonta bacci ta tashi ta tsantsarawa Yaa Fasee duk don ta burgeshi ta kuma karkato da hankalinsa kanta a bisa shawarar aminiyarta Siyama,sai dai kuma da yake Namijin duniya ne haka ya tsallake break d'in ko tab'awa bai yi ba ya fice ya bar mata,yanzu kuwa dole ya ci tunda ta samu hanyar zuwa asibitin sai ta bishi da shi har office d'insa wahalarta baza ta zama a banza ba in sha Allah.
Sai da ta gama jera abincin kana taje ta sanarwa da Talatu sak'on Ammi,ta d'auki d'an abinda zata d'auka suka fito Bala ya jasu zuwa asibitin...
Zan iya cewa a nan free page ya k'are masu buk'atar cigabansa zasu iya samuna kai tsaye a wannan layin 09037093702 na gode.
BEBEE'ARTH RASHUNA[9/18, 2:59 PM] Mtn Number: BEBE'ARTH
2023
Wattpad@Rashuna
Mama Jiddah
Heenah
Silar soyayya
Masoya
Rabee'ah
Babbar Cuta
Muguwar surika
K'addarar Rayuwarmu
Cikin Duniyarmu500
Katanga500
Cin Amana500
Wadjda500
Halittar ZUciya500
Compleet guda hud'unnan ga masu buk'ata zan iya baku a 1500 da kuma samun damar karanta HALITTAR ZUCIYA KYAUTA.
HALITTAR
ZUCIYA
(1)
Shimfid'a
Jajare garin jajaye in kaga bak'i to bak'o ne ya ka zo,wannan inkiya ce ta garin Jajere.Jajere gari ne na fulanin damaturu,Malam Madu yana d'aya daga cikin mutanen garin,haifaffan garinne shi tun iyaye da kakanni,mahaifansa ne suka wanke Mariya suka bashi,Mariya kamar 'ya take a gurinsu saboda su sukayi rik'onta tun tana yarinya,sun tsinceta ne a wani kango da ake gini suka rik'eta ba tare da k'yamata ba,suka kuma d'auketa suka bawa d'ansu duk saboda soyayya,anman Madu sam ba ya k'aunar Mariya,ya karb'i auranta ne saboda biyayya ga iyayansa,suna zaune,lafiya ba mai jin kansu duk da Mariya tana matuk'ar hak'uri da wasu halayen na Madu dan baza ta iya fitowa ta fad'a ba ne ana haka ta samu ciki inda ta haifi 'ya mace,zo kuga ruwan tijara gurin Madu shi ba ya son mace,mace ai k'arin wahala ce babu abinda za ta tsinana maka yak'i yin komai na haihuwa sai iyayansa ne suka yi mata,sunama babansa ne ya rad'a mata Halima,(Sunan mahaifiyar Madun kenan)a haka rayuwa ta gangara Mariya na matuk'ar hak'uri da halayen Madu duk saboda darajar iyayansa wanda su take kallo a matsayin nata iyayan da Allah ya bata sama ta ka,gashi yanzu k'asa ta rufewa Inna Halima idanu wacce ta kasance tana tausayinta da taimaka mata da wasu abubuwan,a haka rayuwa take ta juyawa Madu ya sake auran Hajara, haihuwar fari ta haifo masa namiji zo kuga murna gurin Madu sai a wannan haihuwar Mariya ta san mijin nata ba k'aramin arzik'i ne da shi ba dan sosai ya saki bakin aljihu yana wa Hajara da d'anta hidima har zuwa ranar suna inda yaro yaci sunan mahaifin Madu Idris.
Tun daga haihuwar Halima,Mariya ba ta sake haihuwa ba har sai da Hajara tayi haihuwa uku a jere duk maza wanda suke ganin so da k'auna da gata gurin Madu,Halima kuwa ko kallo ba ta isheshi ba a cewarsa bazai wahalta mata ba,dan su mata sai dai ka wahalta musu a banza ba tare da kaci moriyarsu ba,inda Allah ya taimaki Halima sai ya yota mai sanyin hali,ko kad'an ba ta dosar mahaifin nasu saboda ta san halinsa,abu kad'an za tayi ya mangareta har yanzu kuwa da take da shekaru takwas a duniya.
Hajara da Mariya a lokaci guda suka haihu inda Mariya macen dai ta kuma haifa,inda Hajara ta dinga yadar mata da maganganu shi kwa Madu ba ta isheshi kallo ba daga ita har jinjirar da ta haifa,inda Allah ya taimaketa ta tanadi komai na haihuwarta saboda tana sana'arta ta kayan miya bushashe da kuma wainar gero da k'uli da safe,tunda mai taimakon nata babu ita yanzu a doron k'asa,kamar haihuwar Halima wannan ma mahaifin Madu shi ya nad'awa jaririya suna RAHEENA.
Akwai bam-bamcin halaye k'ara k'ara tsakanin Halima da Raheena,Halima mai shiru shiru ce da sanyin hali,duk inda aka nuna ba'a sonta ba ta dosar gurin,yayin da Raheena ta kasance mai kwaraf niya ga tsokanar tsiya a cikinta kamar me,inda kuma Allah ya d'ora mata k'aunar mahaifinsu Madu duk da kasancewar shi yafi tsanarta ma akan Halima,dan dukan da take sha gurinsa bai daki Halima haka ba ga kyararta da yake anman ba shi zai hana ta koma gurinsa ba,zasu had'u ita da Mubarak tsarar haihuwarta d'an wajan Hajara suyi k'iriniya anman idan Madu ya tashi ko dunguri ba zaiwa Mubarak ba anman in ya kama Raheena da duka kamar Allah ya aikoshi.
Halayen Raheena suna mugun ciwa Mariya tuwo a k'warya anman babu yadda za tayi sai addu'a ta san k'uruciya ce ko wani yaro da kalar k'uruciyarsa nan gaba idan ta san ciwon kanta ba za tayi ba,gashi yanzu ta aurar da Halima tana cikin shekarunta na sha hud'u kenan Raheena kuma shida,komai na auran Halima Baffa Idris mahaifin Malam Madu shi yayi,har yau yana nisar da d'an nasa anma ya kasa ganewa shiyasa ya d'au ido ya zuba masa ya tabbata akwai ranar da zai gane kad'an daga cikin ni'imar da Allah ya yi maka idan ya azurtaka da samun 'ya mace.
Wannan kenan
……