Sashe 4
Halittar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
(4)
Malam ya kira sunansa,ya amsa yana me bawa Malam d'in dukkanin nutsiwarsa,dan da dukkan alamu magana ce zai masa mai muhimmanci,baiyi mamakin ganin bai cewa Inna ta bashi guri ba dan yasan akwai sirrikan Malan d'in da Innar ta sani wanda ko shi da ya haifa bai sansu ba.
"Wanene ni a gurinka." Malam ya jefo masa tambayar nan sai da ya numfasa kafin yace. "Mahaifina ne kai." "To a mtsayina na mahaifinka yau ina k'ara jaddada maka akan abinda muka sanar da kai ni da mahaifiyarka,ko bayan raina ka rabu da Mariya ko ka wulak'anta ta ban yafe maka ba,ina sane da har yau akwai nauyikan da baka sauke mata wannan kuma Allah ne zai tambayeka dalili,dan wallahi dalilinka ba dalili ba ne jahilci ne da jayayya da Ubangin,domin kuwa shine ya halicci ko wani jinsi,kuma shine nan ya bawa Mariya kyautar 'ya'ya matan da kake gudu ya kuma bawa Hajara mazan da kake so saboda haka yaso kuma haka yaga dama dukkaninsu ba zab'insu ba ne ba kuma son ransu ya zab'aba,sai dai dan hakan yayi niya kuma kyautar da yaga damar basu kenan.Bari na sanar da kai abinda baka sani ba,sanda Allah ya bamu cikinka fata muka dinga yi Allah yasa mace ce,anman da aka haifeka kazo a namiji haka muka nuna maka so da gata duk kwa tsanani da son da mukai na mace bai hana mun nuna maka k'auna ba,kuma daga kanka Innarka ba ta sake haihuwa ba har Allah ya bamu kyautar Mariya.
Dan haka abinda kake a tak'aice sunanshi jahilci,idan zaka gyara ka gyara dan wallahi abu d'aya nake jiye maka ranar da ZUCIYAR RAHEENA zata fara tsanarka,in bakai wasa ba kuwa sai kazo kana zub da hawayen ta soka wata rana a lokacin kuma bata da ikon yin hakan.Banga abin tsana a mace ba.Mahaifiyarka mace ce,kowa da ka gani a duniya silar zuwansa macece,idan ba macen za'a haifa ma mazan da kake so ne?
Mace na nufin k'warin guiwa.
Idan ba mace ba hayayyafa.
Idan ba mace ba rayuwar halitta.
Idan ba mace ba Zubin halitta.
Idan ba mace ba d'orewar gobe.
Idan ba mace babu ahali.
Idan ba mace babu gudanar da rayuwa.
Idan ba mace babu samun nutsuwar rayuwa.
idan ba mace ba ni'imar rayuwa.
Mace abar a tausayawa ce ba abar tsangwama da kyara ba. Idan maganganuna sun hankaltar da kai ruwanka,duk da ba yau na fara ba,idan kaci gaba da nunawa Raheena tsangwama da kyara ruwanka Allah yana gani."
Daga haka ya mik'e sukai sallama da Inna ya fice yabar Baba a durk'ushe ko karatun Malam ya shige shi?
(To wa ya sani sai mun bishi munji tukunna. )
Washe gari RAHENA ragas ta tashi,dan haka da su Bulki suka biyo mata makaranta a shirye suka tarar da ita,suna zuwa suka rankaya suka tafi Bulki rik'e da jakar Rahin d'in dan ita ke d'aukar mata ba kuma ta isa tace ta gaji baza ta d'auka ba.
"Rahin nima jiya fa banje makarantar ba Abun gidan Bawa me jakai na tsokana a burtsatse shekaran jiya shine na gudu tace sai a makaranta zata kama ni taci ubana."
"Me yasa ba ki gaya mata ubanki yayi mata kad'an ba sai dai taci Bawa me jakai dan shine dai dai da ita."
"Bari nayi sai yau ma gaya mata."
A dai dai nan suka shiga cikin ajinsu,Salima ce dake mugun son k'awance da Rahin ta taso ta tareta had'e da fad'in.
"Allah yasa kin tahon da wainar Inna ?"
"Na dai tawo da ita,idan an fita break in zamu ci sai na kirawoki ." "Me yasa jiya ba kizo ba?na tambayi Fad'ime ba ta kulani ba ." Dan haushinta suke ji yadda take likewa Rahinan ta k'arfin tsiya,yanzun ma tsaki sukai suka wucesu.
"Ban ji dad'i ba ne,nayi fama da zazzab'i."
"Ayya,Allah ya sawak'e,idan an fita break d'in sai mu fita tare yai d'ari Innata ta bani "
Washe baki Rahin tayi had'e da farin ciki,a ranta tana b'uyarwa su Bulki zasui wainar ma yau baza taci tare da su ba.
Bayan tashinsu daga makaranta ansha dambe tsakanin Abur wacce Bulki ta tsokano da Rahin,har sai da Rahin tayi mata k'ululu a goshi aikwa tayi rantsuwar baza ta yadda ba washe gari sai takai k'ara gurin Headmastee d'insu dan ba ma za ta kaiwa Innarsu k'arar ba da iyakacinta tace tayi hak'uri.
A k'aida kullum aka tashesu daga makaranta sai ta biya ta gidan Ya Halima,a k'ofar gidan suke rabuwa da su Bulki,su huce ita ta shiga ciki,to yauma hakance ta kasance,da gudu ta manna tayi cikin gidan kawa wacce aka biyo a guje,da ta daki wata buta dake babban tsakar gidan ba ta sauka a ko ina ba sai a gadon bayan Innar Audu (Surukar Halima)da ta tsuguna tana hura hutar iccen da ke ta bata wuya,a fusace ta d'ago dan ganin wanda ya jefo mata butar sukai ido hud'u da Rahin tana shishshigar da ido ciki sai kuma tayi murmushi ta bagarar kafin tace.
"Innar Audu me kike dafa mana ne." Dan haushi da takaici ba ta san sanda bakinta ya bata amsa da "Innarki Mariya nake dafa muku,dan tsabar rashin kunya ki jefon buta,sannan ki tsareni da k'ananun idanuwanki kina tambayata me nake dafa muku,to uwarki Mariya na had'a da yayarki Halima nake dafawa."
Turo baki gaba tayi kafin k'asa k'asa tace."Wannan mitsitsiyar tukunyar taki ai tawa Innata kad'an sai dai wannan tsililin mijin naki me kama da sandar rake,dan shi kam cif tukunyar zata amsheshi har da sarari" "Me kike cewa?" Innar Audu ta tambaya dan ganni bakinta yana motsi,sai kwa Rahin cewa tayi. "Ca nayi da kwa kin samu tsoka ba kamar k'yamushashen mijinki ba da motsatstsiyar Zuwairarki "(Itace Autar Innar daga Audu sai ita)
A harzuk'e Innar Audu ta d'auki muciya tayi kanta,da ta manna a guje tayi sashen Halima.
Halima kuwa tana can da d'an Audunta,fad'a suka yi da faccalarta ta mata gorin haihuwa shine take ta kuka shi kwa ya saka kayarsa a d'aki yace yau ba inda zashi sai sunyi cikin a yau yau d'innan.(To Malam Audu zafin nema ai baya kawo samu da yana kawo wa da mutane da yawa ba su jiggata ba,samu da rashi duka na Allah,Allah ka bamu zuri'a tsarkakakkiya.)
Jin yadda aka banko k'ofarsu aka shigo da mugun gudu yasa Audu hantsilawa gefen gadon yana k'ok'arin shigewa k'ark'ashin gadon,Halima kuwa cikin sif take k'ok'arin shigewa tsabar razana da kad'uwar da sukai babu wanda ya tsaya suturta jikinsa,duk a tunaninsu 'yan bindigar da aka ce suna harin k'auyansu ne suka shigo,a tsakar gidan ta tsaya tana rarraba idanu ,dan Inna ta hana ta afkawa mutane d'aki kai tsaye.
"Yaya Halima" Ta shiga rattaba mata kira,jin muryar Rahina yasa Halima sauke ajiyar zuciya da fasa shiga cikin sif din da take ta k'ok'arin yi,zani ta janyo ta d'aura,tana kallo Audu ma ya ja rigarsa yana maidawa,kallon Rahinan take cike da takaici kafin ta hauta da fad'an shigowa a gujen da tayi,sai cewa tayi." To ba Innar Audu ce ta biyoni da muciya ba" "Hala b'arnar da kika saba yi mata kikai mata?" "To ba ita bace daga tambayarta me take dafa mana tace Inna da ke take dafawa ba shine nace..." Saurin katseta Halima tayi,sanin cewar Audu yana jinsu,kuma tasan ba abu me dad'i Rahinan zata fad'a ba.
Fitowa Audun yayi yana.
"Kaga k'anwar matas,tafi matas kyau,duk da ba haka naso ba,amman haka dai nake maleji,dama can rufa ido aka mini"
Wani dad'i ne ya kasheta dan daga Baba Malam sai Innarta sai Audun ne kawai suke cewa tafi Halima kyahu,kowa sai dai kiji yace Halima ta fita kyau, Inna kwa cewa take a jira aga girman Rahinan tata musamman idan ta nutsu guri d'aya.
"Allah ya bar mini Yaya Auduna,anman da ni zaka tafi Habujar ko?"
"Ai k'afata k'afarki matas,dole naje da ke na sanya ki a makaranta mai kyau da inganci,Allah dai yasa Inna ta bamu ke."
Wani ihu da tsalle ta daka tana murna kafin tace.
"Zata baku mana,ai Inna tana so nayi karatu sosai,tace baza tamin aure da wuri kamar Yaya Halima ba."
"To ya zaki da saurayinki Tanimu?" Ya fad'a cike da tsokana. "
Cif wa zai auri wannan k'azamin gaja da shi? Nidai na tafi gayawa Inna da ni za'a Habuja."
Ba ta jirayi cewarsu ba ta manna a guje,tayi ball da tukunyar Innar Audu ta kife akan murhun ta kashe hutar da ta bata huya kafin ta kama anman ko waiwaye Rahin ba tayi ba ta fice,Innar Audu ta shiga sababi da masifa har sai da Halima ta kuma hura mata wutar ta mai da mata da tukunyar a ranta tana ta adduar Allah ya shirya musu RAHEENAH.
09037093702
Sa k'amshi sa dad'i,hana gafi k'arni no,spices da curry kenan gangariya gurin k'awata girki.
09037093702
Ina macen da girkinta ke k'arni idan tayi amfani da nama,ina macen da ke son amfani karafish tana tsoron k'arni,ina kuma macen da rashin albasa ke hanata soya k'wai,ina macen da take son girkinta ya k'ara dad'i da d'and'ano da kuma k'amshi?maza hanzarta ki nemi spices d'in Rashuna domin kuwa nata ba irin nasu ba ne.09037093702
Mata da dama idan suka soya kifi zubar da man suke saboda gudun k'arni,abinda kuma ba ku sani ba kun zubar da sinadarin ki kelaya abinki Hajiyata,ki kawo curry da spices d'in Rashuna ki zuba,Hmmm na rantse miki da Allah mityarki ba za tayi k'arni ba.
[9/18, 2:59 PM] Mtn Number: BEBEE'ARTH
HALITTAR
ZUCIYA.....
Watpad@Rashuna
Mama Jiddah
Heenah
Silar Soyayya
Masoya
Rabee'ah
Babbar Cuta
Muguwar Suruka
K'addarar Rayuwarmu
Cikin Duniyarmu500
Katanga500
Cin Amana500
Wadjda500
Halittar Zuciya500
Hak'k'in Mallaka.Rabee'ah Shu'ayb Nababa (Rashuna,Bebee'arth)Ban yadda a juya mini littafaina ba ko ta wata siga,duk wanda yaci da gumina idan ban gani ba Allah yana gani.
Malam ya kira sunansa,ya amsa yana me bawa Malam d'in dukkanin nutsiwarsa,dan da dukkan alamu magana ce zai masa mai muhimmanci,baiyi mamakin ganin bai cewa Inna ta bashi guri ba dan yasan akwai sirrikan Malan d'in da Innar ta sani wanda ko shi da ya haifa bai sansu ba.
"Wanene ni a gurinka." Malam ya jefo masa tambayar nan sai da ya numfasa kafin yace. "Mahaifina ne kai." "To a mtsayina na mahaifinka yau ina k'ara jaddada maka akan abinda muka sanar da kai ni da mahaifiyarka,ko bayan raina ka rabu da Mariya ko ka wulak'anta ta ban yafe maka ba,ina sane da har yau akwai nauyikan da baka sauke mata wannan kuma Allah ne zai tambayeka dalili,dan wallahi dalilinka ba dalili ba ne jahilci ne da jayayya da Ubangin,domin kuwa shine ya halicci ko wani jinsi,kuma shine nan ya bawa Mariya kyautar 'ya'ya matan da kake gudu ya kuma bawa Hajara mazan da kake so saboda haka yaso kuma haka yaga dama dukkaninsu ba zab'insu ba ne ba kuma son ransu ya zab'aba,sai dai dan hakan yayi niya kuma kyautar da yaga damar basu kenan.Bari na sanar da kai abinda baka sani ba,sanda Allah ya bamu cikinka fata muka dinga yi Allah yasa mace ce,anman da aka haifeka kazo a namiji haka muka nuna maka so da gata duk kwa tsanani da son da mukai na mace bai hana mun nuna maka k'auna ba,kuma daga kanka Innarka ba ta sake haihuwa ba har Allah ya bamu kyautar Mariya.
Dan haka abinda kake a tak'aice sunanshi jahilci,idan zaka gyara ka gyara dan wallahi abu d'aya nake jiye maka ranar da ZUCIYAR RAHEENA zata fara tsanarka,in bakai wasa ba kuwa sai kazo kana zub da hawayen ta soka wata rana a lokacin kuma bata da ikon yin hakan.Banga abin tsana a mace ba.Mahaifiyarka mace ce,kowa da ka gani a duniya silar zuwansa macece,idan ba macen za'a haifa ma mazan da kake so ne?
Mace na nufin k'warin guiwa.
Idan ba mace ba hayayyafa.
Idan ba mace ba rayuwar halitta.
Idan ba mace ba Zubin halitta.
Idan ba mace ba d'orewar gobe.
Idan ba mace babu ahali.
Idan ba mace babu gudanar da rayuwa.
Idan ba mace babu samun nutsuwar rayuwa.
idan ba mace ba ni'imar rayuwa.
Mace abar a tausayawa ce ba abar tsangwama da kyara ba. Idan maganganuna sun hankaltar da kai ruwanka,duk da ba yau na fara ba,idan kaci gaba da nunawa Raheena tsangwama da kyara ruwanka Allah yana gani."
Daga haka ya mik'e sukai sallama da Inna ya fice yabar Baba a durk'ushe ko karatun Malam ya shige shi?
(To wa ya sani sai mun bishi munji tukunna. )
Washe gari RAHENA ragas ta tashi,dan haka da su Bulki suka biyo mata makaranta a shirye suka tarar da ita,suna zuwa suka rankaya suka tafi Bulki rik'e da jakar Rahin d'in dan ita ke d'aukar mata ba kuma ta isa tace ta gaji baza ta d'auka ba.
"Rahin nima jiya fa banje makarantar ba Abun gidan Bawa me jakai na tsokana a burtsatse shekaran jiya shine na gudu tace sai a makaranta zata kama ni taci ubana."
"Me yasa ba ki gaya mata ubanki yayi mata kad'an ba sai dai taci Bawa me jakai dan shine dai dai da ita."
"Bari nayi sai yau ma gaya mata."
A dai dai nan suka shiga cikin ajinsu,Salima ce dake mugun son k'awance da Rahin ta taso ta tareta had'e da fad'in.
"Allah yasa kin tahon da wainar Inna ?"
"Na dai tawo da ita,idan an fita break in zamu ci sai na kirawoki ." "Me yasa jiya ba kizo ba?na tambayi Fad'ime ba ta kulani ba ." Dan haushinta suke ji yadda take likewa Rahinan ta k'arfin tsiya,yanzun ma tsaki sukai suka wucesu.
"Ban ji dad'i ba ne,nayi fama da zazzab'i."
"Ayya,Allah ya sawak'e,idan an fita break d'in sai mu fita tare yai d'ari Innata ta bani "
Washe baki Rahin tayi had'e da farin ciki,a ranta tana b'uyarwa su Bulki zasui wainar ma yau baza taci tare da su ba.
Bayan tashinsu daga makaranta ansha dambe tsakanin Abur wacce Bulki ta tsokano da Rahin,har sai da Rahin tayi mata k'ululu a goshi aikwa tayi rantsuwar baza ta yadda ba washe gari sai takai k'ara gurin Headmastee d'insu dan ba ma za ta kaiwa Innarsu k'arar ba da iyakacinta tace tayi hak'uri.
A k'aida kullum aka tashesu daga makaranta sai ta biya ta gidan Ya Halima,a k'ofar gidan suke rabuwa da su Bulki,su huce ita ta shiga ciki,to yauma hakance ta kasance,da gudu ta manna tayi cikin gidan kawa wacce aka biyo a guje,da ta daki wata buta dake babban tsakar gidan ba ta sauka a ko ina ba sai a gadon bayan Innar Audu (Surukar Halima)da ta tsuguna tana hura hutar iccen da ke ta bata wuya,a fusace ta d'ago dan ganin wanda ya jefo mata butar sukai ido hud'u da Rahin tana shishshigar da ido ciki sai kuma tayi murmushi ta bagarar kafin tace.
"Innar Audu me kike dafa mana ne." Dan haushi da takaici ba ta san sanda bakinta ya bata amsa da "Innarki Mariya nake dafa muku,dan tsabar rashin kunya ki jefon buta,sannan ki tsareni da k'ananun idanuwanki kina tambayata me nake dafa muku,to uwarki Mariya na had'a da yayarki Halima nake dafawa."
Turo baki gaba tayi kafin k'asa k'asa tace."Wannan mitsitsiyar tukunyar taki ai tawa Innata kad'an sai dai wannan tsililin mijin naki me kama da sandar rake,dan shi kam cif tukunyar zata amsheshi har da sarari" "Me kike cewa?" Innar Audu ta tambaya dan ganni bakinta yana motsi,sai kwa Rahin cewa tayi. "Ca nayi da kwa kin samu tsoka ba kamar k'yamushashen mijinki ba da motsatstsiyar Zuwairarki "(Itace Autar Innar daga Audu sai ita)
A harzuk'e Innar Audu ta d'auki muciya tayi kanta,da ta manna a guje tayi sashen Halima.
Halima kuwa tana can da d'an Audunta,fad'a suka yi da faccalarta ta mata gorin haihuwa shine take ta kuka shi kwa ya saka kayarsa a d'aki yace yau ba inda zashi sai sunyi cikin a yau yau d'innan.(To Malam Audu zafin nema ai baya kawo samu da yana kawo wa da mutane da yawa ba su jiggata ba,samu da rashi duka na Allah,Allah ka bamu zuri'a tsarkakakkiya.)
Jin yadda aka banko k'ofarsu aka shigo da mugun gudu yasa Audu hantsilawa gefen gadon yana k'ok'arin shigewa k'ark'ashin gadon,Halima kuwa cikin sif take k'ok'arin shigewa tsabar razana da kad'uwar da sukai babu wanda ya tsaya suturta jikinsa,duk a tunaninsu 'yan bindigar da aka ce suna harin k'auyansu ne suka shigo,a tsakar gidan ta tsaya tana rarraba idanu ,dan Inna ta hana ta afkawa mutane d'aki kai tsaye.
"Yaya Halima" Ta shiga rattaba mata kira,jin muryar Rahina yasa Halima sauke ajiyar zuciya da fasa shiga cikin sif din da take ta k'ok'arin yi,zani ta janyo ta d'aura,tana kallo Audu ma ya ja rigarsa yana maidawa,kallon Rahinan take cike da takaici kafin ta hauta da fad'an shigowa a gujen da tayi,sai cewa tayi." To ba Innar Audu ce ta biyoni da muciya ba" "Hala b'arnar da kika saba yi mata kikai mata?" "To ba ita bace daga tambayarta me take dafa mana tace Inna da ke take dafawa ba shine nace..." Saurin katseta Halima tayi,sanin cewar Audu yana jinsu,kuma tasan ba abu me dad'i Rahinan zata fad'a ba.
Fitowa Audun yayi yana.
"Kaga k'anwar matas,tafi matas kyau,duk da ba haka naso ba,amman haka dai nake maleji,dama can rufa ido aka mini"
Wani dad'i ne ya kasheta dan daga Baba Malam sai Innarta sai Audun ne kawai suke cewa tafi Halima kyahu,kowa sai dai kiji yace Halima ta fita kyau, Inna kwa cewa take a jira aga girman Rahinan tata musamman idan ta nutsu guri d'aya.
"Allah ya bar mini Yaya Auduna,anman da ni zaka tafi Habujar ko?"
"Ai k'afata k'afarki matas,dole naje da ke na sanya ki a makaranta mai kyau da inganci,Allah dai yasa Inna ta bamu ke."
Wani ihu da tsalle ta daka tana murna kafin tace.
"Zata baku mana,ai Inna tana so nayi karatu sosai,tace baza tamin aure da wuri kamar Yaya Halima ba."
"To ya zaki da saurayinki Tanimu?" Ya fad'a cike da tsokana. "
Cif wa zai auri wannan k'azamin gaja da shi? Nidai na tafi gayawa Inna da ni za'a Habuja."
Ba ta jirayi cewarsu ba ta manna a guje,tayi ball da tukunyar Innar Audu ta kife akan murhun ta kashe hutar da ta bata huya kafin ta kama anman ko waiwaye Rahin ba tayi ba ta fice,Innar Audu ta shiga sababi da masifa har sai da Halima ta kuma hura mata wutar ta mai da mata da tukunyar a ranta tana ta adduar Allah ya shirya musu RAHEENAH.
09037093702
Sa k'amshi sa dad'i,hana gafi k'arni no,spices da curry kenan gangariya gurin k'awata girki.
09037093702
Ina macen da girkinta ke k'arni idan tayi amfani da nama,ina macen da ke son amfani karafish tana tsoron k'arni,ina kuma macen da rashin albasa ke hanata soya k'wai,ina macen da take son girkinta ya k'ara dad'i da d'and'ano da kuma k'amshi?maza hanzarta ki nemi spices d'in Rashuna domin kuwa nata ba irin nasu ba ne.09037093702
Mata da dama idan suka soya kifi zubar da man suke saboda gudun k'arni,abinda kuma ba ku sani ba kun zubar da sinadarin ki kelaya abinki Hajiyata,ki kawo curry da spices d'in Rashuna ki zuba,Hmmm na rantse miki da Allah mityarki ba za tayi k'arni ba.
[9/18, 2:59 PM] Mtn Number: BEBEE'ARTH
HALITTAR
ZUCIYA.....
Watpad@Rashuna
Mama Jiddah
Heenah
Silar Soyayya
Masoya
Rabee'ah
Babbar Cuta
Muguwar Suruka
K'addarar Rayuwarmu
Cikin Duniyarmu500
Katanga500
Cin Amana500
Wadjda500
Halittar Zuciya500
Hak'k'in Mallaka.Rabee'ah Shu'ayb Nababa (Rashuna,Bebee'arth)Ban yadda a juya mini littafaina ba ko ta wata siga,duk wanda yaci da gumina idan ban gani ba Allah yana gani.