← Book details Fin Karfi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 12

Sashe 6

Fin Karfi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ya ce "wannan abun fa da nike sanar dake duk a can gida Katsina ya faru.

Momy ta ce "Tunda na ji ka kira ƙaton fili na gane can gida abin ya faru."

Ya ci gaba "Koda muka je gaban Alhaji Mansur shi da Alhaji Aminu Jega muka sameshi wani dallali kuma mai Kula da gine-ginen Alhaji Mansur da filayenshi muka zauna ƙasa muka gaisa dasu cikin girmamawa Alhaji Mansur ya dubeni "Kaine Sani."

Na ce "Eh,ni ne ranka yaÉ—aÉ—e."

Ya ce "muna tare da ku amma ban san ku ba?" Muka yi shiru.

Ya ci gaba "Ni nasan mahaifinku sosai dattijon arziƙi mai son jama'a sam shi abin shi be rufe mai ido ba,kun san fili na na kusa da ku gurinshi na amsa,naima filin kuɗin gwamnati, kuma na bada ma wasu kuɗin daga baya akai mishi ashe saƙon bai same shi ba." Mu kace ya wuce ba komai." Ya ce "yanzu ya labarin wannan gurin naku? Ni ina son gurin zan siya.

Na ce "To bari muje muyi shawara da sauran Æ´an'uwanmu, mahaifiyarmu tana nan da rai dan haka sai mun shawarta.

Ya ce "To hakan ya yi."

Jega dake gefe ya ce "Kuna da takardar gurin ta gwamnati?"

Na ce "Muna da ita."

Alhaji ya ce "Ku nawa ne gurin mahaifinku."

Na ce "mu sha É—aya ne sai mahaifiyarmu."

Ya ce "amma ai kuna da gidan kan ku ko?"

Na ce "ƙwarai gidan mu muke ciki."

Ya ce "Ni ku ɗauke ni tamkar ɗan'uwa don bazan cuceku ba, kuyi shawara nawa zaka saida min da gurin dan ba zan ci haƙƙin marayu ba."

Muka ce "To." Muka tashi muna godiya.

Bayan munyi shawara mu saida mishi sai muka sake dawowa da ƙanina. Miliyan uku da rabi muka ce su bamu.

Jega har yana cewa wai shima tunda shi ne yazo ya yi ma Alhaji tallar gurin sai mun bashi wani abu,sai muka ce babu komai.

Dubu É—ari biyar muka ce zamu bashi in an biya mu, duk da ba tallah muka yi ba.

Bayan wasu ƙwanaki suka bamu miliyan biyu saura ɗaya da rabi,da shike muna cikin buƙatar kuɗin ne sai muka ce mu raba.

Malamai ne ma dai suka raba mana kowa aka bashi nashi,muna jiran sauran kuɗin, rannan sai ga saƙo daga Jega,wai fili gwamnati ta riga ta ba wani, kuma wanda aka ba yaron Alhaji Mansur ne, don haka takardun mu na ƙarya ne mu dawo da kuɗi,ki na ji?

Momy ta ce "Ina sauraron ka." Ya ci gaba "Koda na ji sai naje na ce to muje land and sobe ɗin ai fayil ɗinmu na can a taƙaice dai Hajiya haka wannan Jega ɗin suka yo takardun bogi suka ce na gurin ne sai mu dawo da kuɗi. Bayan duk unguwarmu kowa yasan tsohonmu da gurin ga takardu ga komai, haka suka sa ƴan sanda suka kamamu suka tafi damu (State C.I.D) aka tsare mu da har ma ance gidan yari za'a kaimu tunda mu rasa wanda zamu cuta sai (former I.G).

Munsha wuya,don ma ƴan'uwanmu da Abokaina sun yi ta ƙoƙarin ganin haɗa kuɗin an basu, tunda sun ce sai mun basu kuɗin su sannan zasu sake mu, wasu suka ce duk sharrin Jega ne aje a samu (Former I.G) shi zai sa a fito damu dan mutumin kirki ne, ana zuwa ya ce magana tana gurin Jega, anyi-anyi amma yaƙi ya ce a sake mu, tunda shi ne mai kuɗin, Hajiya lokacin ƴan'uwana da mahaifiyarmu sun shiga tashin hankali, mata ta......

🖊️🖊️🖊️
[7/28, 08:27] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 2*

*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*

Page 4

Mata ta da yarana, lokacin su waɗannan ya nuna su (Ruƙayya)suna ƙanana haka ƴan'uwa da Abokaina suka dinga samun manyan mutane don su sa baki, amma kowa ya ji da (Former I.G)ne Alhaji Mansur,sai suce gaskiya sai dai kayi haƙuri ba zamu iya tunkarar shi ba, don ubanmu ne, to Hajiya ƙarewa ma ƙwamishinan ƴan sanda na jihar Katsina a wancan zamanin shi ne da kanshi ya zo ya tafi damu, kuma don tsohon wulaƙanci.

Bayan mun saida sauran kadarorinmu mun haɗa miliyan biyun su mun basu sai da muka ƙara ƙwana uku sannan suka sake mu,bugu da ƙari sun sa ƙwamishina ya amsa mana takardar gurin. Kinga sun amshe mana guri ga ɗauri ga kuma asarar sauran kadarorinmu, baƙin cikin wannan abun shi ne yasa ni nabar Katsina na dawo nan Kaduna da zama, kayan koli nike saidawa kuma ba laifi dashi ne na samu na sai wannan tsohon gidan nawa kuma nike biyawa yara kuɗin makaranta nake ci dasu.

Sannan yanzu duk mutumin da ya yi min wannan aikin na ɗan shi ƴata,ai ko ƴan sanda ka kira min ka gama da ni bare har kasa a tsare ni saboda haka kayi haƙuri ba zan iya bada ƴata gare ka ba, kayi haƙuri.

Gwiwa biyu Dady ya durƙusa a gaban Affa ya ce "don Allah Affa ka taimake ni kada kaimin haka."

"Ni ban maka komai ba." Yusufa ba ƙaramin ɓakin cikin rashin wannan auran nayi ba,don har ga Allah zuciyata tana tsananin son ka har yanzu,sai dai in har na baka ƴata Yusufa ban ma san abin da nake yi ba kenan."

Momy ta yi ajiyar zuciya sannan ta ce "Tabbas nasan sanda abin nan ya faru domin kusan mata uku a wancan lokacin sun zo dan neman nayi ma Alhaji magana, koda nai masa sai ya ce min maganar ta mutu."

Affa ya ce "To kin ji ma kinsan lokacin."

Ta ce "To don Allah Affan Ruƙayya kada ka biyewa halin shi, kayi haƙuri don Allah."

Ya ce "Hajiya na gama magana, hawaye Dady yake sosai amma Affa ya ce "ina."

Itama Ruƙayya sai ta samu da jin zafin abinda Dad ya yi wa Affan ta.

Amma duk da haka sai ya zamo bata ga laifin Dady ba, tunda shi ba shine ya yi ma Affa ba, ta dubi Dady ya ruÉ—e ya fita haiyacin shi.

Ta dube shi ta ce"Kayi haƙuri Allah zai baka wadda ta fini."

Cikin ruɗewa ya ce "Kina nufin kin haƙura dani? Kada kiyi min haka Pretty ni mai sonki ne har abada."

Kuka sosai Ruƙayya ta saki cikin kukan ta ce "Bayan da zan yi ne."

Fati da Murja suka dube ta cikin ƙulewa,dan sukam sun matuƙar jin zafin abinda Dad ya yi ma Affa dan haka sai suka ce "ke kima mutane shiru, tashi mu je tunda ke baki kishin ubanki."

Ruƙayya ta ce "Ku tausaya min rabani da Dady ba ƙaramin abu bane." Suka yi tsaki suka fita.

Momy ta kasa magana dan tasan lallai an ma Affa FIN ƘARFI, yanzu tana jin nauyin ta matsa mishi,miƙewa tayi ta kama hannun Dady ta ce "To zo muje mu bar komai a hannun Allah."

Affa ya ce "Ga kuÉ—in ku nan bari a fita da jakunkunan kayan."

Momy ta ce "Kar kayi haka Affan Ruƙayya,ai Ruƙayya ƴata ce,dan haka daga kayan har kuɗin na bar mata."

Affa ya ce "a'a sam." Momy ta ce,in har kace haka to tabbas akwai wani abu a ranka,ba mahaifin Dady ya baka ba,ni ce nan kuma ko É—aya ban ga laifin ka ba sai na mahaifinshi, domin ko ni akai ma haka, tsakani da Allah ba zan bayar da Æ´ata ba."

Ganin zasu fita Affa ya ce "To shikenan."

Ruƙayya ta duƙar da kai tana kuka mai tsuma rai, sauraron ta Affa yake tayi, tayi har muryar ta ta dushe, ya ce"ki yi haƙuri Ruƙayya ban maku FIN ƘARFI ba,bana son mahaifinshi ya raina min wayo,ko ba komai zai san cewa shima talaka yana da rana da kuma baiwa, wacce zayayi iko da ita, ina son ki nutsu ki bar zancen aure, karatun ki shi zaki sa gaba,ki manta da Yusufa dan ki samu zaman lafiya a cikin gidan nan, tunda matsawar kika bijiremin ko ƴan'uwanki ba zaki samu ƙwanciyar hankali da su ba."

Ta ce "To."

Ya ce "Maza tashi kije kiyi sallah."

Ta miƙe ta fita. Koda ta shiga ɗakinsu su Murja suna sallah, bayan sun idar itama ta idar ta tashi taje ta kawo musu abinci, ta koma kan katifa ta ƙwanta saboda tsabar ciwon kai,da yake damun ta suka bita da kallo, basu ce ƙala ba suka cigaba da cin abincin su suna hira,taji tausayin kanta wato ma fushi suke yi da ita,tasan da dane taƙi cin abinci zasu yi ta lallashin ta ne har sai taci. Isha'i ma sai a zaune tayi ta ƙwanta cikin tunanin Dady. Shikenan yanzu soyayyarsu ta zama tarihi, tsarin da Dady ya yi musu na zaman aure yasha ruwa,ta tuna wata rana da suke hira da Dady game da bikin su,ya ce "Pretty." Ta dube shi ya ce in mukayi aure nifa kinsan ina son haihuwa da wuri, ina son yarinya ta mace ƙyaƙƙyawa, Ruƙayya tayi dariya ta ce, Ni bana son na haihu da wuri, ya ce "Saboda me?" Ta ce "don na tsufa kai ka auro wata ya yi dariya ya ce "Ai Pretty duniya da lahira ke kaɗai ce mata ta kuma uwar ƴaƴana kullum in ta tattalin ku ina shagwaɓa ku, komai ni zan miki kamar bawa zan koma miki abinci a baki,in miki wanka,in miki wanki,in ki ka ce be miki ba sai na sake miki wani,in zamu fita ni ne mai ɗaukar miki jaka, hannu tasa a bakin ta tana dariya tana faɗin kada kasa ace na mallake ka, ya ce na nawa aini yanzu sai yanda kika ce,kin san Momy zata so mu taso yaranmu.

Ruƙayya ta ƙara fara sabon kuka, Fati ta dubi Murja ta ce , Murja ki ji min ikon Allah zata cika mana kunne.

Murja ta je ta jawo ta ta zauna,bazaki mana shiru ba ko?

Cikin sarƙewar murya da shashshekar kuka ta ce "Yanzu ba zaku tausayawa halin da na shiga ba."

Fati ta ce "Ba fa zancen tausayi a cikin sa kai dan wannan sa kaine, kuma ki mana shiru ko ki ci duka."

Tasan tsaf zasu dake ta,dan haka sai tayi shiru tare da yin kukan zuci.
Chapter 6 · 0% Book details