Sashe 12
Fin Karfi Part 2 Complete Hausa Novel · about 2 min read
Sadiya tana dariya ta miƙa ma M Bash wayar. Cikin shagwaɓa ta ce "Hello Babyna." Ya ce "Sweet Darling me yake faruwa ne, ance kin fasa zuwa dinner ɗin.?"
Cikin shagwaɓa tamkar zata rushe da kuka ta ce "Ba Ruky M bace tace wai ta fasa zuwa nima shi ne kawai na fasa Please ka zo da kanka in kana son na je sai mu lallashe ta ko?"
Ya ce "four mint gani nan."
Shi da Master suka zo har cikin bedroom ɗin suka shigo yanda suka ƙwanta tuni suka tashi suka sake, Munira tana ta ɗan danne-danne a waya kanta na saman cikin Ruky, Al-Mustapha dariya suka bashi ya ce "Haba Ruƙy ke kuma da zaki gyara wasa sai kuma ki ɓata."
Ta tashi tana dariya ta ce "Ban ɓata ba Al-Mustapha na ce bazan samu zuwa bane shi ne wannan shagwaɓaɓɓiyar amaryar taka tace ta fasa sai ka ce kaine kace ba zaka je ba."
Ya ce "To ke me yasa bazaki bane?"
Ta ce "Wani dalili ne kawai."
Master yasa baki "Haba baby a gurin nan na boby kin gane?"
Al-Mustapha ya ce "Kai kuma malam kai mana shiru."
Ruƙy ta harari Master, ya ce "Allah ya huci zuciyarki Baby gani nayi kin fi sauran aji ko baki san aji ba?"
Al-Mustapha ya dube ta "don Allah Ruky saboda menene?"
Ta ce "Gaskiyar magana aƙwai wanda bana son mu haɗu da shi.
Ya ce "Kada ki damu ba zaku haɗu ba."Nan dai ta yarda zata daƙyar........
Ku ɗan ƙaramin haƙuri zuwa na uku dan jin yadda zata kaya..
Taku Halima Abdullahi K/Mashi
Cikin shagwaɓa tamkar zata rushe da kuka ta ce "Ba Ruky M bace tace wai ta fasa zuwa nima shi ne kawai na fasa Please ka zo da kanka in kana son na je sai mu lallashe ta ko?"
Ya ce "four mint gani nan."
Shi da Master suka zo har cikin bedroom ɗin suka shigo yanda suka ƙwanta tuni suka tashi suka sake, Munira tana ta ɗan danne-danne a waya kanta na saman cikin Ruky, Al-Mustapha dariya suka bashi ya ce "Haba Ruƙy ke kuma da zaki gyara wasa sai kuma ki ɓata."
Ta tashi tana dariya ta ce "Ban ɓata ba Al-Mustapha na ce bazan samu zuwa bane shi ne wannan shagwaɓaɓɓiyar amaryar taka tace ta fasa sai ka ce kaine kace ba zaka je ba."
Ya ce "To ke me yasa bazaki bane?"
Ta ce "Wani dalili ne kawai."
Master yasa baki "Haba baby a gurin nan na boby kin gane?"
Al-Mustapha ya ce "Kai kuma malam kai mana shiru."
Ruƙy ta harari Master, ya ce "Allah ya huci zuciyarki Baby gani nayi kin fi sauran aji ko baki san aji ba?"
Al-Mustapha ya dube ta "don Allah Ruky saboda menene?"
Ta ce "Gaskiyar magana aƙwai wanda bana son mu haɗu da shi.
Ya ce "Kada ki damu ba zaku haɗu ba."Nan dai ta yarda zata daƙyar........
Ku ɗan ƙaramin haƙuri zuwa na uku dan jin yadda zata kaya..
Taku Halima Abdullahi K/Mashi