Sashe 4
Fin Karfi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri ya ja motar mutanen bakin lungun da zauna gari gulma dama ji suke kamar su shiga lungun su ga meke faruwa,sai suka ganshi ya fito ya ja motar yayi ƙasa, wasu suka ce kai yaron nan yana tsakanin son yarinyar nan,ji bi duk ya damu.
Wasu kuma suka ce,in sune me zasuyi da wata Ruƙayya,dama dai Yayartace don kaf ƴan'uwanta sun fi ta ƙyau, wani kuma dake can gefe ya ce "Kai itama fa yarinyar akwai ta fa,kai mata uzuri nan da ƴan shekaru,ai ƙaramar yarinya ce shi yasa" shi ko wani cewa ya yi tsohonta ai ya mata buƙulu, wannan yaron fa ɗan gidan former I.G ne fa ubanshi har Gwamna ya yi a Katsina. Kuma shi ne ɗan daya mallaka ɗaya tilo. Ruƙayya ta fito dan kada sa'idawan bakin lungun su sa mata ido,sai tayi sama don tayi zagaye ta wani lungu, da ido suka bi ta suna ci gaba da sharhi akan fasa auran nata,yana tsaye jikin motar gefen direba, kanshi ya kifa a saman murfin motar da yake a buɗe,sam bai san zuwan ta gurin ba,sai dai ji yayi ta ce "Dady."
Da sauri ya juyo,motar ya shige sannan ya buɗe mata ɗaya ƙofar ta shiga ta rufe duk da akwai ƙarancin mutane sai da ya rufe gilasan motar sannan ya kunna (A.C) ya juya yana mai da dukkan hankalinshi akan ta "Pretty to yau menene abin yi?"
Ta ce "To nidai ka samu Affa ko yaya ka ce?
Ya yi shiru na É—an lokaci sannan ya ce "kamar yaushe kenan?"
Ta ce "ko yau da dare ne."
Ya yi ajiyar zuciya sannan ya ce "Ya Allah na ma rasa gane kan wannan matsalar,na rasa wanda ya yi mana wannan sanadin tsiyar don wannan, domin bala'i ne."
Ruƙayya ta ce "Bakomai, akwai Allah."
Ya ce "haka ne Pretty, ina son yanzu mu yiwa juna wani alƙawari."
Ta dube shi kamar yaya?
Ya ce "yauwa ina son ki min alƙawarin duk rintsi duk tsanani duk wahala ba zaki rabu dani ba,nima zan miki wannan alƙawarin." Ya miƙo mata ƴar ƙaramar batta kamar aƙwati ya ciro zobuna guda biyu masu shegen ƙyau,
Ta dube shi "Dady ai munyi alƙawarin."
Ya ce "Wannan da zamuyi na musamman ne, kuma yana nufin ba rabuwa."
Ta dube shi sam fuskarshi babu wasa don haka ita ma ta nutsu.
Ya ce "bani yatsan alƙawarin ki." Ta miƙa mishi ya kama dogon yatsan nata mai ɗauke da ƙyakƙyawar ƙumba ya lallatsa ya ciro zoben sai faman ƙyalli yake yi Stone ɗin jiki green.
Ya ce "na ɗauki alƙawari ni Yusuf bazan rabu dake Ruƙayya ba, rana ko dare, ciwo ko tsufa,nakasa ko wahala, Allah kai ne shaida, ya zura mata zoban, jikinta yayi matuƙar sanyi,lallai Dady,ya shiga sosai ya miƙo mata zoben da zata sa mishi gami da yatsan shi,jiki ba ƙarfi ta amsa gami da kama lallausan yatsan shi tamkar bana namiji ba.
Ta ce "To me zan ce?"
Ya ce "abin da ki ka ji nace."
Itama ta maimaita irin kalaman da ya faɗa na alƙawari tana gamawa tasa mishi,gaba ɗaya sai taji wani abu ya ratsa ta kamar tsawa ta dube shi ta ce "kaji abin da ya ratsani kuwa?" Ya ce "kamar yaya?"
Ta ce "ina gama ɗaukar alƙawarin sai naji tamkarr an yi tsawa.
Ya yi murmushi dan ya tsoratar da ita sai ya ce "kin san girman alƙawari kuwa?"
Ta ce, Eh.
Ya ce "To sai ki kiyaye in kuma ki ka karya to wannan tsawar sai ta ci ki."
Ta ce "to bazan karya ba."
Ya ce "Ina phone É—in ki?"
Ta dube shi"tana gida."
Ya ce "to ta zama tana kusa da ke zan dinga kiran ki ko cikin dare ne, sannan yau zan ga Affa bayan magriba."
Ta ce "kasan fa su Yaya Murja dasu muke ƙwana zasu sani kuma zasu saɓamin tun da Affa dasu ya kafa shaida kuma in ya sani suma zata shafe su tunda zai ce sune ya kamata su san halin da nake ciki,su sani hanya mai ƙyau, tare da bin dokar shi.
Ya ce "ki bari zan san yaya zamu yi sai dai in naga Affan yau."
Ta ce zan tafi kada Yaya Fati ta dawo bana nan."
Ya ce "to sai kin jini yarda muka yi anjima dashi zaki ji."
Ta ce "to" ya buɗe mata ƙofa ta fito, sai da yaga ƙulewarta sannan shi ma ya tada motar. Tana isa cikin gida bayan tayi cefane sai ta samu Yaya Fati har taji tsoro ya kamata,dan bata san yamma tayi sosai ba haka."
Harara Yaya Fati ta sakar mata sannan ta ce "Ya yi miki ƙyau, ina kika tafi haka? Cikin faɗuwar gaba ta ce "Cefane fa na je."
Yaya Fati ta ce "Cefane amma ai ba'a nan unguwar ki kayo ba ko? Kusan awa biyu da rabi nima nayi a gidan da dawowa, ƙila satabakin dogo ki ka je?
Ruƙayya dai tayi shiru,Fati ta ce "Ni bani in kin ga dama kije kiyi sallar la'asar,ga wanke-wanke nan. Ruƙayya ta wuce Fati tana ta faɗa tana ci gaba da aiki.
Dady cikin ƴar damuwa ya isa gidan Hajja yana yin sallama, Hajja ta fito daga ɗaki tana faɗin Muryar wa nike ji ne ya yi ƴar fara'a ya ce "Ni ne dai mai gidan , ta ce mai sunan mai gidan dai ashe kana da sauran shan ruwa ɗan nan? Aini fushi nayi da iyayen ka tunda sun ƙi ƴar talaka sai ƴar masu hali, mutumin nan dattijon kirki amma sai da ubanka ya yi sanadin fasa auran."
Ta ce "To sai ka bincika ai shi ba mahaukaci bane da zai sa a tara jama'a sannan kuma ya ce ya fasa."
Dady ya ce "Da aƙwai dalili kam."
"Kinsan ni dashi mahaifin nata aƙwai fahimtar juna,in anjima zan je gunsa nasan zaya fiddani daga duhu."
Ta ce "to Allah ya taimaka yaya ƙarfin jikin?"
Ya ce "Alhmdllh."
Ta ce "ja'iri in anzo nan ayi ta cika min baki sai gashi zaka mutu kan ƙaramar yarinya."
Ya ce "Eh, bakomai duk a cikin sone,so ba ƙarya bane."
Ta ce "Ai fa gashi nan na gani ku so ya dama,shi yasa kullum kuna cikin wahala,mu zamanin mu ina ruwan mu da wani so."
Ya juyo ya fuskance ta cikin dariya ya ce "kenan auren dole ake maku."
Ta ce "Ba wani dole kinsan mijinki bare mu gidan mu tsohonmu sadaka yake bada ƴaƴansa bai taɓa amsar sadakinmu ba."
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[7/26, 18:11] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 2*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 3
Dady yana dariya ya miƙe ya buɗe fridge ya ɗauko Hollandia ya ce "Ina Baba Saude?"
Ta ce "ta je É—auko mana markaÉ—en waina."
Ya ce "To wai Hajja shima tsohon mijin naki haka aka ce miki ga miji?".
Ta ce "ƙwarai kuwa to mu ko kinada ƴan samarin ki na dandali ba lallai bane ki auri ɗayan su dan ni kakan ka ko ganinshi ban taɓa yi ba sai da aka kaini gidan su."
Ya ce "Shi fa ya taɓa ganin ki?"
Ta ce a ina zai ganni? Mahaifinshi aminin tsohon mu ne ba ma a Katsina ya ke ba yana gurin yar mahaifinsu a Huntuwa sai da aka yi auranmu sannan ya dawo nan gidan su."
Dady ya ce "Da kenan ni yanzun ya ma za'a yi na yarda."
Ta ce "To bama kai ba mahaifinka ma soyayya yayi da uwar ka kan ayi auren shi ka biyo ai da yake ance magaji ma fiyi taka take murika tashi."
Dady yayi shiru ya ce "Zan kam bar tarihi dan ni nasan tawa ta ƙare."
Hajja ta ce"kai dai baka da fatan arziƙi mu can za labari."
Ya ce "wa ne canza labari Hajja aini banida labari mafi soyuwa a raina kamar na Pretty na."
Ta ce "Kai ni ja can ga sunan yarinya Ruƙayya mai daɗi amma kaƙi kiranta dashi sai wani kiristine ko pristine ma Oho."
Yayi dariya ya ce "Hajja tawa ni na Ruƙayya gashi kina son sunan ta amma baki iya faɗa ba wai Rukayya."
Ta ce "Aifa ku Æ´an bokon nan komai aka ce ba'a iya ba sai ku."Haka sukayi ta hira har zuwa sallar magriba.
Dady yana zaune gaban Affa bayan sun gaisa sai ya ce "Yusufa sai kuma ka ji yanda Ubangiji ya yi ikon sa ko?"
Dady kanshi a ƙasa ya ce "na ji Affa sai dai har ya zuwa yanzu kaina yana duhu Affa ban san laifi na ba kai min irin wannan horon duk da nasan kai uba ne na gari mai hangen ƙwarai nasan bisa ga babban dalili ka aikata wannan abu zan so nasan dalili inda hali.
Jikin Affa ya yi sanyi ƙwarai da jin lafazin Yusuf kuma har ma yaji kunya, ya gyara zama sannan ya ce "Yusufa da farko dai kai min afuwa har ga Allah da nasan cewa Alhaji Mansur Yusuf Katsina shine mahaifin ka da babu dalilin da zan baka ƴata da sauri Dady ya dubi Affa bakin shi yana rawa ya ce "Affa saboda me?"
Affa ya ce "kafin haka ina son kayi haƙuri ka bar Ruƙayya,ga kayan ku nan da kuɗin ku kai hatta ƙyautar farko da kayi mata duk da na kashe,na samo na harhaɗa na maida na fasa baka Ruƙayya mahaifinka shi ne yakamata ya baka labarin dalilin da yasa na fasa aura maka ƴata, kuma nima dole ne na hana aurenta koda hakan yana nufin zaku rasa rankune kai da ita zan so ka gane, yanzu bari na shiga in sa a haɗo maka kayan ku. Zan cigaba da yi maka fatan alheri dan kaifa ɗa ne Yusuf."
Æari jikin Dady ya soma yi ya kasa magana har sanda Affa ya shigo ya zube mishi kuÉ—i a gabansa,ko takan kuÉ—in Dady bai bi ba, ya ce "Ka ce na tambayi Dad É—ina ko?"
Affa ya ce "Ƙwarai ka ce masa wanene koda yake ai kasan Jega ko?
Ya ce "Alhaji Aminu Jega?"
Affa ya ce "Shi"
Dady ya ce "nasan shi, shi ne mai kula da harkokin gine ginen Dad É—ina."
Affa ya ce "yauwa ka ko san shi, to ka je kace da mahaifin naka na ce ya sanar da kai me ke tsakanina dashi da Jega?"
Wasu kuma suka ce,in sune me zasuyi da wata Ruƙayya,dama dai Yayartace don kaf ƴan'uwanta sun fi ta ƙyau, wani kuma dake can gefe ya ce "Kai itama fa yarinyar akwai ta fa,kai mata uzuri nan da ƴan shekaru,ai ƙaramar yarinya ce shi yasa" shi ko wani cewa ya yi tsohonta ai ya mata buƙulu, wannan yaron fa ɗan gidan former I.G ne fa ubanshi har Gwamna ya yi a Katsina. Kuma shi ne ɗan daya mallaka ɗaya tilo. Ruƙayya ta fito dan kada sa'idawan bakin lungun su sa mata ido,sai tayi sama don tayi zagaye ta wani lungu, da ido suka bi ta suna ci gaba da sharhi akan fasa auran nata,yana tsaye jikin motar gefen direba, kanshi ya kifa a saman murfin motar da yake a buɗe,sam bai san zuwan ta gurin ba,sai dai ji yayi ta ce "Dady."
Da sauri ya juyo,motar ya shige sannan ya buɗe mata ɗaya ƙofar ta shiga ta rufe duk da akwai ƙarancin mutane sai da ya rufe gilasan motar sannan ya kunna (A.C) ya juya yana mai da dukkan hankalinshi akan ta "Pretty to yau menene abin yi?"
Ta ce "To nidai ka samu Affa ko yaya ka ce?
Ya yi shiru na É—an lokaci sannan ya ce "kamar yaushe kenan?"
Ta ce "ko yau da dare ne."
Ya yi ajiyar zuciya sannan ya ce "Ya Allah na ma rasa gane kan wannan matsalar,na rasa wanda ya yi mana wannan sanadin tsiyar don wannan, domin bala'i ne."
Ruƙayya ta ce "Bakomai, akwai Allah."
Ya ce "haka ne Pretty, ina son yanzu mu yiwa juna wani alƙawari."
Ta dube shi kamar yaya?
Ya ce "yauwa ina son ki min alƙawarin duk rintsi duk tsanani duk wahala ba zaki rabu dani ba,nima zan miki wannan alƙawarin." Ya miƙo mata ƴar ƙaramar batta kamar aƙwati ya ciro zobuna guda biyu masu shegen ƙyau,
Ta dube shi "Dady ai munyi alƙawarin."
Ya ce "Wannan da zamuyi na musamman ne, kuma yana nufin ba rabuwa."
Ta dube shi sam fuskarshi babu wasa don haka ita ma ta nutsu.
Ya ce "bani yatsan alƙawarin ki." Ta miƙa mishi ya kama dogon yatsan nata mai ɗauke da ƙyakƙyawar ƙumba ya lallatsa ya ciro zoben sai faman ƙyalli yake yi Stone ɗin jiki green.
Ya ce "na ɗauki alƙawari ni Yusuf bazan rabu dake Ruƙayya ba, rana ko dare, ciwo ko tsufa,nakasa ko wahala, Allah kai ne shaida, ya zura mata zoban, jikinta yayi matuƙar sanyi,lallai Dady,ya shiga sosai ya miƙo mata zoben da zata sa mishi gami da yatsan shi,jiki ba ƙarfi ta amsa gami da kama lallausan yatsan shi tamkar bana namiji ba.
Ta ce "To me zan ce?"
Ya ce "abin da ki ka ji nace."
Itama ta maimaita irin kalaman da ya faɗa na alƙawari tana gamawa tasa mishi,gaba ɗaya sai taji wani abu ya ratsa ta kamar tsawa ta dube shi ta ce "kaji abin da ya ratsani kuwa?" Ya ce "kamar yaya?"
Ta ce "ina gama ɗaukar alƙawarin sai naji tamkarr an yi tsawa.
Ya yi murmushi dan ya tsoratar da ita sai ya ce "kin san girman alƙawari kuwa?"
Ta ce, Eh.
Ya ce "To sai ki kiyaye in kuma ki ka karya to wannan tsawar sai ta ci ki."
Ta ce "to bazan karya ba."
Ya ce "Ina phone É—in ki?"
Ta dube shi"tana gida."
Ya ce "to ta zama tana kusa da ke zan dinga kiran ki ko cikin dare ne, sannan yau zan ga Affa bayan magriba."
Ta ce "kasan fa su Yaya Murja dasu muke ƙwana zasu sani kuma zasu saɓamin tun da Affa dasu ya kafa shaida kuma in ya sani suma zata shafe su tunda zai ce sune ya kamata su san halin da nake ciki,su sani hanya mai ƙyau, tare da bin dokar shi.
Ya ce "ki bari zan san yaya zamu yi sai dai in naga Affan yau."
Ta ce zan tafi kada Yaya Fati ta dawo bana nan."
Ya ce "to sai kin jini yarda muka yi anjima dashi zaki ji."
Ta ce "to" ya buɗe mata ƙofa ta fito, sai da yaga ƙulewarta sannan shi ma ya tada motar. Tana isa cikin gida bayan tayi cefane sai ta samu Yaya Fati har taji tsoro ya kamata,dan bata san yamma tayi sosai ba haka."
Harara Yaya Fati ta sakar mata sannan ta ce "Ya yi miki ƙyau, ina kika tafi haka? Cikin faɗuwar gaba ta ce "Cefane fa na je."
Yaya Fati ta ce "Cefane amma ai ba'a nan unguwar ki kayo ba ko? Kusan awa biyu da rabi nima nayi a gidan da dawowa, ƙila satabakin dogo ki ka je?
Ruƙayya dai tayi shiru,Fati ta ce "Ni bani in kin ga dama kije kiyi sallar la'asar,ga wanke-wanke nan. Ruƙayya ta wuce Fati tana ta faɗa tana ci gaba da aiki.
Dady cikin ƴar damuwa ya isa gidan Hajja yana yin sallama, Hajja ta fito daga ɗaki tana faɗin Muryar wa nike ji ne ya yi ƴar fara'a ya ce "Ni ne dai mai gidan , ta ce mai sunan mai gidan dai ashe kana da sauran shan ruwa ɗan nan? Aini fushi nayi da iyayen ka tunda sun ƙi ƴar talaka sai ƴar masu hali, mutumin nan dattijon kirki amma sai da ubanka ya yi sanadin fasa auran."
Ta ce "To sai ka bincika ai shi ba mahaukaci bane da zai sa a tara jama'a sannan kuma ya ce ya fasa."
Dady ya ce "Da aƙwai dalili kam."
"Kinsan ni dashi mahaifin nata aƙwai fahimtar juna,in anjima zan je gunsa nasan zaya fiddani daga duhu."
Ta ce "to Allah ya taimaka yaya ƙarfin jikin?"
Ya ce "Alhmdllh."
Ta ce "ja'iri in anzo nan ayi ta cika min baki sai gashi zaka mutu kan ƙaramar yarinya."
Ya ce "Eh, bakomai duk a cikin sone,so ba ƙarya bane."
Ta ce "Ai fa gashi nan na gani ku so ya dama,shi yasa kullum kuna cikin wahala,mu zamanin mu ina ruwan mu da wani so."
Ya juyo ya fuskance ta cikin dariya ya ce "kenan auren dole ake maku."
Ta ce "Ba wani dole kinsan mijinki bare mu gidan mu tsohonmu sadaka yake bada ƴaƴansa bai taɓa amsar sadakinmu ba."
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[7/26, 18:11] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 2*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 3
Dady yana dariya ya miƙe ya buɗe fridge ya ɗauko Hollandia ya ce "Ina Baba Saude?"
Ta ce "ta je É—auko mana markaÉ—en waina."
Ya ce "To wai Hajja shima tsohon mijin naki haka aka ce miki ga miji?".
Ta ce "ƙwarai kuwa to mu ko kinada ƴan samarin ki na dandali ba lallai bane ki auri ɗayan su dan ni kakan ka ko ganinshi ban taɓa yi ba sai da aka kaini gidan su."
Ya ce "Shi fa ya taɓa ganin ki?"
Ta ce a ina zai ganni? Mahaifinshi aminin tsohon mu ne ba ma a Katsina ya ke ba yana gurin yar mahaifinsu a Huntuwa sai da aka yi auranmu sannan ya dawo nan gidan su."
Dady ya ce "Da kenan ni yanzun ya ma za'a yi na yarda."
Ta ce "To bama kai ba mahaifinka ma soyayya yayi da uwar ka kan ayi auren shi ka biyo ai da yake ance magaji ma fiyi taka take murika tashi."
Dady yayi shiru ya ce "Zan kam bar tarihi dan ni nasan tawa ta ƙare."
Hajja ta ce"kai dai baka da fatan arziƙi mu can za labari."
Ya ce "wa ne canza labari Hajja aini banida labari mafi soyuwa a raina kamar na Pretty na."
Ta ce "Kai ni ja can ga sunan yarinya Ruƙayya mai daɗi amma kaƙi kiranta dashi sai wani kiristine ko pristine ma Oho."
Yayi dariya ya ce "Hajja tawa ni na Ruƙayya gashi kina son sunan ta amma baki iya faɗa ba wai Rukayya."
Ta ce "Aifa ku Æ´an bokon nan komai aka ce ba'a iya ba sai ku."Haka sukayi ta hira har zuwa sallar magriba.
Dady yana zaune gaban Affa bayan sun gaisa sai ya ce "Yusufa sai kuma ka ji yanda Ubangiji ya yi ikon sa ko?"
Dady kanshi a ƙasa ya ce "na ji Affa sai dai har ya zuwa yanzu kaina yana duhu Affa ban san laifi na ba kai min irin wannan horon duk da nasan kai uba ne na gari mai hangen ƙwarai nasan bisa ga babban dalili ka aikata wannan abu zan so nasan dalili inda hali.
Jikin Affa ya yi sanyi ƙwarai da jin lafazin Yusuf kuma har ma yaji kunya, ya gyara zama sannan ya ce "Yusufa da farko dai kai min afuwa har ga Allah da nasan cewa Alhaji Mansur Yusuf Katsina shine mahaifin ka da babu dalilin da zan baka ƴata da sauri Dady ya dubi Affa bakin shi yana rawa ya ce "Affa saboda me?"
Affa ya ce "kafin haka ina son kayi haƙuri ka bar Ruƙayya,ga kayan ku nan da kuɗin ku kai hatta ƙyautar farko da kayi mata duk da na kashe,na samo na harhaɗa na maida na fasa baka Ruƙayya mahaifinka shi ne yakamata ya baka labarin dalilin da yasa na fasa aura maka ƴata, kuma nima dole ne na hana aurenta koda hakan yana nufin zaku rasa rankune kai da ita zan so ka gane, yanzu bari na shiga in sa a haɗo maka kayan ku. Zan cigaba da yi maka fatan alheri dan kaifa ɗa ne Yusuf."
Æari jikin Dady ya soma yi ya kasa magana har sanda Affa ya shigo ya zube mishi kuÉ—i a gabansa,ko takan kuÉ—in Dady bai bi ba, ya ce "Ka ce na tambayi Dad É—ina ko?"
Affa ya ce "Ƙwarai ka ce masa wanene koda yake ai kasan Jega ko?
Ya ce "Alhaji Aminu Jega?"
Affa ya ce "Shi"
Dady ya ce "nasan shi, shi ne mai kula da harkokin gine ginen Dad É—ina."
Affa ya ce "yauwa ka ko san shi, to ka je kace da mahaifin naka na ce ya sanar da kai me ke tsakanina dashi da Jega?"