← Book details Fin Karfi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 12

Sashe 1

Fin Karfi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

 *FIN ƘARFI BOOK 2*

*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*

Page 1

Sulaiman sun yi iya nasu ƙoƙarin dan ganin uban amarya ya sauka amma abin ya ci tura domin har ya kai da faɗin wallahi baza a ɗaura auran ba,in dai shine ya haifi Ruƙayya ba zata auri Yusuf ba.

Gefen Dad shima ya ce "ban da ɗan yau da ƙaƙule-ƙaƙule ɗan shi yafi ƙarfin ƴar talaka. Kuma in ƴan mata huɗu yake so yau ɗin nan zaya aura masa don haka ya jiƙa ƴar tashi yasha.

Jami'an tsaro sun so damƙar Affa amma sai Dad ya hana su ya ce "ku bar shi yaji da hasarar da yajawa ƴar tasa tunda yai mata baƙin cikin hutawa da cin tuwon dawa."

Gurin ya kaure gami da ya mutsewa jama'a sai surutu suke yi wasu na ƙorafin an ɓata musu lokaci ya yin da dangin amarya suka rasa dalili da yasa Affa ya aikata haka,su ko dangin ango nasu ganin su aka wulaƙanta don haka sun shaƙa matuƙa.

Dad tsaye jikin motarshi yana waya Momy yake mawa inda yake ce mata "In son be fito ba Hajiya kada ki barshi ya fito."

Gaban Momy ya faÉ—i ta ce "saboda me?"

Ya ce "Akwai matsala ne shi yasa dan auran ma an fasa É—aurawa."

Ta ce cikin faÉ—uwar gaba "akan me?"

Ya ce wulaƙanci mana mahaifin yarinyar ba dattijo bane ki tare son kada ya fito fa."

Jikin Momy yayi sanyi ta ce "ai tuni sun fita shi da abokinsa sai dai gyaran Allah."

Cikin shadda galila ƴar gaske blue takalmi da hula duk sun amshi angon yayi ƙyau, har ya gaji suna ta ratsa jama'a cikin motocin su da suka jero shi da abokinshi guda goma kowacce cike take da ɗan adam.

Yayan Dad shi ne ya tsaida su tare da faÉ—in su fito, ya dubi Dady ya ce "To Dady sai ka daina rawar kai tunda an fasa É—aura auran." Jin maganar Dady ya yi kamar saukar aradu ya dubi wan mahaifin shi, ya ce "In dai da gaske kake yi kodai kana tsokana ta ne?"

Ya ce "Kai abokin wasa na ne da zan tsokane ka? Don haka ku juya gamu nan zuwa," ido Dady ya tsurawa Uncle ɗin nashi tamkar yau ya soma ganin shi tun yana ganin shi tar-tar har ya soma ganin wasu taurari suna zagaya kan Uncle ɗin,kai har ya zamana duhu ya mamaye baya ganin komai da kowa. Su Sadiƙ da suma suna cikin ruɗani suka juya domin su lallashi Dady ya zo su wuce,sai ganin shi suka yi ya kusan kaiwa ƙasa,da sauri suka kama shi suka saka shi a mota, Dad cikin ruɗewa shi ma isa da gudu ya shiga mota, girgiza shi yake yana faɗin My son! My son!! Kai innalillahi,wai wama ya sanar da shi wannan abin.

Ita ma Ruƙayya lokacin da labarin ya iso mata nan take ta faɗi sai dai ita hankalin ta be gushe ba,ta dai shiga ruɗu mara misaltuwa,kuka har muryar ta ta dushe. Yaya Murja da Yaya Fati su ne suka sa ta tsakiya suna lallashinta gami da nuna mata kada ta damu in har Dady mijinta ne babu makawa sai ta aure shi sai dai in ba mijinta ba ne.

Cikin kuka Ruƙayya ta ce "nasan zaya yi wuya in auri Dady kuna fa jin yanda me nan gidan ya ce, cewa fa yayi Affa ya cewa mahaifin Dady,ko Dady ne autan maza ba zaya bashi ni ba ya fasa,kun fi kowa sanin halin Affa mutum ne shi wanda baya magana biyu.

Yaya Murja ta ce "haka ne to amma abin mamaki menene dalilin Affa na ƙin amincewa da auran, alhalin da farko ya yarda? Bugu da ƙari sai da ya bari mutane sun taru, wannan abin sam be min daɗi ba don za'a zage shi a gari.

Fati ta gyara zama sannan ta dubi Murja ta ce "amma fa ina ganin aƙwai dalili mai ƙarfi."

Ruƙayya ta ɗaga ido ta dubi Yaya Fati "shin wane dalili yasa Affa yayi min ƙwalele haka."

Yaya Fati ta ƙwantar da ita a jikinta,ta ce "Auta kiyi haƙuri, Affa shi ne ƙaɗai yake da amsar wannan tambayar,ki jure wata rana sai labari."

Lamo tayi tana sauraron Yaya Fati,tasan dole ne ma ta jure amma yanzun tana tunanin da wane ido zata dubi Dady?

Shin yanzun wane hali ma yake ciki? Duk da yake ma yanzu tasan baya tare da hankalinsa tafi kowa sanin irin son da Dady yake mata.

Sabon kuka ta saki tana cewa "nasan Dady yana cikin wani hali."

Su kansu sun rasa yanda zasuyi, basu kuma yi mata magana ba har tayi ta gaji, kafin wani lokaci tuni zazzaɓi ya rufe ta.

Ƴan biki jin anfasa tuni kowa ya kama gaban shi, sai dangi na jiki suma da gari ya waye gaban su zasu kama. Hafsi kam ji tayi tamkar sallah dan Yusra har da rawa tana jin daɗi.

Har zuwa wayewar gari Dady be farfaɗo ba, tashin hankali na ƙarshe iyayen shi sun shiga, don haka duk ilahirin likitocin dake asibitin, sun taru akan Dady, Momy kam kuka take da addu'o'in Allah yasa kada ɗan tilon ɗan nata kada ya tafi ya barta, shi kam Dad cewa yake in har yaron shi ya mutu bazaya yarda ba, to ko wanene zaya biya shi? Oho.

Kusan sha biyu saura na rana Dady ya farka, ruwan da ake ƙara masa ya bi da kallo shiru yayi yana tuna komai dalla-dalla, kanshi ya soma tambaya shin menene yasa Affa ya fasa bashi Pretty? Yasan yanda yake tsananin son ta kuwa,? Bama zai yiwu bane ace bazai auri Pretty ba,shin yanzu Pretty ɗin ma cikin wane hali take?

Tuni su Dad sun san cewa ya farfaɗo,sai dai likitan ya hana su suyi mashi magana, cewar likitan wai su barshi ya tuno abin da ya faru cikin sauƙi Dady ya juya ya dubi Dad ido ya zuba mishi kamar ya warke makanta, sannan ya mai da duban shi ga Momy,a ƙarshe ya koma ga likitan dukkan su suma shi suke kallo,a hankali likitan ya taka ya isa bakin gadon, yasa hannu ya shafa gefen fuskar Dady ya ce.

"Yusuf Son ya jikin? Kuma ina ne yake damun ka yanzun?

Shiru Dady ya yi tamkar kada ya tanka dan shi yanzu haushin kowa ma yake ji, amma daya tuna yana son yaje yaga Pretty ɗin sa sai ya tattara ɗan sauran ƙarfin halin ya yunƙura za ya tashi zaune likitanne ya taimaka masa, da sauri Dad da Momy suma suka iso bakin gadon ya dubi likitan ya ce "Doctor ni fa ina son a sallame ni dan ba inda yake min ciwo."

Dad ya riga likitan magana, My son kayi haƙuri kaɗan ƙara jin sauƙi mana, cikin sigar lallashi Dad ke magana, likitan ya ɗora kan batun Dad, "ko nan da ƙwana uku, sannan ka zama normal."

Dady ya ce gaskiya fa ko awa uku bana jin zan ƙara a nan,dan ina son naga Pretty na kuma san halin da take ciki.

Idon Momy ya cika da hawaye dole ne ma tasan abin yi game da wannan lamarin, Dad ya soma mishi faÉ—a.

"Ka kashe kanka saboda wata ƴar matsiyata duk da irin wulaƙancin da ubanta ya yi mana,da zagin da yayi min cikin bainar jama'a,na tara mutane manyan ƙasa da Sarakuna ya bani kunya gabansu,ai dole ne ma na nunama mutumin nan kuskuren sa."

Dady ya ji zuciyarshi ta na mishi ƙuna saboda irin zagin da Dad ke ma Affa,yana da tabbacin cewa aƙwai wani babban dalilin da yasa Affa ya aikata wannan abun, kuma yana zargin cewa Dad ko ɗan'uwanshi ne sila,wato Uncle.

Ɗaya hannun shi yasa ya zare allurar da aka sa mishi cikin hannu,dama shi ne ƙarin ruwan, ya miƙe tsaye da sauri.

Ganin haka likita ya riƙe shi "Ina zaka Yusuf?" Da sauri itama Momy miƙe ta riƙe shi tana faɗin.

"Dady ina zaka ne?"

Ya ce yana haki "Bar ni na tafi koma ina ne kina jin irin faÉ—an da Dad yake yi bana son ji, zuciyata na min zafi, kamar ta faso ta fito waje."

Momy ta ce "to kaji,in ɓacin ran da yake ciki be kashe shi ba, to kuwa kai faɗan ka ya kashe shi,kabar shi mana yaji daɗi."

Tsaki yayi sannan ya ce "Na rasa menene Son ya gani gurin yarinyar nan ga mata ma nan ƙyawawa ƴaƴan manyan mutane, amma ya ƙi ya tsaya gurin wannan ƴar matsiyatan."

Da sauri likitan ya ja Dad ɗin Office ɗin shi bayan sun zauna Doctor ya dubi Dad da ke ta cika yana batsewa, ya ce "Alhaji ba abin da ya dace kayi kenan ba,ya kamata ka kula da yaron nan dan kuwa yana cikin wani hali,so ba ƙarya bane,ko kasan jinin ɗan ka ya hau?"

Da sauri Dad ya miƙe cikin tashin hankali,ya ɗaga murya ya ce "Doctor ka ce jinin Son ɗina ya hau?"

Doctor ya ce "Of Course,bayan haka ma zuciyarshi zata iya bugawa a kowane lokaci matsawar zaya dinga shi ga irin wannan halin da yake yanzu,ko kuma a dinga sanyashi cikin tashin hankali.

Matuƙar tashin hankali Dad ya shiga ya dubi likita "to yanzu menene mafita?"

Doctor ya ce "Yauwa,da farko sai ayi ƙoƙarin ƙwantar mishi da hankali ta hanyar nuna mishi za'a san yadda za'ayi a mallaka mishi yarinyar."

Dad ya ce"zaya yi wuya ya samu yarinyar nan saboda wani ƙwaƙwƙwaran dalili mahaifinta ba zai yarda ba, shi yasa nike so Son ya haƙura da yarinyar dan tun farko ma bata dace da shi ba, ƙaramar yarinya ce sosai fa,ban san me yake ganin gurin yarinyar nan ba."
Chapter 1 · 0% Book details