Sashe 6
Dingishin Kwado Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washagari har azahar ban ga Yaya Sulaiman ba. Na kalli Mami da muke zaune a falo na ce "Yaushe zai zo na gan shi ne? Na kasa samun wayarsa".
Mami ta muskuta ta ce "Ina ganin gobe alhamis su dawo tare da Babanku".
Na ce "To Alla ya kaimu ya kuma kawosu lafiya".
Ta amsa da "ameen".
Washagari kuwa tare da Baba karami suka dawo. Na jima ina karewa Yaya Sulaiman kallo domin ya zama zabgegen saurayi na k'asaita .Kammanina da shi sun sake bayyana karara. A tsaye yake cak tamkar dai Yaya Asad, banbancin yafi Yaya Asad haske. Ba farine kamar ni ba, amma kuma ba za'a shi a sahun bakake irinsu Baban Bilkisu ba.
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Hoton fuskata na ga ni a fuskarsa sai banbancin gemu da kuma hasken fatata da sauran abubuwan da zasu banbanta jikin mace da na namiji. Amma tabbas muna matukar kama da juna.
Na tafi lissafin shekarunsa domin shekaru shida ya bamu. A lokacin shekarunsa talatin da uku. A wanccan lokacin gani ake yi ya zama tuzuru domin dukkan sa'aninsa da ma wanda ya girma sun yi aure har sun haihu.
Tun filazal Yaya Sulaiman dan gaye ne kuma dan bokone na gaske. Amma da ya dawo na fahimci ya samu cigaba mai yawa, ya goge da ilimi da kuma wayewar rayuwa.
Sadda suka iso ni da Abida muna farfajiyar harabar wajen adana motoci, gidan Yaya Faruk zamu je yini.
Da girmamawa muka gaida Baba karami.
Ya kalli Abida ya ce "Maryam kin huce, kin daina fishin?"
Ta dauke kai i tana fishi fishi kunya kunya ba tare da tanka ba.
Ya ce "Ato gara kisan matakin dauka dan kuwa tabbas babu maganar wata makaranta kuma sai a dakinki. Ke ko sha'awar yanuwanki da kike ganinsu da yaransu ba kya ji?"
Da shagwaba ta ce "To Baba sun duk sun samu mazan ni kuwa fa?"
Ya zabura ya mata dakuwa tare da yin kanta zai kai mata bugu.
Ta yi maza ta goce ta falfaala bata tsaya ba sai da ta bada tazara, sannan ta tsaya tana dan haki.
Ya ce "Mutane nawa suna zuwa wajenmu da sunan sun gan ki suna so, kina yin tsallen albarka kina fadin ba da yawunki suka zo ba?"
Ta kasa amsa masa. Ya yi kwafa ya ce "wannan karon kam ko ni ko ke na gaji da iyashegen ki, inma jinnul ashuq ne akanki zasu ci iyayensu dan kuwa na shirya yin arangama mai zafi da su".
✏️
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Daga ni har Yaya Sulaiman muka kwashe da dariya domin yadda Baba ya furta jinnul ashuq akwai ban dariya kwarai da gaske, yayin da ita kuma ta sha mur.
Haka muka tafi gidan Yaya Faruk tana ta gungunin ita bata da mashanshani, don kuwa duk wanda ake lissafin sun zo da sunan suna sonta ba jarumai bane ba kuma mijinta a ciki. Don ta yi imani da akwai mijin da kaddara ta zaba mata a cikinsu da tuni ta yi auren ai.
Muka isa gidan Yaya Faruk muka tarar yana shirin tafiya gidan gona. Ya dinga marabtarmu cikin barkwanci.
Haka ma matarsa domin a yanzu kam gaisuwar girma da arziki muke yi ta daina tsananta mini.
Ya zauna ya ce to ku gaisa da matar gidan ku sha ruwa sai mu tafi gidan gonar mu yini a can ko sarauniyar shaiba?"
A duk sadda ya ce hakan har cikin raina nake jin sunan. Tare da tasowar al'amura masu yawa a kansa.
A sanyaye na ce "To Yaya Faruk".
Ya saka hannu ya dauki mai sunansa da ya yi barci tun a hanya. Yana fadin my name sake tashi ka ga Yaya Faruk senior."
Na murmusa ba tare da na ce komai ba.
Ya kalli Abida ya ce "Autar momi wai har yanzu ba ki huce ba ne?"
Ta sake zumbura baki amma bata tanka ba.
Ya sassauta ya ce "Indai kin san akwai wanda yake sonki ki ba shi dama mana, ba fa wacce su Baba suka daga mata kafa irin ki. Ina jiye miki kada ki yiwa kanki sanadin da zaki ji sun bada aurenki ga wanda suka ga ya dace"
Ta murmusa ta ce "Ba maganar a mini auren dole Yaya Faruk. A wannan karnin? Da ilimina?"
Ta girgiza kai tabbacin ba mai yiwuwa ba ne.
Na zuba mata ido ba tare da na furta komai ba. Wato Abida asalin feminine ce.
Ya Farook ya kalle mu ya ce "Rigunan jininku sun mini kyau. Ban cika ganin abayas irin haka ba anan".
Abida ta ce "Bilki ta siya mana a wajen Umm Aslan &Asalah. Egyptian abayas ne kasan sune original. Ya ce gaskiya sun yi kyau sosai nima zan baki ki siyowa Jamila irinsu ".
201121544627 da +2349162662750 Kawai ta tuntube ta a WhatsAp sai ta zaba da kanta idan kun tura kudin, sai na karba muku a Kano tunda anan kayanta suke sauka.
Haka muka rankaya muka nufi gonar ladi farms da kwandon abincinmu matarsa ta hado mu da shi.
Yadda muka zo a motar Abida haka muka shiga ya ja muka yi gaba yayin da ya shiga tasa ya bimu a baya.
Gabadaya gidan gonar ya sake habaka, dukiyar dabbobi kala daban daban a ciki iya ganinka. Haka nan an gyara ta gyra na mussaman domin har zuwa ake yi da sunan yawon bude ido. Sosai ake hada hadar kasuwanci a ciki. Madara da yogurt din da ake sarrafawa a ciki na manyan kudade ne masu matukar nauyin gaske. Hatta kwai a kullum ana diban sama da dubu talatin ban da wanda suka fashe, shiyasa ma'aikatan wajen suma yawane da su tamkar me, an samu cigaba ta hanyar samarwa matasa masu yawa aikin yi
Yaya Faruk ya sake zama babban mutum kudi ya zauna masa duk da shi kadai ne a Funtua cikin yayyanmu. Amma yana cikin daula don idan kana gidansa ma sai ka zaci kana Abuja ne cikin rikunin uguwanni masu daraja.
Duk yadda nasan ladi farms girmanta ya kai kurewa amma a wannan ranar da na shiga cikin shekaru na hankali, ina kuma cikin nutsuwa sosai, na tsorata da irin girmanta da tarin dabbobi da shuke shuke. Don yanzu har 'katon runbun abinci an gina ta yadda ake adana kayan amfanin da aka nomawa a ciki.
Jikin mangwarori suka yi parking muka yi shimfida muka zauna. Gabadaya wajen yabanya ce ga danshin k'asa a dalilin duk safiya da maraice sai an jona tiyo a duk inda aka yi shuke shuke ko inda koriyar ciyawa take.
Duk yadda shekarun nan suke tafiya Yaya Faruk bai canja ba. Zama yake cikinmu a rak'ashe duk mai matsala ta zano masa, shi kuma zai saurare ka da kunnen basira ya kwantar maka da hankali ya kuma baka shawara ta gaskiya.
A yau kam Abida ce ta dinga jero masa laifukan Momi. Ashe duk yadda soyayyar Abida bata boyuwa a wajen Momi yanzu zaman nasu ya fara tsami bisa dalilai guda biyu. Ita Momi aure take so Abida ta yi, dan haka ta matsa lambar sai ta fito da miji, bayan haka mafi yawa bata bari ta yi dinkuna ko saka kayan alatu bisa hujjar wai maza zasu kasa dunfararta da sunan aure tunda suna ganin matsayin aikinta da matsayin gidansu, kaya masu tsadar gaske kuma zasu sake kaita kololuwar
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: matsayi.
Ya yi dariya ya ce "Hakuri za ki kara yi, lamarin iyaye dole a bisu yadda suke so. Sannan ni kaina so nake ki yi auren Abida! Menene ya rage miki ne? Aure kuma shine suturar mace. Duk zurfin karatun da zaki yi, matukar ba ki da aure kin rasa wata kariya ta mutuntaka da aure kadai ke bawa mace shi. Ki nutsu ki sassauta burinki, ba yadda za'a yi ki samu irin teste din ki, domin no body is perfect a cikin wannan rayuwar."
Ba walwala ta ce "Aure lokaci ne fa yaya Faruk. Kuma ni ba wani dogon buri ko wani tsatssauran ra'ayin na dauka ba. Kawai wanda zuciyata ta nutsu ne ban samu ba, amma ko yanzu idan na samu wanda na aminta da shi zan gabatar da shi. Akan me za'a matsa mini har sai na je na auri wanda ba mijina ba ne?.
Muka kwashe da dariya. Na kasa ce wa komai domin yanzu zata sauke mini fishinta da take fama da shi, na sani. Yaya Faruk ne ya ce "Dama ana auren mijin da ba naka ba ne autar momi?
Da dukkan zuciyarta ta ce "sosai ma domin idan na auri wrong person ai ban auri mijina ba domin na fada cikin garari da talajaurar duniya".
Ya gintse dariyarsa ya ce "Da ikon Allah na gari za ki aura albarkacin adalcin da iyayenmu maza suke yiwa iyayenmu mata ba za ki yi aure inda za ki wulakanta ba. Fatana ki kwantar da hankalinki. Ki bude zuciyarki ki fahimci manufar iyayenmu ".
Anan muka yi sallar la'asar.
Wajen karfe biyar sai ga Yaya Sulaiman ya iso akan machine.
Yaya Faruk ya kalle shi ya ce "Baka son yin tuki ne?"
Da walwala ya ce "Da kafata na yi rabin tafiyar.
Sai kuma na hau machine domin daga bakin gate din nan ma shigowa ciki ba karamin tafiya ba ce mikakkiya".
Yaya Faruk ya ce "Ka yi kokari, ka kuma motsa jikinka.
Na kalle shi na ce "Yaya Sulaiman sannu da zuwa dama na k'osa mu hadu".
Ya zauna yana ce wa "Ga ni "Bilkisu sarauniyar shaiba in ji Yaya Faruk ".
Muka murmusa gabadayanmu ban da Abida da dama ba wani jituwa suke yi ba tun filazal.
Ya kalle!ta ya ce "Autar momi saboda Allah har yanzu ma da kika girma ba zamu shirya ba? Tunda na dawo sau uku kika bude baki kika mini magana fa".
Yana rufe baki ta ce "To ai sau ukun muka hadu."
Ya ce" yau fa?"
*Gunis hijab ba na biyunta wajen kawo hijaban da suke da kyau da nagartar.*
*Gunis hijab ado cikin wayewar addini da rayuwa*
*08163761797*
Mami ta muskuta ta ce "Ina ganin gobe alhamis su dawo tare da Babanku".
Na ce "To Alla ya kaimu ya kuma kawosu lafiya".
Ta amsa da "ameen".
Washagari kuwa tare da Baba karami suka dawo. Na jima ina karewa Yaya Sulaiman kallo domin ya zama zabgegen saurayi na k'asaita .Kammanina da shi sun sake bayyana karara. A tsaye yake cak tamkar dai Yaya Asad, banbancin yafi Yaya Asad haske. Ba farine kamar ni ba, amma kuma ba za'a shi a sahun bakake irinsu Baban Bilkisu ba.
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Hoton fuskata na ga ni a fuskarsa sai banbancin gemu da kuma hasken fatata da sauran abubuwan da zasu banbanta jikin mace da na namiji. Amma tabbas muna matukar kama da juna.
Na tafi lissafin shekarunsa domin shekaru shida ya bamu. A lokacin shekarunsa talatin da uku. A wanccan lokacin gani ake yi ya zama tuzuru domin dukkan sa'aninsa da ma wanda ya girma sun yi aure har sun haihu.
Tun filazal Yaya Sulaiman dan gaye ne kuma dan bokone na gaske. Amma da ya dawo na fahimci ya samu cigaba mai yawa, ya goge da ilimi da kuma wayewar rayuwa.
Sadda suka iso ni da Abida muna farfajiyar harabar wajen adana motoci, gidan Yaya Faruk zamu je yini.
Da girmamawa muka gaida Baba karami.
Ya kalli Abida ya ce "Maryam kin huce, kin daina fishin?"
Ta dauke kai i tana fishi fishi kunya kunya ba tare da tanka ba.
Ya ce "Ato gara kisan matakin dauka dan kuwa tabbas babu maganar wata makaranta kuma sai a dakinki. Ke ko sha'awar yanuwanki da kike ganinsu da yaransu ba kya ji?"
Da shagwaba ta ce "To Baba sun duk sun samu mazan ni kuwa fa?"
Ya zabura ya mata dakuwa tare da yin kanta zai kai mata bugu.
Ta yi maza ta goce ta falfaala bata tsaya ba sai da ta bada tazara, sannan ta tsaya tana dan haki.
Ya ce "Mutane nawa suna zuwa wajenmu da sunan sun gan ki suna so, kina yin tsallen albarka kina fadin ba da yawunki suka zo ba?"
Ta kasa amsa masa. Ya yi kwafa ya ce "wannan karon kam ko ni ko ke na gaji da iyashegen ki, inma jinnul ashuq ne akanki zasu ci iyayensu dan kuwa na shirya yin arangama mai zafi da su".
✏️
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Daga ni har Yaya Sulaiman muka kwashe da dariya domin yadda Baba ya furta jinnul ashuq akwai ban dariya kwarai da gaske, yayin da ita kuma ta sha mur.
Haka muka tafi gidan Yaya Faruk tana ta gungunin ita bata da mashanshani, don kuwa duk wanda ake lissafin sun zo da sunan suna sonta ba jarumai bane ba kuma mijinta a ciki. Don ta yi imani da akwai mijin da kaddara ta zaba mata a cikinsu da tuni ta yi auren ai.
Muka isa gidan Yaya Faruk muka tarar yana shirin tafiya gidan gona. Ya dinga marabtarmu cikin barkwanci.
Haka ma matarsa domin a yanzu kam gaisuwar girma da arziki muke yi ta daina tsananta mini.
Ya zauna ya ce to ku gaisa da matar gidan ku sha ruwa sai mu tafi gidan gonar mu yini a can ko sarauniyar shaiba?"
A duk sadda ya ce hakan har cikin raina nake jin sunan. Tare da tasowar al'amura masu yawa a kansa.
A sanyaye na ce "To Yaya Faruk".
Ya saka hannu ya dauki mai sunansa da ya yi barci tun a hanya. Yana fadin my name sake tashi ka ga Yaya Faruk senior."
Na murmusa ba tare da na ce komai ba.
Ya kalli Abida ya ce "Autar momi wai har yanzu ba ki huce ba ne?"
Ta sake zumbura baki amma bata tanka ba.
Ya sassauta ya ce "Indai kin san akwai wanda yake sonki ki ba shi dama mana, ba fa wacce su Baba suka daga mata kafa irin ki. Ina jiye miki kada ki yiwa kanki sanadin da zaki ji sun bada aurenki ga wanda suka ga ya dace"
Ta murmusa ta ce "Ba maganar a mini auren dole Yaya Faruk. A wannan karnin? Da ilimina?"
Ta girgiza kai tabbacin ba mai yiwuwa ba ne.
Na zuba mata ido ba tare da na furta komai ba. Wato Abida asalin feminine ce.
Ya Farook ya kalle mu ya ce "Rigunan jininku sun mini kyau. Ban cika ganin abayas irin haka ba anan".
Abida ta ce "Bilki ta siya mana a wajen Umm Aslan &Asalah. Egyptian abayas ne kasan sune original. Ya ce gaskiya sun yi kyau sosai nima zan baki ki siyowa Jamila irinsu ".
201121544627 da +2349162662750 Kawai ta tuntube ta a WhatsAp sai ta zaba da kanta idan kun tura kudin, sai na karba muku a Kano tunda anan kayanta suke sauka.
Haka muka rankaya muka nufi gonar ladi farms da kwandon abincinmu matarsa ta hado mu da shi.
Yadda muka zo a motar Abida haka muka shiga ya ja muka yi gaba yayin da ya shiga tasa ya bimu a baya.
Gabadaya gidan gonar ya sake habaka, dukiyar dabbobi kala daban daban a ciki iya ganinka. Haka nan an gyara ta gyra na mussaman domin har zuwa ake yi da sunan yawon bude ido. Sosai ake hada hadar kasuwanci a ciki. Madara da yogurt din da ake sarrafawa a ciki na manyan kudade ne masu matukar nauyin gaske. Hatta kwai a kullum ana diban sama da dubu talatin ban da wanda suka fashe, shiyasa ma'aikatan wajen suma yawane da su tamkar me, an samu cigaba ta hanyar samarwa matasa masu yawa aikin yi
Yaya Faruk ya sake zama babban mutum kudi ya zauna masa duk da shi kadai ne a Funtua cikin yayyanmu. Amma yana cikin daula don idan kana gidansa ma sai ka zaci kana Abuja ne cikin rikunin uguwanni masu daraja.
Duk yadda nasan ladi farms girmanta ya kai kurewa amma a wannan ranar da na shiga cikin shekaru na hankali, ina kuma cikin nutsuwa sosai, na tsorata da irin girmanta da tarin dabbobi da shuke shuke. Don yanzu har 'katon runbun abinci an gina ta yadda ake adana kayan amfanin da aka nomawa a ciki.
Jikin mangwarori suka yi parking muka yi shimfida muka zauna. Gabadaya wajen yabanya ce ga danshin k'asa a dalilin duk safiya da maraice sai an jona tiyo a duk inda aka yi shuke shuke ko inda koriyar ciyawa take.
Duk yadda shekarun nan suke tafiya Yaya Faruk bai canja ba. Zama yake cikinmu a rak'ashe duk mai matsala ta zano masa, shi kuma zai saurare ka da kunnen basira ya kwantar maka da hankali ya kuma baka shawara ta gaskiya.
A yau kam Abida ce ta dinga jero masa laifukan Momi. Ashe duk yadda soyayyar Abida bata boyuwa a wajen Momi yanzu zaman nasu ya fara tsami bisa dalilai guda biyu. Ita Momi aure take so Abida ta yi, dan haka ta matsa lambar sai ta fito da miji, bayan haka mafi yawa bata bari ta yi dinkuna ko saka kayan alatu bisa hujjar wai maza zasu kasa dunfararta da sunan aure tunda suna ganin matsayin aikinta da matsayin gidansu, kaya masu tsadar gaske kuma zasu sake kaita kololuwar
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: matsayi.
Ya yi dariya ya ce "Hakuri za ki kara yi, lamarin iyaye dole a bisu yadda suke so. Sannan ni kaina so nake ki yi auren Abida! Menene ya rage miki ne? Aure kuma shine suturar mace. Duk zurfin karatun da zaki yi, matukar ba ki da aure kin rasa wata kariya ta mutuntaka da aure kadai ke bawa mace shi. Ki nutsu ki sassauta burinki, ba yadda za'a yi ki samu irin teste din ki, domin no body is perfect a cikin wannan rayuwar."
Ba walwala ta ce "Aure lokaci ne fa yaya Faruk. Kuma ni ba wani dogon buri ko wani tsatssauran ra'ayin na dauka ba. Kawai wanda zuciyata ta nutsu ne ban samu ba, amma ko yanzu idan na samu wanda na aminta da shi zan gabatar da shi. Akan me za'a matsa mini har sai na je na auri wanda ba mijina ba ne?.
Muka kwashe da dariya. Na kasa ce wa komai domin yanzu zata sauke mini fishinta da take fama da shi, na sani. Yaya Faruk ne ya ce "Dama ana auren mijin da ba naka ba ne autar momi?
Da dukkan zuciyarta ta ce "sosai ma domin idan na auri wrong person ai ban auri mijina ba domin na fada cikin garari da talajaurar duniya".
Ya gintse dariyarsa ya ce "Da ikon Allah na gari za ki aura albarkacin adalcin da iyayenmu maza suke yiwa iyayenmu mata ba za ki yi aure inda za ki wulakanta ba. Fatana ki kwantar da hankalinki. Ki bude zuciyarki ki fahimci manufar iyayenmu ".
Anan muka yi sallar la'asar.
Wajen karfe biyar sai ga Yaya Sulaiman ya iso akan machine.
Yaya Faruk ya kalle shi ya ce "Baka son yin tuki ne?"
Da walwala ya ce "Da kafata na yi rabin tafiyar.
Sai kuma na hau machine domin daga bakin gate din nan ma shigowa ciki ba karamin tafiya ba ce mikakkiya".
Yaya Faruk ya ce "Ka yi kokari, ka kuma motsa jikinka.
Na kalle shi na ce "Yaya Sulaiman sannu da zuwa dama na k'osa mu hadu".
Ya zauna yana ce wa "Ga ni "Bilkisu sarauniyar shaiba in ji Yaya Faruk ".
Muka murmusa gabadayanmu ban da Abida da dama ba wani jituwa suke yi ba tun filazal.
Ya kalle!ta ya ce "Autar momi saboda Allah har yanzu ma da kika girma ba zamu shirya ba? Tunda na dawo sau uku kika bude baki kika mini magana fa".
Yana rufe baki ta ce "To ai sau ukun muka hadu."
Ya ce" yau fa?"
*Gunis hijab ba na biyunta wajen kawo hijaban da suke da kyau da nagartar.*
*Gunis hijab ado cikin wayewar addini da rayuwa*
*08163761797*